https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ *💖JUYAYI💖* ```The secret issues``` *N.S* EPISODE 1 Destiny ......Zaune take tsakiyar tafkeken royal bed ɗinta,Ta cure waje guda banda sauke numfashi babu abinda take,sai yalwataccen gashinta wanda jifa² iskar ɗakin ke kaɗashi,Zuwa yanzu ta gama yanke jindaɗin rayuwarta,A yau tasan cewa bata da wani gata face na Ubangijin daya halicceta yanzun mai zata kira kanta *ƘARUWA* ko *ƳAR ISKA* ko kuma wacce yayanta ya lalata a dare mafi muhimmanci,A hankali ta ɗago manya-manyan lulu eyes ɗinta wanda suke always sleepyn ta zubasu kan oval face ɗinsa mai matuƙar kyau da kuma tsari Allah yay masa baiwar kyau da kuma kwarjini ba zaka taɓa iya yin 4eyes dashi ba sbd wasu kifiyo masu kaifi da suke cikin idonsa,Dubanta takai kan faffaɗan ƙirjinsa wanda ya cika da yalwataccen gashi baƙi siɗik mai sheƙi,Wasu siraran hawaye ne suka shiga zuba daga cikin idonta,bata taɓa jin tsanar wani ɗan adam aduniya ba sai yau,tayi masa tsana mafi muni da ace tana da ikon kashe kanta kota kashe shi babu shakka da tayi hakan. Numfashi ya shiga fitarwa a hankali ga wata zufa da take keto masa duk da sanyin A.C'n ɗakin,Cikin kasala da kuma ɗan saurin ƙarfin daya rage masa yasa hannu ya dafe saman forehead ɗinsa,Sannu a hankali ya kejin duniyar na sauya masa wani abu ya tokare masa ƙirjinsa,Jin kansa yake a wata duniya ta daban yayinda tsoro da fargaba suka dirarwa zuciya a lokacin guda,Mamaki ne ya cikasa baya da tsoro haka baisan yadda ake jin saba amma yau shine tsoro ya sauka a cikin zuciyarsa Why!! Why!! Why!! Shine abinda yake tambaya amma babu maiyi masa bayanin akan dalilin faruwar hakan,lumshe manya² idonsa yay wanda some minutes suka koma asalin red,Saurin dafe saitin zuciyarsa yay sbd saukar kukanta daya jiwo meya faru cikin wannan daren har take kuka haka,wanne irin kukane wanda ya cika gidan gaba ɗaya,he hope ace ba jikinta bane ya tashi,Jin kukanta yay yawa ne yasa cikin yanayi na kasala ya ware sexcy eyes ɗinsa zuwa saman ɗakin,Tun daga saman ɗakin ya fahimci bawai a cikin ɗakinsa yake ba,kansa ya juyawa zuwa side ɗin daya kejin kukan a ɗan tsorace ya ƙara ware manyan idonsa,jikinsa yabi da kallo ganinsa naked hatta boxer jikinsa babu,Zuciyansa ne ya bada sauti damm gaba ɗaya badsheet ɗin ya ɓace da blood,"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shine kaɗai abinda bakinda mai yasa yay loosing control a kanta abinda bai taɓa yi ba,shikenan ya ruguza rayuwar his biogical sister ɗinsa ya rabba how can dat happen shine ya amshi virgin ɗin sister ɗinsa wacce suke the same mom and Dad da ita a dare mafi muhimmanci,Mai zaice mata tayaya zai mata bayanin bada gangan ya aikata hakan ba,wannan abin kunyar har ina kodai ya haukace ne ko kuma ya sha wani abune no it's impossible pls FAHAD wake up in ur bad dream. Jiki a sanyaye ya zura jallabiyarsa haɗi da saka boxer ɗinsa,runtsa ido yay ganin duk blood a jikin laps ɗinsa,yana kammalawa yasa kai ya fice daga ɗakin ya nufi flat ɗinsa,yana gaf da shige yaji saukar muryar Dad a kunnansa,Tsayawa yay cak tare da ignoring maganar Dad ɗin" Dr hope dai lafiya ka fito tsakiyan wannan daren?"Dad ya ƙara mai²ta tambayarsa zuwa FAHAD taune jajayen siraran laɓɓanta yay kafin ya fesar da numfashi mai zafi cikin son kawar da abinda yake damunsa gudun kar daɗi ya fahimci komai yace"notin"kafin ya tafi Dad ya ƙara jefa masa tambaya"yaya jikin OUR LILI?"ɗan juyowa yay tare da zuba Dad ɗin nasa ido na wani lokacin "she is fny"yana faɗin hakan yasa kai ya fice. *Maidugori road* Washe gari Juyi yake saman fafaɗan bed ɗinsa wanda a ƙallah zai iya ɗaukan mutum wajan 6,tym to tym yakan ɗanja tsaki haka nan kawai yake jin kansa cikin fargaba da kuma faɗuwan gaba yay try numberta harya gaji,yauce rana ta farko daya kira bai sameta ba jinsa yake kamar someting bad gonna happen to his LILI,ɗan murmushi yay ganin cewa nan da 5hours ta zama mallakinsa kuma halaliyarsa a yau zata kwana a gidansa matsayin matarsa,yana mata wani irin mahaukanci so wanda ko a baki aka tambayeshi wanne irin so yake mata bazai taɓa iya faɗa shi dai yasan he luv her more & more most. Turo ƙofar ɗakin nasa akai wasu frends ɗinsa ne suka shigo fuskarsu wasai sai fara'a suke,Cike da zulaya Abdul yace"ango ango today is ur tym fa harna hango ka kana.."murmushin gefen baki FAISAL yana jin wani daɗi na ratsashi kallon Abdul yay yace"u never undertsant my emotion for her inajinta fiye da yadda nakeson komai na rayuwata Abdul inajin idan babu ita life is ending ta zama kamar itane numfashin da Faisal ke shaƙa a koda yaushe i luv you my Beby boo" Dariya su Abdul sukai daga nan suka shiga nuna masa hall ɗin da za'ai event ɗin after an shafa fatiha. *Nasarawa* Zaune take akan luntsumemiyyar sofar da take parlon hannunta ɗauke da wayarta tana latsawa amma kana ganin yanayinta kasan She is not felling Wall,idonta ya kumbura sosai sbd kukan data kwana ta nayi,lips ɗinta ya ƙara jaa sbd taunashe data ringayi,jin an zauna kusa da ita yasa ta ɗaga dara-daran idonta tare da saukesu akan Najma wacce ta zuba mata ido tare da faɗin"are you ok?"ɗanya tsuna fuska LILI tayi tare da faɗin"more than you are"ɗan jinjina kai Najma tayi tare da ƙara zubawa Lili ido tana son fahimtar halinda ƴar uwarta take ciki amma ta kasa,Gyara zama tayi tare faɗin"today is ur wedding day and you're sitting so carelessly busy with ur fucking phone don't know that we have lots things to do?" Najma ta faɗa tare dasa hannu ta amshe wayar hannun Lili,taune laɓɓanta tayi tare da lumshe idonta sosai ta kejin bugun zuciyarta na ƙaro haka numfashinta guda dazai fita baya taɓa fita ba tare da tsanar yayanta mai ƙaunarta da sonta ba FAHAD,tayi masa mummunar tsana bata ƙaunar ji ko sauraran muryarsa ko kuma ganin mummunar fuskarsa wacce a daren jiya ta ɓata komai najin daɗin rayuwa,tana kuɗi ilimi asali kyau diri amma hakan bai sata jin daɗi ba saima tsanar komai da tayi,ta rasa mutuncinta ta siyar Yayanta yaya sunan wannan auren da zatai me zata gayawa FAISAL idan yasan cewa ita ba budurwa bace wasu siraran hawaye ne suka shiga sauka daga cikin idonta a hankali ta furta"what should i do?". Kafin ta ƙara magana Mamy ta ƙarasu wajan hannunta ɗauke da wata roba,murmushi fal fuskarta tace"hi my bebies" baki suka haɗa wajan faɗin "good morning Mamy"..morning my grils,My Lili how is ur body?"kanta a ƙasa tace"felling much better Mamy"robar hannunta ta miƙa mata da alama zuba ne a ciki tace"oyya drink kije Dad na kira"she said it in serious voice. Ba tayi musu ba ta amsa tasha tare da miƙewa ta fara jan ƙafarta tare daɗan ɗingisawa Najma da Mamy ne suka zuba mata ido ba tare da kowa yay mgn ba. Lokaci kaɗan ta isa flat ɗin Dad yana zaune saman kujera yana duba jarida ya amsa mata sallamarta tare da faɗin"Mamana badai jikin bane naga ɗingishi?"murmushin da baya rabuwa da fuskarta tayi tare da ƙarasawa wajan Dad ta gaishesa,cike da so da ƙauna ya shafa kanta"Maman soon za'a manyanta igiyar aure zaihau kanta,Allah yay maki Albarka naji daɗi fiye da tunanin mai tunanin yau zanga auren ƴarta kuma zai kaita gidan mijinta tare da mutuncinta,tabbas kin cika ƴar ta gari wacce ta killace mutuncinta har zuwa gidan mijinta,nan da wasu hours za'a ɗaura Aurenku nasha tambayarki duk da kene kika kawo Faisal da kanki a matsayin mijin da zaki aura amma haƙƙine a kaina na kara shaida irin sonda kike masa"shuru yay na wani lokacin kafin yaja numfashi haka kawai yaji fargaba ta ziyarci zuciyarsa,cikin son kawar da abunda yake damunsa yace. "kin tabbatar kina son Faisal kuma kin amince a yau a ɗaura maku aure dashi?" *Tofa mekuke tunanin zai faru,shin za'ai wannan auren ko yaya? Aci gaba da biyoni* Wattpad@Nimcyluv a nan zaku samu ci gaba thank you. *💖JUYAYI💖* *N.S* EPISODE 2 Tension *SELF DU'A👐🏻* Dear God if i am wrong,right me. If i am lost,guide me. And if i start to give up,keep me going👏🏻 .....Sadda kanta ƙasa tayi haɗe da lumshe dara-daran manyan idonta lips ɗinta ta shiga taunewa ta nayi tana runtsa idonta sbd yadda zuciyanta ke bada bugu da ƙarfi ga yanayin yadda gudun zuciyarta daya ƙaro,wasu wahalallun hawaye ne suka shiga fita daga cikin sleepyn eyes ɗinta wanda suke koda yaushe a rufe,ƙasa cewa komai tayi domin bata da amsar da zata bawa Dad a wannan lokacin,Kallonta Dad yay tare da zuba mata ido yana son karantar yanayin ƴar tasa but he did'nt understand her condition cikin serious voice yace. "Mamana bazan maki dole ba bcz ur happiness is my happiness,bana da wani jin daɗi daya huce na faranta maku keda yayyanki banda wani ambition wanda ya huce naga ko wannanku ya cimma ambition ɗinsa wanda yake aceving domin inganta rayuwarku,i wish ace kin auri wanda zai kula dake sbd rashin lafiyanki...shuru yay tare da zuba mata ido yana mamakin irin hawayen dake fita daga idonta,fesar da numfashi yay kafin ya ƙara dubanta yace "Mamana i'm with u i need ur amswer tym is not ur side ok". Shassheƙar kuka ta fara few minutes eyes ball ɗinta suka ƙanƙance jikinta ya shiga rawa jijiyoyin ƙanta suka fara tashi ta ƙyar ta samu tayi tear out voice ɗinta na creating tace"i don't love him anymore,my life is nothing for him,pls Dad ada katar da bikin nan a kaina,ina neman alfarmar a bayar da bikin kan Yaya Najam gudun kada girmanka ya zube idon mutane" Wani murmushin kin rainamin hankali Dad yay mata,gefe guda na zuciyarsa ya najin tausayi da kuma rauni haɗi da bugun zuciya,tabbas zai mata abinda takeso duk da yasan zallar wawta ke damunta musamman idan yay duba zuwa ƙanƙantar shekarunta,Jaridarsa ya ɗauka tare da kawar da kansa gefe yace"get out". Jiki a sanyaye ta miƙe tana ɗanjan ƙafarta waccw tym to tym take riƙe mata sbd tsananin zabar data keji a ƙasanta,Dana daurewa ne kawai sbd bata son barin wani sing da zainuna tana da matsala,tsayawa tayi ta goge hawayen fuskarta tare da saita nutsuwarta,Ci gaba tayi dajan ƙafarta zuwa parlo taji daɗin ganin babu kowa dan haka tasa kai ta shige bedroom ɗinta,Darect bathroom ta shige tana zuwa ta shige cire kayan jikinta tare da zubasu a hanger ɗin da take saƙale kayanta idan zatai wanka,Ruwan zafi ta haɗa sosai cikin Jakuzzie tsayawa tayi tana tunanin da wanne magani zatai using wanda zai rage mata pind ɗin data keji,Ganin bata san komai yasa tayi shahadar shiga cikin ruwan ƴar ƙara ta saki jin wani zafi haɗi da raɗaɗi ya ziyarceta lokaci guda,kuka ta shigayi tare faɗin"Ya rabb ka samamin sauƙi a cikin zuciyata ubangiji ka fini sanin dai² da kuma ba dai² ba ina roƙonka da dukkan sunayenka ka haskakamin zuciyata dan haske Alkur'ani mai girman,tabbas nasan itace ƙaddarata kuma ƙaddara mafi muni a cikin ƙaddarori Allah ka bani ikon cinye jarrabawar daka ɗuramin, Na tsaneshi tsana mafi muni kamar yadda na tsani kaina,Ubangiji ka ɗauki raina idan hakan shine mafi sauƙi a cikin rayuwata nasan baƙin cikin YAYA shine zai ajali naيا الله يا رحمن يا رحيم يا رب العرش العظيم 🙌🏻😢 saida ruwan ya gama ratsa jikinta sannan ta ƙara sauya wani ruwan tayi wankanta sosai,gaban mirrow taje ta zuba kan ido ta cikin tafkeken mirrow'n dake manne a toilet ɗin nata,murmushin baƙin ciki tayi wanda yafi kuka ciwo LILI kyakkyawace ajin farko Allah ya bata manyan ido farare tas tana da blue eye ball ɗin sai zara-zaran eye lashis baƙi siɗik wanda ya sauka saman idonta yay luff dashi,tana da Oval face ƴar madaidai ciyya mai kyau da tsari haɗi da dugwan hancinta wanda ya tsaya dai² ɗan ƙaramin bakinta wanda yake ɗauke da siraran jajayen laɓɓa masu kyau wanda kullum ƙara red suke saboda taunesu da take anytime,tana da gashin kai mai tsayi sosai wanda ya sauka har gadon bayanta saidai gashinta ba baƙi bane yay colour tana turawa,tsarin halittar cikin ƴar madaidai ciyya tana ɗan faffaɗan waist dai² da faɗin ƙirjinta,sai ƴan ma dai-dai tan brest wanda suke da ɗan girma amma ba sosai ba saidai tsayi,cikinta *JUYAYI* Continew ....Nimcy Luv: a lafe yake kamar babu kayan ciki ko bata cin abinci,tsaki taja mai ɗan sauti a taushashe ta wara laɓɓanta cikin muryarta wacce ta gama dadishewa sbd kukan tace"Kyau masifa ne lallai idan namiji yace zai auri mace dan kyanta babu shakka zai auri kusan matan duniyyar nan" ash long towel ta ɗauka ta ɗaura saman ƙirjinta tare da ɗaukan ƙaramin ta shiga goge kanta saida ta gama sannan ta ajjiye towel ɗin tare da fice daga toilet ɗin,manyan idonta ta shiga ƙifƙifawa sakamakon ganin Mamy zaune a gefen bed ɗinta a zaune,a sanyaye taja kujerar dake manne gaban mirrow zata zauna taji saukar muryar Mamy na faɗin "Zonan Lili"bata kawo komai a ranta ba ta ƙarasa wajan Mamy tare da zama kusanta tare da sadda kanta ƙasa ba tare da tace komai ba,fuska Mamy ta ɗaure kana ganinta kasan babu wasa tace"Lili meke damunki kike jan ƙafa?" Ya iliahi tabbas da ace tasan wannan tambayar zatai mata kuma tasan tana ɗakin da ba zata taɓa fituwa daga toilet ɗin ba,shuru tayi Mamy ta shiga wasa da hannunta ran Mamy ba ƙaramin ɓaci yay ba,dan idan masiface wajan Mamy ba laifi a kwaita cikin muryar faɗa tace"i'm i ur mate da zanna magana kina ignoring nawa" turo baki Lili tayi cike da shagaɓar data zauna mata tace"is noting serious naɗan ji ciwo ne a lap ɗina"tsaki Mamy taja tasa hannu ta kwantar da Lili akan bed tare da ƙoƙarin ware towel ɗin dake cikinta,cikin Sauri Lili ta miƙe zaune tare da riƙe hannun Mamy tace"Ayya Mamyn Ubangiji ya haramta kallon tsaraicin Mutum fa"zubawa Lili ido tayi tare da sakinta ta miƙe tsaye tace. "Allah subuhanahu wata'alah da kansa ta faɗa cikin Alkur'ani mai girma ta kuma hadisi yace _بسم الله الرحمان الرحيم da ƴar ƴar da dukiyya amanane gareku,idan kunci amanarsu kamar kuci amanta ne,Rana gobe alƙiyyama zan tambayeku amanar dana baku_ Kinga hakan na nufin idan nayi tarbiyarku na kula da dukkan wani mutsi na naku,na baku rayuwa da ilimi mai kyau ina da tabbacin Allah bazai tambayeni haƙƙinku ba,amma ki sani muma iyaye muna da haƙƙi a kanku,bana da burin naga na kaiku gidan mazajenku da mutuncinku wanda mijinku zai Alfahari daku Lili kiji tsoron Allah kada ki watsa tarbiyyar da nayi maku wannan tunatarwa nai maki Allah yay maki albarka" Tana faɗin hakan tasa kai ta fice daga bedroom ɗin,faɗawa saman bed Lili ashe ma kuka rahama ne,dama zata iya da taji sauƙi a cikin ranta,wani zafi haɗi da raɗaɗi ta keji a cikin zuciyarta yauta ƙara tabbatarwa bata da wani sauran gata daya huce gatanta na wajan Ubangiji,Addu'ar neman sauƙi take a cikin zuciyarta kafin daga ƙarshe ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciyar dukkan wanda ya saurara. FAHAD Tunda yabar ɗakin Lili ya shige flat ɗinsa ya kasa zaune ya kasa tsaye sai safa da marwa yake a tsakiyar tafkeken bedroom,duk ƙoƙarinsa nason bawa ƙwaƙwalwarsa damar yin tunani amma abun ya gagara brain ɗinsa a cunƙoshe take yayinda gudun zuciyarsa ya ƙara gudu very past,hannu yasa ya dafe ƙansa wanda yake barazar tar watsewa sbd tsananin ciwo da azabar da yake masa jijiyoyin kansa sun tashi sunyi raɗa-raɗa sbd tsananin a zaɓa,gaba ɗaya birkice ya zama kamar bashi ba,banda fesar da huci da yake akai² babu abinda yake daga ƙarshe ya fasa wani ihu ya shiga watsi da dukkan abinda yay ƙaro dashi saida ya gama har ƙisa ɗakin tas sannan ya tsaya yana kallon hannunsa wanda yak ɗigar jini sbd kwalbar data yankesa,a hankali yake takawa zuwa wajan wata loker cike da kuzari data ƙama yake takonsa harya isa wajan loker,ɗan durƙusawa yay tare dasa hannu ya buɗe lokar hannu yasa a ciki tare da ɗakko first aid box ɗinsa yana buɗewa ya ciro wata injection,saida ya mayar da komai sannan ya cire jallabiyarsa bai tsaya sauraran komai ba yabi abinda ruhi da gangar jikinsa suke buƙata ya cikawa ƙansa injection ɗin tare danne ruwan allurar a jikinsa,yana gamawa yay cilli da sirijin some minutes jikinsa ya ɗauri rawa gargasar jikinsa ta miƙe hannu yasa ya shiga hargitsa tulin sumar ƙansa kafin kace me ya fita hayyacinsa baya iya gane komai tunaninsa ya tsaya cak kamar yadda brain ɗinsa ta tsaya da aiki,a zafafe ya kaiwa bango naushi tare da faɗin"Yes i'm a mad,i don't have any importand for her life i'm notin for her"ya faɗa yana buga ƙansa da jikin bango tan gaɗi ya fara a haka ya faɗa saman royal bed ɗinsa ya shiga surutar idonsa fal hawaye wanda ya hana idonsa zubarsu baison raunin da yake ɓuyewa ya baiyya a haka bacci yay gaba dashi. Ƙarfe 7 alam ɗin ɗakin ya fara ƙara wanda ya haddasa farkawarsa,a hankali ya shiga buɗe dara-daran manyan idonsa wanda suke cike da magagin bacci,a hankali ya miƙa hannunsa ya kashe ƙarar Alam ɗin, kansa ya ɗaga ya duba lokaci da sauri ya diro daga kan bed ɗin bakinsa ɗauke da sallati ganin ko sallah baiyi ba,ɗakin yabi da kallo ganin duk ya hargitse tunanin abinda ya faru ya shigayi amma ya gagara tunanin komai,toilet ya faɗa a gurgoje yay wanda tare da ɗaura alwala da brush kansa da gashin faffaɗan ƙirjinsa na ɗigar ruwa haka ya zura wata farar jallabiya ya nemi gefe ya shimfiɗa prayer mat ya data sallah ya idarwa ya shiga salatin annabi da neman ya fiyarsa akan lattin da yayi yana idarwa ya shafa,cikin sauri ya shiga gyara ɗakin yana gamawa ya faɗa kan bed ɗinsa tare da lumshe idonta yana jin kamar ya aikata wani abu ba dai² ba a cikin rayuwarsa amma ya manta komai bazai iya tuna komai ba amma ya najin babu daɗi a zuciyarsa,wani baƙin ciki da takaici haɗi da tsanar rayuwarsa ya dirar masa,a haka yay ta juyi yana dafe kansa har bacci yay nasarar ɗaukesa. Maidugori road Misalin ƙarfe 10:30 gidansu Faisal ya gama ciki da ƴan uwa kowa yasha kwalliya ban damu da ganin nan ba,a hankali na duba saman bene jin an rangaɗa muɗa tare da faɗin"Masha Allah" wow kawai na faɗa Faisal ne cikin shigar manya kaya yasha farar shadda gezner ɗinkin riga da wando da kuma babbar riga,kansa sanye da black ɗin hula mai tangaran sai sheƙi yake,ƙafarsa sanye take black ɗin cobbet shoe mai tsadar gaske,fuskarsa ɗauke da zallar murmushi wanda yake ƙawata fuskarsa,Faisal kyakkyawa ne ajin farko dukkan inda ake faɗar cikar kamala da kuma ta ƙama Faisal yakai fari ne tas yana da zagayayyiyar fuska mai ɗauke da ɗan gemu but babu saje idonsa farine tas,cikin kuzari yake sakkowa daga saman benen zuwa ƙasa babu inda ya nufa sai wajan mahaifiyarsa yana zuwa ya faɗa jikinta tare da sauke ajjiyar zuciya yace"Ammina zamu tafi asa mana albarka"dariya Anty Billy tayi masa tana faɗin"tab there's a big problems fa,today is ur weeding day but ji yadda kake abu kamar ɗan goye"kwaɓe fuska yay tare da kallon Ammi yace"Ammina kin ganta ko?"murmushi tayi masa irin na mayan mata tace"little forget about her sister kaji,Ubangiji yay maka albarka kaida iyalinka Allah yasa maka farin ciki kamar yadda ka farantamin naga ranar aurenka Allah ya nunamin yaran da zaka haifa nima naga jikoki na,my little an girma za'a guda abar Ammi"ta faɗa tana maida ƙwallar idonta,faɗaɗa fuskarsa yay tare da faɗin "Madallah da addu'ar uwa ta gari ina roƙan Allah ya bawa Ammina nisan kwana domin taga yaran da zan haifa"riƙe baki Anty billy tayi tare da faɗin"wonderfull shall never end"gwalo yay bata tare da faɗin"ban bari ki ɓatamin rai a rana mafi muhimmanci a wajena bye Ammina"ya faɗa tare dayi mata peak a forehead ɗinta ya fice. Ƙofar gidan Alhj Mustapha Rano ciki yake da ɗumbin jama'a wanda suka halacci ɗaurin auren ƴar tasa,manya-manyan gari da ƴan siyayasa haɗi da ƴan jaridu,saura ƴan minutes a ɗaura auren FAHAD ya fito sanye da wani milk ɗin boyal mai shegen kyau sosai cikin yadin da yake da manyan zane kuma shara-shara ana ganin farar singlet ɗin daya saka, ya saka cofie ɗin hular mai taushi dan bata fiya haske ba,ga sajen fuskarsa sai sheƙi yake yay kwance luff a fuskarsa,ya manne idonsa da farin glass mai tsaka irin na likitoci dan kana iya ganin eye ball ɗinsa wanda suka ƙanƙance haɗi da ƙara lumshe su da yake,saurin juyawa yay domin ɗakko wayarsa daya manta a flat ɗinsa,amma kallamar da yaji maroƙin ya faɗa ita tasa zuciyarsa bugawa da ƙarfi idonsa ware waje tare da zare glass ɗin idonsa cikin ƙaraji yace "WHAT?. *(Kada ku manta da Comments da Kuma share haɗi da Vote domin shine jin daɗin Sarauta,ina son ayi share ɗinsa ya basu ko ina harma da inda banyi tunani ba,idan kukaimin hakan kun faramin rai sosai🥰😍 i luv u my real fans na TELEGRAM WASAPP WATTPAD FACEBOOK)* *Wattpad@Nimcluv* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ *💖JUYAYI💖* *N.S* EPISODE 3 Shadow *MSS FLOWER* ```Never lie to someone who trusts you,And never trust someone who lies to you👌🏻``` *Thank you soo much my Elizabeth dedicated to you* .....Wata irin bugawa zuciyar FAHAD tayi lokacin guda yaji duniyar na juya masa,lumshe lumtsumammun idonsa yay yana mai baƙin ciki rayuwarsa a halin yanzu,da ace duniya za taji abinda ya aikata wa ƴar uwarsa babu shakka dasai an samu mai tsine masa,bai ƙara tabbatar da abinda yaji ba saida Maroƙin ya ƙara faɗin *An ɗaura auren Faisal Khalil Jibaɗo da Amaryarsa Lubna Mustapha Rano akan sadakin dubu hamsin Allah ubangiji yaywa rayuwarsu albarka* cikin sauri Fahad ya juya tare da ficewa daga wajan darect wajan haɗaɗɗiyar motarsa ya nufa blue black mai ƙirar Ferari 2020,yana zuwa yasa key ya buɗe motar tare da faɗawa ciki ya jata da guda yabar anguwar tasu,Abdul abokin ango shine ya ɗan taɓa ango tare dayi masu showing motar Fahad wacce ta tashi daga wajan yace"frend i think he is ur wife's brother right?"taɓe baki Faisal yay domin haushin Fahad ya kejin haka nan musamman miskilancinsa da kuma girman kansa shi yafi bashi haushi,jin shuru yay yawa yasa Abdul ƙara taɓu Faisal yace"kai dilla i'm talking to you ka naji kayi shuru"kallon Abdul Faisal yay kafin yace"yerh he is"yana faɗin hakan ya kalli Najeeb yace"les'go muje naga amaryata"dariya sukayi gaba ɗaya sannan suka shige cikim Compound ɗin gidan. Can cikin gida kowa Najma ce zaune gaban dressing mirrow ta caɓa uban ado tayi shiga ta alfarma,Sanye take cikin farin lass wanda yasha manyan flowers mai red colour,Kanta saman dressing mirrow haka nan yau ta kejin faɗuwar gaba tunaninsa gaba ɗaya ya hanata sukuni dajin daɗi,bata iya ganin komai cikin eye ball ɗinta sai kyakkyawan sexcy eyes ɗinsa mai masifar kyau da kuma kwarjini,Soyayyarsa tayi mata masifar kamu a lokacin da ba tayi tunanin hakan ba,wasu hawayen tausayin kanta ne suka shiga zubuwa daga cikin idonta,yaya zatai da soyayyarsa shin ta gaya masa tana sonsa ko ta rabu dashi domin tasan yay mata nisan da ba zata iya kamushi ba,ƙatuwar wayarta ta ɗakko tare da zubawa kyakkyawar fuskarsa ido mai cike da haiba da kuma kwarjini,lumshe ido tayi tare da manna wayar a saitin zuciyarta,cikin muryar kuka tace"i luv you soo much zanci gaba da sonka har ƙarshen rayuwata koda sonka zai zama ajalina,Ubangiji ka fini sanin dai² ina roƙonka ka yayemin abinda na keji game da bawan Allah nan naka ya rabb ka kawowa zuciyata ɗauki" ta faɗa lokacin da wasu hawayen na ƙara zubu mata,turo ƙofar da akai da saurin ne yasa tayi saurin goge hawayen fuskarta tare da gyara ɗaurin kanta,a hankali ta juyo tare da zubawa wacce ta shigo ido,ɗan girgiza kanta tayi tana mamakin sauyawar ƙanwar tata a kwana biyun nan,tashi ta ƙarasa wajanta tare da kama hannunta tace"what happen again Lilin Faisal today is ur special day banga abinda zai saki kuka at this time ba,Ya kamata ace kinfi kowa farin ciki bcsz u have what u need"kasa cewa komai Lili sai jikin Najma data faɗa tare da saka kuka,Sosai kukan ke taɓa zuciyan Najma a hankali tasa hannu ta shiga bubbuga bayanta tare da rarrashinta,Lili bata da riƙe mutum sannan bata fiye saka abu a ranta ba,dan haka ta kasa ɓuye abunda yake damunta ƙara lafe jikin ƴar uwarta tayi ta shiga sauke ajjiyar zuciya,cire jikinta tayi daga jikin Najma tayi tare dasa hannu ta riƙe hannun Najman tace"Yaya Najma ki taimakeni ki taimaki rayuwata ina son kimin wata alfarma pls kada kice a'a"..baki da wani abu da zaki nema a wajanki na kasa yi maki bana da kowa wanda ya huce keda Yaya Fahad,bana tunanin akwai abinda zai gagareni na kasa yi maku shi,nayi maki alƙawarin ko menene zan maki"Najma ta faɗa tana ƙara matse hannun Lili jin jikinta ya ɗauki zafi,a karo na farko tun bayan abinda ya faru tsakaninsu da Fahad tayi murmushi tare da kawar da abinda yake ranta tace"ina son kije flat ɗin saukar baƙi ki zauna ki karɓi Faisal a zummar nice,banson ya ganni sai a gidansa pls"waro ido Najma tayi tare da furta"lallai Lubna baki da hankali i can't gsky,he is not blind da zai kasa gane ni haba think before you talk"ƙwaɓe fuska Lili tayi tare dayin raurau da ido tace"but you promise me tun kafin kiji mene and banda abinki ai zaki iya kashe hasken ɗakin saiki shiga shadow kinga ɗakin nada duhu he can't understand any indai bake kika bada hanyar a gane ba,dan Allah kimin kodan farin ciki na pls we have are the same voice and body dan haka komai zai dafi dai² by thw grace of God"jinjina kai Najma tayi tana ganin haukan sister ɗinta ta,Ganin ta riga da tayi mata alƙawari yasa tace"ok fine zani are you happy?"taune lips ɗinta na ƙasa Lili tayi ba tare data kalli Najma ba tace"Thank you"tana faɗin hakan tasa kai ta fice daga cikin ɗakin,Lili na ficewa Najma ta ƙarasa gaban dressing mirrow tana zuba kanta ido ta cikin madubi,ganin bata da matsalar komai kuma make up ɗinta ko Amarya albarka yasa tayi murmushin gefen baki wanda kana ganinsa na zallar baƙin cikine,saman bata son zuwa wajan Faisal as his wife bayan she is not,Kwalin turarenta ta ɗakko irin na Lili ta shiga feshe jikinta dashi saida taji komai yayi sannan ta ajjiye turaren ta ƙara goga pink lipstics a lips ɗinta mai ɗan faɗi,wajan wadrope ta isa tare da ɗakko vail ɗinta ta yafa saman kanta cikin sauri ta fita daga ɗakinta tare da kullewa ta nufi guest room some minutes ta isa tana shiga ta fara gashe gloves ɗin ɗakin yaza mana baka iya ganin komai a cikin parlon harma da cikin bedroom ɗin,a hankali ta juya tare da nufar duguwar sofa ta zauna hasken kayan jikinta shi zai tabbatar maka akwai mutum a cikin parlo. FAHAD Gudu yake bana wasa ba ya nayi yana cije lips ɗinsa shi kansa baisan inda ya nufa ba,yabar gidanne sbd bazai iya cigaba da sauraran abinda Maroƙin ke faɗa ba,saida yay nisa da gida sosai sannan yay gangara gefen titi tare dayin parking a wajan ya kashe motar,fesar da numfashi mai zafi ta cikin bakinsa,yanzu wanne kallo mijinta zai mata zai iya yi mata uzuri akan bata da laifi ko kuma zai mata kallon ƴar isaka wacce ta bada mutuncinta a waje kafin taje gidan mijinta,ko kuma yaje yakai kansa wajan wajan ƴan sanda ya gaya masu gskyar lamarin,"no Fahad think about that hakan ba mai yiwuwa bane" hannunsa ya tura cikin tulin sumar kansa ya hargitsa ta,cikin zazzaƙar muryarsa mai fita a hankali yace"ya rabb what should i do now?" yana ganin kawai zaibar wannan maganar ta zama *SICRET ISSUE* ganin bashi da wani mafita yasa ya fara karanto sunayen Allah tsarkaka a haka har yaji zuciyarsa ta fara sanyi,Gorar ruwa ya ɗauka a gefen kujerarsa ya ɓalle murfin haɗi da kaf bakinsa akan gorar ruwan ya shiga ƙwanƙwaɗa saida ya shaye tas sannan ya rufe emty rubar ya ajjiye a side ɗin mai zaman banza,a lokaci ya duba yaga wajan 12pm sanin cewa yana da tiater 12:30 yasa shi yiwa motar key tare da harbata tsakiyar titi ya nufi AMINU KANO TEACHING HOPITAL. Kasan cewar gudu yake sosai yasa lokacin kaɗan ya isa asibitin,a compound na asibitin yay parking motarsa tare da fituwa daga cikin motar harabar asibitin ya shiga ƙarewa kallo na wani lokacin kafin ya zura hannayensa cikin aljihun wandonsa ya fara tafiyarsa wacce take nuni da cewa tabbas ya isa namiji cike da kuzari haɗi izza da gadara yake tafiya har isa emagency yana zuwa mutane suka fara tururowar gaishe shi,idonsa kawai yake lumshe tare da waresu akan mutunan hakan ya tabbatar masu da amsawa yake,a haka ya isa office ɗinsa yana shiga ya zauna tare da fara duba files ɗin gabansa,knoking ƙofarsa yana ji yay burus kamar baiji ba,cigaba da buga ƙofar akai tsaki yaje tare da cije lips ɗinsa sbd tsaɓar baison mgn da takura yasa faɗin cewa"who is dat?"daga can waje matashiyar budurwar ta ƙara langwashe murya cikin salo tace"sir dr Layler speaking"lumshe idonsa yay tare da ɗan jujjuya kujerar da yake kai wajan 5min ya ɗauka kafin yace"come in"handle ɗin ƙofar Layler ta kama tare da murɗawa ta shiga cikin,da sallama ta shiga a kwance saman duguwar kujera ya lumshe idonsa,ajjiyar zuciya Layler ta sauke kafin taja ƙafafunta ta ƙarasa wajansa tare da durƙusawa kusansa,cikin mayan so da kuma takai hannunta ta shafa kyakkyawan sajen dake gefen fuskarsa cikin wata makirar muryar tace"dr na u have to get ready it ardy 12:30pm yaron na cikin matsala"ta faɗa tana ɗura kanta saman faffaɗan ƙirjinsa,jin yay mata banza yasa ta kama hannunsa ta riƙe cikin nasa tare da faɗin"how long zamu kasance a haka,pls do something i really luv with all my heart mai yasa kake nuna ƙyama a gareni,kasan cewa ba mutum ne ke faɗawa soyayya ba soyayyace ke faɗawa mutum kaga bazan hana zuciyata sonka ba domin kana da abinda ya dace ko wacce ƴar mace ta soka,Nayi zaman jiranka na wasu shekaru gashi yanzu ka dawo sai wata hanya hanya kakemin,ware manyan manyan sexcy eyes ɗinsa yay tare da mannasu akanta,saurin ɗauke kanta tayi daga kallonsa dan ba zata iya jure kallon cikin ƙwayar idonsa ba,hannu yasa ya cireta a jiinsa ba tare da yace komai ba ya miƙe ya ɗauƙi green ɗin rigarsa ta aiki,cikin sauri ya zare farar rigar boyal ɗinsa nan faffaɗan ƙirjinsa ya bayyana wanda ya cika da yalwataccen baƙin gashi wanda yay luff a ƙirjin nasa,lumshe ido Layler tayi tana saƙa abubuwa da dama ta yadda za'ai ta mallaki dr cikin sauƙi,gani ba zata iya jure ganin jikinsa a haka ba yasa ta miƙe tare dayin waje,a ɗan hanzarce ya ƙarasa zura rigar aikin nasa cikin jarumta yasa kai ya fice daga office ɗin nasa babu inda ya tsaya cikin tiater room. LILI Bayan ta bar ɗakin Najma cikin sauri ta shige flat ɗin tana zuwa ta zura dugwan hijab ɗinta tare da saka liƙaf wayarta ta ɗauka tare da key ɗin motar ta tayi waje,da sauri² take tafiya domin barin parlon don bata so taga Faisal bare hankalinta ya tashi dan she ardy make a decision bata jin ko zata mutu zata sauya abinda tayi niya, kanta a ƙasa take tafiya ta nayi tana duba cikin jakarta daf da zata fice daga babban parlon sukayi karo da juna cikin saurin taja baya tare da ratsa ta gefensa ta huce ganin babu kowa a compound na gidansu yasa tayi saurin ƙara sawa wajan motarta ta shiga tana shiga ta rufe motar tare da sakin wani marayan kuka ita kaɗai tasan abinda yake damunta inama wani zai fahimci halinda take ciki koya tausaya mata, cikin kukan take faɗin" BOOBI ka cuceni ka cuci rayuwata ka cuci mai sona ka wargatsa duk wani farin cikin masoya na tsaneka har abada bazan taɓa sonka ba,abinda kayimin Allah shine zai sakamin ba wani ba"jin numfashinta na ɗaukewa yasa tayi saurin ɗakko *INHELER* ta shiga shaƙa da sauri saida ya lafa mata sannan tayiwa motar key tare da fisgarta da ƙarfi tayi waje. Faisal bin bayanta yay da kallo ya najin kamar yabi bayanta yaga wacce mai irin sufar matarsa,wata zuciyarce tace"mezai saka wify ta fita a wannan yanayin"da wannan tunanin yay hanyar guest room yana shiga ya tsaya ganin parlon yay duhu murmushi yay ganinta zaune akan sofa baya iya ganin face ɗinta sai hasken kayanta,a hankali ya yaka zuwa gareta yana zuwa yasa duka hannayensa ya miƙar da ita tsaye tare da faɗin"amincin Allah ya tabbata ga ruhin Faisal sai yau Ubangiji ya bani damar taɓa jikinki a iya shekarun da muka kwashe Aure rahama ne,Allah ya nunamin ranar da zaki haifamin yara kyawawa masu kama dake"ita dai Najma binsa kawai tayi da kallon zuciyar banda bada sauti babu abinda take,a hankali take control kanta ganin abinda take ɓuye yana shirin bayyana kansa,kasa ce masa komai tayi sai sunkuyar da kanta kasa tayi tana sauraran bugun zuciyarta dake fita da saurin,bata tsinke da lamarin Faisal ba saida ta jita saman ƙirjinsa yana faman shafa kwantaccen gashin kanta daya cire mata ɗan kwalin kanta,wani yamm yarr taji a jikinta gaba daya gargasar jikinta ta shiga miƙewa,tana jin wata muguwar faɗuwar gaba na ziyartar ta,ƙoƙarin kwace kanta take ganin abinda yake bata bai dace ba domin shiɗin ba muharraminta bane Mijin ƙanwarta ne,ƙara matseta yay a jikinsa tare da manna mata sumba a tsakiyar wuyanta ajjiyar zuciya ta sauke ba shiri ta lafe a jikinsa tana sauke numfashi akai²,gaba ɗaya brain ɗinta ce ta tsaya da aiki ta farajin baƙon yanayi na shigarta a hankali eye ball ɗinsa keyi mata gizo tana jin wata kewarsa na ratsa dukkan wata gaba ta jikinta,wasu hawaye ne suka shiga zuba daga cikin idonta sai yaushe ne zata ganshi? Sai yaushe zata fallasa asirin zuciyarta,jin hawaye mai zafi na sauka a ƙirjinsa yasa yay saurin ɗagota daga jikinsa hannunsa na rawa ya taɓa idonta domin tabbatar da abinda ya keji"ayya my beby boo ba sai kinyi kuka zai tabbatar min kina cikin farin ciki ba,i'm always be ur side i luv you for rever and ever my wify ina ji kamar na mai daki zuciyata na huta da abinda na keji game da ke"ganta ta ɗaga a hankali ta zuba masa ido bata iya ganin komai sai jajayen laɓɓansa,shima ita yake kallo musamman lips ɗinta da suka ji lipstic,hannunsa ya saka ya shiga shafa lips ɗin nata mai ɗan faɗi matsuwa yay daf da iya cikin kasalalliyar murya yace"i need ur cute lips"kafin tayi wani tunanin taji ya haɗe bakinsu waje guda,jikin Najma ne ya fara rawa jin baƙon yanayin daya ziyarce ta a lokacin da bata shirya masa ba,lumshe idonta tayi tana mai jin wai daɗi na ratsata cikin goshewar hankali itama ta cafki lips ɗinsa. *😘Nimcy luv ce ina sauraran Comments ɗinku wanda shi zai tabbatarmin kuna tare dani pls and pls dan soyyayar da kukemin ina son duk wanda ya karanta yay share👐🏻Son so nake maku my fans😍* Wattpad@NimcyluvNimcyluv *💖JUYAYI💖* *N.S* EPISODE 4 Relationships are like a Book. It takes years to write but second to burn. *DADICATED TO YOU👉🏼🧝🏻‍♀️ SIS KAUSAR AGLAN NISSA🥰* kiji daɗinki ......Tattara dukkan wani feelings da emotion dake gaggar jikinta haɗi da zuciyarta tayi zuwa garesa,A lokaci guda wata wutar feelings ɗinsa ta tasu mata gaba ɗaya ta manta dawa dake tare bare ta gojewa afkuwar wani abu a tsakaninsu,Inama wanda take muradin kasancewa dashi ne tabbas data nuna masa zallar ƙauna,yadda Faisal ke mata ne yasa ta ƙara haukacewa hakan yasa ta ƙara lafewa jikinsa ta shiga fitar da numfashi mai ɗan sauti,babu abinda ke yawo a cikin eyes ball ɗinta sai kyakkyawar surarsa haɗi da beautifull sexcy eyes ɗinsa wanda yake ƙara dilmiyar da ita a ƙaunar,Wani daɗi ne ke ziyarta dukkan wata gaba ta jikinta sosai ta kejin daɗin silver ɗinsa da take zuga ta riga data manta da MIJIN ƘANWARTA take,A hankali ta ƙara shigewa jikinsa tare da ƙara ƙarfafa abinda yake matan. Sosai zucyar Fahad ke beating very fans,gefe guda kuma ji yake kamar ana buga masa wani abu a tsakiyar kansa,dalilin hakan yasa jijiyoyin kansa sukai raɗa² yayinda jikinsa ya shiga rawa dukkan abinda yake mata yi kawai yake dan yaga tana buƙata amma sam ba daɗinsa ya keji ba,wani wawan numfashi ya sakar mata mai zafin gaske a tsakiyar bakinta,A zafafe ya shiga zuge zip ɗin rigarta jin mararsa tayi wani irin murɗawa haɗi da kumbura kamar zata fashe. Jin yana ƙoƙarin sutale mata riga yasa tayi saurin dawowa hayyacinta tare da buɗe baki daɗan ƙarfi tace" no Najma con he is my sister's husband how can that happen Astagafirullah"da sauri tayi baya haɗi girgiza da kuma rufe bakinta da tafi hannunta ta shiga ƙifƙifta idonta tana tsoran ko yaji abinda tace,Shikam banda Lilinsa babu abinda yake ganin a cikin idonsa gaba ɗaya brain ɗinsa tsaya tayi da aiki jin wani abu ya sukesa a saitin zuciyarsa ba tare daya fahimci abinda take faɗi ba yay kanta,cikin sauri ta zulle tare dayin waje tabar parlon baƙin,Ɗan tsayawa tayi ta saita nutsuwarta tare da gyara zaman rigarta a hankali ta fice daga gidan gaba ɗaga darect hanyar da zata kaita Lambun gidan tayi tana zuwa ta zauna ƙansar shuƙar Fasadabir da yay girma sosai haɗi da nuna,Lambun cike yake da shuke² na fruit kala²,cure jikinta tayi waje guda yayinda ta shiga sauke ajjiyar zuciya akai² kamar wacce tayi tseren gudu,jin wani abu na binta kamar kiyashi yasa ta ƙara cure jikinta waje guda yadda abin keyi mata wani yamm yarr ajikine ya sata fashewa da kuka,saidai tayi mai isarta sannan ta miƙe tare da ficewa daga Lambun kai tsaye bedroom ɗinta ta nufa tana shiga ta faɗa saman bed,Lumshe ido tayi tana jin wani fitanan feelings na ƙara tasu mata wanda bata san na menene ba,Juyi ta shigayi a kan makeken royal bed ɗin nata da ace mutum ke ɗurama kansa son wani babu shakka da tuni ta cire sonsa a zuciyarta ta fahimci ita kalan ƙaddararta ce haka son wanda baisan ta nayi ba,A hankali moment ɗinsu na ɗazu ita da Faisal ya shiga dawowa cikin brain ɗinta ƙara lafewa tayi a tsakiyar bed ɗin cikin abinda bai huce 10min ba bacci yay gaba da ita. Bayan fitar Najma Faisal ji yay kamar ya zunduma ihu sbd wata irin azaba data ziyarci dukkan wata ƙofa dake jikinsa,a zafafe ya dunƙule hannu ya kaiwa wool naushin kafin yaɗan saki ƙara mai sauti jin yadda mararsa ke murɗa masa,Jikinsa ne ya shiga rawa yayinda jijiyoyin kansa suka fito raɗaɗa baya yaja kaɗan tare da faɗawa saman duguwar sofar dake gefensa,A hankali ya runtsa idonsa sbd a zabar zafin da ya keji a gaggauce ya fara bawa kansa taimakon gaggawa lumshe ido yay tare da ƙanƙame jikinsa ya saki ƙara kafin ya lafe jikin sofar hakan ya tabbatar daya samu nutsuwa daga pain ɗin daya keji,A kasalance ya miƙe tare da saita nutsuwarsa yay waje,tunda ya fita Abdull ya zuba masa ido ganin yadda yake haɗa hanya gane hakan da yayne yasa ya haɗe ransa,Yana ƙarasuwa wajan frnds ɗin nasa Abdull ya tuntsure da dry tare da faɗin "Jaraba da tsakar rana haka wlh my eyes can't stop looking you when you are doing..dan nasan za aga true luv"Najeeb ne ya karɓe zancen ta hanyar faɗin"sai aje a nemi lemon tsami ko a samu sauƙi jan kwaluwa kai da akai"baki Faisal ya taɓe haɗi da faɗin"na you sabi"yana faɗin hakan ya faɗa motar Kabeer tare da rufe ƙofar dan gaba ɗaya sun bashi haushi,Cikin sauri suma suka shige motar a hankali suke cinna hancin motocin zuwa waje a haka har suka fice daga cikin gidan. LILI Zaune take gaban dr Layler tana shassheƙar kuka wanda ita kanta bata san na mene ba,da ace kuka na maganin damuwa da tuni damuwarta ta daɗe da yayewa daga cikin zuciyarta,Tabbas koda ace kuka na maganin damuwa tayi imanin wannan damuwarta ta kuka bai isa yay mata magani ba,bata da kamar dr Layler duk da cewa ta girmeta nesa ba kusa ba amma bata iya ɓuye mata damuwar dake kwance ƙasan zuciyarta ba,dr Layler zubawa Lili ido tayi ba tare data hanata kukan da take ba da ace itama tana da ikon kukan a wannan lokacin data daɗe dayi kota samu sauƙi abunda yake damunta a zuciya,Tana masa mahaukacin so ta yadda bakinta bazai iya faɗin a dadin son da take masa a cikin zuciyarta ba, Tunanin mafita take amma still bata samu wani hanya da zata cimma buƙatar ta ba,Ganin kukan nata yay yawa ne yasa ta shafa kanta a hankali tace"Lubna a ina kika taɓa ganin kuka ya zama maganin yayewar damuwar mutum? Kuka baya maganin komai face cefa mutum cikin damuwa ki zama mai ta wakkali ki zama irin matan da babu wanda ya isa ya sauya masu ra'ayinsu,Ki zama mace da take ɓuye rauninta haɗi da damuwarta ta yadda babu wanda zai iya ganewa,Yanzu kizumin kina kuka shin kuka kikeso nayi nima ko kinsan abinda na keji a raina nima so pls stop cry kinji Lilin Boobi" jin ta ambaci Boobi yasa Lili ƙara fashewa da kuka dan babu sunan wanda ta tsani jin irin sunan yayan nata,da ƙyar dr Layler ta shawo kanta ta labarta mata dukkan abinda dake faruwa har hukunci data ɗaukan naƙin auren Faisal tace a ɗaura dana Najma amma Dad yaƙi amince saida aka ɗaura da ita. Kallon dr Layler tayi kafin ta runtse idonta da ƙarfi haɗi da taune lips ɗinta na ƙasa ta najin zuciyarta na beating very past,ware manya-manyan idonta tayi akan dr Layler tayi kafin ta ware ƴan ma dai² tan laɓɓanta tace"ya kikeso nayi yanzu mai zancewa Faisal a lokacin daya fahimce i'm not virgin ina cikin damuwa fiye da tunaninki,Inajin ajikina akwai tarin ƙaddarorin da suke jirana a nan gaba saidai nasan komai da lokacinsa ita ƙaddara abace mara tabbas a koda yaushe tana iya sauyawa"takai ƙarshen maganar tana ƙara lumshe idonta haɗi curewa wajan guda sosai ta kejin kanta na mugun sarawa. Sosai maganar Lilin ta shigi dr Layler ganin idan ta nuna damuwarta a fili Lili zata ƙara shiga damuwa yasa ta basar tare da jinjina kanta tace"Amma Lubna yana da kyau a fara bincikar jikinki kafin mu tabbatar da abinda muke tunani.." saurin katseta Lili tayi ta hanyar faɗin "wanne bincike kike magana nida abin ya faru dani,Nasan inada ƙarantar shekaru amma hakan bazaisa na kasa gane abinda ke faruwa ba,Inada ilimi nasan menake" murmushi dr Layler tayi kana tace"nasan da hakan amma ki yarda da maganata pls"jinjina kai Lili tayi haɗi da lumshe gajiyayyun idonta few minutes ta ƙara waresu tare da mannasu akan dr Layler'n hakan da tayi ne ya tabbatarwa da Layler'n cewa Lili ta amince,wayarta ta ɗauka zatai kira sai kuma ta manta ardy ya shiga Tiater room,Ajjiye wayar tayi kana ta miƙe tsaye tare da riƙe hannun Lili suka fice daga Office ɗin gaba ɗaya. *Maidoguri road* Cikin nutsuwa motocinsu sukai parking a parking space,daɗan sauri ya buɗe murfin motar da ya fice daga ciki,Darect cikin gidansu ya nufa idonsa a lumshe yayinda yasa hannu ya dafe kansa dake barazanar tarwatsewa sosai ya kejin zazzaɓi haɗi da ciwon kai,a babban parlo ya tarar da Anty bily da Anty kausar cike da zulaya suka amsa masa sallamar da yay,bai ƙara kallon kowa a cikinsu ba duk da irin tsokanar da suke masa,ɗan gyara zama Anty kausar tayi kafin tace"meke faruwa da babban yayane?"hular kansa ya cire kafin ya yatsuna face yace"i'm ok"yana faɗin hakan ya haura saman benen a hankali ya murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin nasa,Yana shiga ya fara sutale kayan jikinsa yana sawa a datti close saida ya rage daga shi sai boxer sannan ya shige cikin toilet yana shiga ya haɗa ruwan zafi a cikin jacuzzie a hankali ya shige cikin ruwan wata sassanyar ajjiyar zuciya ya sauke jin yadda ruwan zafin yana ratsashi,lumshe idonsa yay a hankali moment ɗinsu na ɗazu shida Lilinsa ya fara dawowa cikin brain ɗinsa,Lokaci guda gargasar jikinta ta shiga buɗewa wani sanyi ya shiga ratsashi some minutes wani zazzafan zazzaɓi ya rufesa daƙyar ya samu yay wankan tare dayin brush ya ɗauka alwala,Ya fitu sanye da long peach ɗin towel a jikinsa,ko lotion bai iya shafawa ba a gaggauce ya zura jallabiya tare da gabatar d sallah yana idarwa ya faɗa samen bed ɗinsa tare da lulluɓa da balget ya shiga rawar sanyi a haka wani wahalallan bacci ya ɗaukesa. ..da kallo Anties ɗin nasa suka bisa harya ɓacewa ganinsa,kafin suyi magana Ammi ta shigo parlon hannunta ɗauke da place ɗin dambun nama,tana tafe tana ɗan ɗingisa ƙafarta sbd ciwon da take mata,A hankali ta samu ta zauna kusa da Anty kausar da sauri Anty billy ta dawo wajan mahaifiyartasu ta shiga matsa mata ƙafarta"naji dawowar motoci hala yaro nane ya dawo ko?"cewar Ammi Anty billy ce ta amshi zancen da cewa"you are right Ammi yaronki ya dawo amma baya cikin mind ɗinsa i think someting bad happened to him but I'm not sure" zare farin glass ɗin dake manne a idonta tayi dan tafi kowa sannin halin ɗan nata da kuma abinda yake sashi damuwa,Shuru tayi tana tunani a ranta kafin ta ɗauki wayarta ta shiga dailing number jinta a kashe ya ƙara tabbatar mata da akwai problm yauce ranar daya kamata ace yafi kowa farin ciki to mezai sashi damuwa har haka,kallon yaran nata tayi kafin tace"yushe zaku tafi gidajanku tunda angama biki sai kawo amarya"turo baki Billy tayi kafin tace"haba Ammi nifa 1week zanyi"ita kam Anty kausar ba tace komai ba daman bata fiye surutu ba,harara Ammi ta watsa mata tace"kinji sakalci wannan yana ɗaya daga cikin abinda yasa maza suke ƙara aure sbd shirme dan kinzu biki sai kinyi 1week wlh ko wacce ta ɓacemin da gani kuje ko fara shiri kafin gobe kowa ya huce gidansa"cikin sauri gaba ɗayansu suka miƙe tare da shigewa cikin bedroom ɗin da suka sauka. Can waje kowa bayan Faisal ya fita a mota shi kansa Kabeer saida yay murmushi ganin zallar abinda yake damunsa ya bayyana akan fuskarsa,basu ɓata lokaci ba suka ƙara yiwa motocinsu key tare da barin gidan darect Tahir guest place suka nufa domin a nan suka sauka. *NASARAWA* Wajene mai kyan gaske wanda yake cike da furanni masu kyau da ƙamshi tana sauye da wata red ɗin t.shirt wacce a gabanta akai mata ado da stone tare dayin rubutu da manyan baƙi aka saka MY HAPPINESS,A hankali ta ɗaga idonta tare da saukesu akansa yasha ado sai zabga ƙamshi yake amma fuskarsa babu walwala kana ganinsa zaka tabbatar yana cikin damuwar da bazai iya ɓuye taba kuma a koda yaushe sirrin zuciyarsa gaf yake da tunuwa musamman idan akai duba da yadda ya kejin faɗuwar gaba haɗi da bugawar zuciya,murmushi tayi mai cike da kissa jiki na rangaji ta miƙe tare da nufar inda yake zaune kansa a sama yana shaƙar ƙamshin furanni da suke zuba a wajan,Tana zuwa ta zauna kusansa tare da shigewa jikinsa ta ɗura kanta saitin zuciyarsa sosai ta kejin yadda heart ɗinsa ke beating,A hankali ya ware lumshasshun idanunsa tare da mannasu akanta cikin sauri ya ƙara matseta a jikinsa,Wani tattausan murmushi ya saka wanda ya kara bayyanar da zallan ƙyansa ganin fuskar da yake muradi ta bayyana a wajansa a koda yaushe da ita yake kwana yake tashi bashi da burin daya huce ya sanyata cikin idonsa,Sai a yau mafarkinsa ya zama gsky bakinsa yakai dai² goshinta yana shirin sumbata yaji wata iska mai daɗin gske haɗi da wata cool voice ta doki cikin kunnanta bai gama tabbatar da muryar daya keso bace saida yaji ance"hakan da kake shirinyi dai² yake da bugawar zuciyata,kai nake muradin a koda yaushe mai yasa idonka ya rufe kake ƙoƙarin aikata abinda bai dace ba,i luv you for rever and ever da inajin sonka shine a jalina"da sauri ya hankaɗe wacce ke jikinsa ya miƙe da gudu ya nufi inda ya kejin muryar yana gaf da ƙarasawa yaji saukar wani abu mai kama da itace ƙara ya saki tare da sulalewa a wajan jini ya shiga zuba daga cikin kansa,Da sauri ta yarda itacen hannunta tayo kansa tare da jijjigashi tana ambatasan sunansa ganin baya numfashi ya tabbatar data kashesa. Wata ƙara ta fasa tare da faɗin "Bani na kashesa ba" tsaki Mamy taja wacce ta daɗe da shigowa cikin ɗakin Najma ganin tana bacci yasa bata tasheta ba. Firgigit ta farka daga nauyayyen baccin daya ɗauketa tare dayin addu'ar duk da tazu bakinta,Shuru tayi tana tunanin mafarkin da tayi yanzu gaba ɗaya bata lura da Mamy da take kusa da ita ba saijin saukar muryarta tayi"mutum yayta bacci har la'asar ba dole ya dunga shirme mafarkai ba,maza tashi ki shirya kizu flat ɗin Daddynku yana jiranku keda Lili don't wast our tym ok"da kallo Najma tabi Mamy harta ɓacewa ganinta cikin sauri ta miƙe tare da nufar toilet Tana shiga ta zare kayan jikinta tare da sakarwa kanta shower wanka tayi sannan tayi wankan tsarki domin bata yadda da kanta ba,brush tayi tare da ɗaura alwala saida ta gama komai sannan ta fitu daga cikin toilet ɗin a gaggauce ta gama shirinta tare da gabatar da sallah tana idarwa Mamy na ƙara shiguwa,rusunawa tayi tare da faɗin"barka da yamma Mamy".."yauwa beb maza kije ki tahu da ƴar ukarki Daddynku na nemanku yanzu na faɗa masa nazu na gaya maki amma ya ƙara turoni"cike da fargaba Najma tace"ok Mamy we will be there insha Allah"murmushi Mamy tayi tare da ƙarewa bedroom ɗin Najma kallo kafin ta miƙe tayi waje,Tana fita Najma taja wayarta da saurin ta shiga kiran Lili amma bata shiga. HOSPITAL Suna fita babu inda suka nufa sai LAV ɗakin gwaje²,dr Layler ce ta bawa Lili umarnin kwanciya akan wani ɗanma dai-daicin gado wanda ke cikin Lav ɗin,cike da ƙwarewa ta farayi mata duk gwaje-gwajen daya kamata,ido ta ware waje ganin abinda result ɗin ya bata,hannu tasa ta shiga share zufar dake zuba daga kanta kafin wasu hawayen tusayin Lili'n suka shiga sauka daga cikin idonta,zama tayi daɓas akan wata sofa tare da ƙifa kanta tama rasa meza tace dan gane da wannan babban labarin yaya yaruwar Lubna zata ƙare,Murmushi baƙin ciki Lili tayi kana ta miƙe zaune lumshe sleepyn eyes ɗinta tayi tare da cije lips ɗinta tace"now you can agree with me rayuwata ta lalace bana da wani saurin amfani daga nan ba zanje gida ba wlh guduwa zanyi kinga dole a suke aurena da Faisal"cike da tashin hankali dr Layler ya kalleta kafin ta miƙe tsaye ta ƙarasu wajan Lili tace. *(Ruwan Comments ɗinku kawai nake jira kafin gobe mu ɗura dan ko fara wasan ba'ai ba👯🏻‍♀️👯🏻‍♀️😍🥰aƙi Comment na hau bed nayi baccina mai cike da farin ciki🤗 aha kada a manta da share👌🏻)* *Wattpad@Nimcyluv* *Sun/Dec/2020 1:27pm* *💖JUYAYI💖* *N.S* EPISODE 5 When someone with mouth odour talking to you show ur reaction using emoji.🤷🏻‍♀️💁🏻‍♀️😂😅 ......shuru dr Layler tayi tana sauke numfashi tare da zubawa Lili idanu tana mai jin tausayinta cikin ranta,gajiya Lili tayi da kallon da dr Layler keyi mata hakan yasa tace"uhm i'm with you ke nake saurare" wani ihu dr Layler tayi tare da rungome Lili tace"you still virgin Lubna ke budurwace"kallon kin rainamin hankali tayiwa dr Layler tare da zura hijab ɗinta ta ɗauki wayarta da hand bag ɗinta saida ta gama komai sannan ta kalli dr Layler tace"you're so funny wlh,how can that happy da zaki ce am virgin i'm not baby am adult nasan komai idan ni virgin ce what about the blood?"wasu files dr Layler ta ɗauko tare da result ɗin scaning ɗin da tayi mata kafin ta kalli Lili cikin nutsuwa da kuma fahimta tace"Look Lubna yana da kyau ki ajjiye ƙuruciyarki a gefe kiyi tunanin future ɗinki,zai iya zama ace yay ƙoƙarin rapping ɗinki amma bai samu dama ba dalilin hakan kika samu ciwo a jikinki,sannan ciwon da ki kaji a ƙasanki zai iya zama yay romance ɗinki before yay ƙoƙarin shigarki,akwai wasu halittu a jikin mace wanda basa aiki sai lokacin da namiji ya raɓeta musamman ga budurwa,lokacin da ake romance da mace a lokacinne suke buɗewa tare da kumbura shine za kiji mararki ta kumbura tare da ɗaurewa a hankali kuma zasu fara fitar da wani ruwa idan abun yay nisa idan akayiwa mace haka shine dukkan wani feelings ɗinta ke fituwa abun yay mata daɗi shine ba'a samun wahala wajan shiga jikin mace,amma abinda ya bani mamaki duk wannan halittun basu nuna sun taɓa aiki a jikinki ba i'm scared Lili labarin nan yabani tsoro amma thank God tunda abinda muke tsoro bai faru ba,kici gaba da addu'a amma akwai Ɓoyayyen labarin cikin rayuwarki wannan abun yasa brain ɗina JUYAYI". Cike da farin ciki mara misaltuwa Lili ta rungome dr Layler tare da sakin kuka wanda bata san dalilin yinshi ba,sosai ta samu farin ciki a zuciyarsa ta najin yanzu bata da wata sauran damuwa hatta Yayan Boobi taji bata da wani problm dashi am dwon heart ɗinta sosai take beating very past,raba tsaninsu dr Layler tayi kafin ta ƙara da cewa"maza jeki ga mijinki Lili yanzu ne lokacinki ya suma kada kibar duk wata hanya da wata ƴar mace ko wani ɗa namiji ya shiga rayuwarka har saku a JUYAYIN da zaku kasa gane abinda ke tsakanin,ki zama mace mai jajircewa ki rage wannan shurun naki,ki zama mace mai tsayawa akan ra'ayinta all the best bebyn Boobi no more faɗa tsakaninki da yayanki oyyah go". Cikin saurin Lili ta fice daga office ɗin babu inda ta tsaya sai compound ɗin asibitin inda ta ajjiye motart,Tana zuwa ta buɗe motar tare dayin bisimillah ta faɗa ciki bata tsaya jiran komai ba ta yiwa motar key da gudu ta fice daga cikin asibitin. Da kallo dr Layler tabi bayan Lili haka kawai taji wata far gaba mai kama da tsoro sun shigeta,tabbas she still virgin amma tayaya za'ai brother yaywa sister nashi haka,shiyasa a kace duk inda mace da namiji suka keɓe na ukunsu sheɗanne,haka kawai ta samu kanta da son ganin yayan Lili wanda taji tana gaya masa suna Boobi,Lumshe ido tayi lokacin data tuna da farin cikinta wanda ta kejin ko duk mutanan duniya zasu haɗu babu wanda ya isa ya hanata mallakarsa a matsayin mijinta,bata son kowa ya raɓu dashi hatta ƴan uwansa tafi son ace komai nasa itace ta zama ruwa da tsokar jikinsa(uhm abeg Halima muhamman umar come carry ur ƴar uwa😅). Ji tayi aikin duk ya dameta babu wanda ta keson gani sai dr ɗinta cike da zumuɗi ta cire farar rigar jikinta ganin ardy tym ɗin tashi yaya dan wajan 5:30 wata blue black ɗin abaya ta ɗauka ta saka a jikinta tare dayin rolling da vail ɗin rigar a kanta wani peach ɗin lipstic ta ɗauka a cikin hand bag ɗinta ta shafa saman faffaɗan lips ɗinta mai ɗan duhu tana gabawa ta ɗauki perfume ta shiga fesawa a jikinta dashi saida ta gama komai sannan ta fice daga office'n ta nufi office ɗinsa,A hankali ta shiga knoking amma shuru ba'ai magana ba kasancewar tasan halinsa bazai magana ba musamman idan yasan itace,Murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga,fituwarsa kenan daga cikin toilet ya wasa ruwa yana ƙoƙarin saka rigarsa ta shigo ciki,Idonta ne ya sauka a gashin ƙirjinsa da yake baƙi siɗiƙ yay luff sai ɗigar ruwa yake ido ta lumshe ta najin wani abu nayi mata yawo a jiki musamman yadda lafiyayyiyar skin ɗinta ke zubar da ƴan ƙananun ruwa sai shaning take gaba ɗaya surar jikinsa abin kallonce musamman idan kayi duba da lafiyayyiyar arms ɗinsa wacce take a murɗe,lips ɗinsa ta zubawa ido ganin yadda yake ta taunesu tare da lumshe idonsa banda shi babu wanda taga yana yawan taune lips sai Lili ta rasa abinda su keji game da hakan,Murmushi tayi tare da zura lips ɗinta na ƙasa ciki bakinta ta haɗa da haƙoranta ta taune lips ɗinta cikin sauri ta fitu da harshenta tare dayin wata ƙara sbd azabar da taji,Tsaki Fahad yaja jin kamar zata fasa masa kai sbd ƙarar da tayi key ɗin motarsa ya ɗauka yana shirin fita tayi saurin shan gabansa tare da faɗin"Haba Fahad amma yana da kywu ka tsaya kaji me zance maka ko"lumshe idonta yay yana jin kamar ana buga masa guduma aka sbd tsananin ciwon da kansa yake masa,Ko kallonta bai yiba yana ƙoƙarin hucewa yaji ta shige jikinsa tare da sakin kukan munafurci da kissa"meye laifina dan zuciyata tasu wanda ya kamata ace ana sonsa,pls Fahad kaji tausayina wallahi ina sonka sosai dan Allah kada kasa sonka ya jani na aikata abinda bai dace ba"takai ƙarshen maganar tana ƙara ƙaleshi,lips ɗinsa ɗinsa na ƙasa ya shiga sucking a rayuwarsa ya tsani mace mai bibbiko matsifa shifa yana da hankali yasan mai yake tayaya take tunanin zaiso mace kamarta wacce bayyana tsaraici bayayi mata wahala ɗan tsaki yaja kana yasa hannunsa ya zareta daga jikinsa tare da kama hannunta suka fice daga office ɗin,Suna fita yay saurin sakinta tare da rufe office ɗin nasa,Baibi ta kanta ba ya huce harabar asibitin yana zuwa ya nufi wata ƙaramar motarsa mai kyan gaske wacce ake yanzu yana zuwa ya buɗe tare da ɗaga rigarsa ya zauna ya daɗe a cikin motar kafin yay mata key yabar asibitin da sauri. *Maiduguri road* A hankali ya shiga buɗe idonsa wanda sukai masa nauyin gaske sbd daɗewa da yayi yana bacci,bakinsa ɗauke da addu'ar tashi daga bacci ya gama ware idonsa da suka ƙanƙance sosai zallar damuwa ta bayya saman kan fuskarsa duk ƙoƙarinsa nason ɓuye abinda yake damunsa amma ya gagara yin hakan,sosai abinda sosai abinda sukai shida Najma keyi masa yawo a brain ɗinsa duk da cewa baisan cewa Yayar matarsa bace gaba ɗaya tunaninsa bbynsa ce,amma mai yasa rauni keson bayyana a tattare dashi mai yasan yake tsintar kansa cikin faɗuwar gaba haɗi da bugawar zuciya,Ganin baya da amsa ga kuma yadda yaji masallatai suna kiran sallar magrib yasa ya miƙe jiki a sanyaye ya shige toilet ɗin dake cikin ɗakinsa,yana shiga ya zare jallabiyar jikinsa tare da saita ruwan shower'n yazu daɗan ɗuminsa,a tsakiyar shower'n ya tsaya tare da sauke ajjiyar zuciya sbd yadda ruwan yake dukan jikinsa yana ratsa duka wata ƙofa ta gangar jikinsa,Ya daɗe ruwa na ratsashi kafin ya shiga yin wankan yana kammalawa yay brush tare da ɗaura alwala ya fitu daga cikin toilet,Wajan dressing mirrow ya nufa ya shiga tsane kansa wani lotion ya ɗauka ya shafa a jikinsa yana gamawa ya fesa body spray,Ganin bayajin daɗi kuma babu inda zashi hasalima matar tasa sai gobe za'a kawota yasa ya ɗauki wata jallabiya mai sauƙin nauyi yasa baya jin zai iya zuwa masallaci dan haka ya shimfiɗa paryer mat ya data sallah. A can parlo kuma Ammi ce zaune ita da Papa suna ɗan tattaunawa a tsakaninsu,ɗan gyara zama Papa yay tare da faɗin"wai ina son ne i have been see him lpa dai"cikin muryar damuwa Ammi tace"tun bayan ɗaurin aurensa daya shigo ya shige ɗakinsa bai ƙara fituwa ba amma inajin there's a prblm am not sure dai bari na kirasa"ta faɗa tare da ɗaukan wayarta,jin alamin ana sauka daga steps ɗin bene yasa ta ɗaga nan sukai haɗa ido dashi ido ta zuba masa tana son ganin abinda ke damunsa dake Faisal bai iya riƙe damuwa a ransa ba nan take fuskarsa ta nuna damuwar da yake ciki. Ɗan murmushi yay tare da ƙarasawa wajan mahaifin nasa ya gaidashi,kallonsa Papa yay kafin yace"meke damunka?"..."no Papa i'm ok don't wurry" Faisal ya faɗa lokacin da yake kunna wayarsa,Murmushin jin daɗi iyayen nasa sukai kafin Papa ya miƙe tare da faɗin"follow me"yana faɗin hakan ya huce flat ɗinsa,Jiki a sanyaye ya miƙe tare da bin bayan mahaifin nasa. *Nasarawa* Lokaci kaɗan ya ƙarasu harabar babban gidan nasu yana zuwa ya samu wajan yay parking a parking space,cike da nutsuwa da kuma kamala haɗi da juriya da kuma kwarjini ya fitu daga cikin motar hannunsa ɗaukw da P.c ɗinsa wacce yake using da ita kai tsaye cikin gidan nasu ya nufa taɓe baki yay jin gidan shuru kamar babu mutane dan daman yasan Najma tafi kowa tsuru more than Lili,ambatar sunanta da yay cikin ransa yaji gabansa yay mugun faɗuwa,baisan mai yasa ta ɗauki gaba dashi har haka ba bai san mai yay mata da zafi haka ba shida yay amfani da kalaman data faɗa masa a matsayinsa na wanda ya lalata mata rayuwarta wanda ya rasa lokacin da hakan ya faru a duk lokacin daya takura kansa wajan yin tunanin gaskiyar abun amma ƙwaƙwalwarsa bata bashi damar hakan a lokacin kuma ji yake kansa kamar zai tarwatse,sautin waƙa yaji na ɗan tashi daga ɓangaren Lilin girgiza kansa kawai yay dan tabbas idan kaji Lili najin waƙa tana cikin matsanacin farin ciki ba ɗan kaɗan ba,Cike da taƙama yasa kai tare dayin hanyar flat ɗinsa dake ƙarshen gidan,yana zuwa yasa key ya buɗe ɗakin nasa wani ni'imataccen ƙamshine ya daki hancinsa ka sancewarsa bai bala'in son ƙamshi,shi yasa ya ƙara buɗe dugun hancinsa ya shiga shaƙa ya daɗe a wajan kafin ya ɗura ƙafarsa akan italian carpet ɗinsa nan take ƙafarsa ta shige cikin carpert ɗin,daman tun a hanya yay sallar magrib da yaji anayi ƙarasawa yay ya ajjiye p.c ɗinsa inda yake ajjiyeta tare da wayarsa ya shiga zare kayan jiinsa ya zubasu a wani ɓangare dake wadrope ɗinsa,Yana gamawa ya shige cikin bathroom kai tsaye wajan shower yaje ya sakarwa kansa ruwa kasancewar bai fiya son ruwan zafi ba,hannayensa duk biyun yasa ya dafe bango ruwan ya shiga dukan tsakiyar bayansa numfashi ya shiga fitarwa mai zafi jikinsa ya ɗauki rawa ba komai ya haddasa masa hakanba sai brain ɗinsa da take son wargatsa matsa lissafi a lokacin da baya buƙatar wani tunani duk yadda ƙwaƙwalwarsa ta keson sashi tunanin ya hanata faruwar hakan,a haka ya kammala wankan tare dayin brush ya ɗaura alwala jin amfara kiran sallar issha'i,wani light blue ɗin toiwel ya ɗaka ya ɗaura a waist ɗinsa kana ya fice daga toilet ɗin,gaban dressing mirrow ya ƙarasa tare da ɗaukan cump ya fara gyara kansa lokaci kaɗan kansa ya shige gyalli haɗi da fitar da wani sahihin ƙamshi sumar tayi luff har ƙasan wuyansa,wani versiline ya ɗauka ya shiga shafawa tattausar fatar jikinsa yana kammalawa ya ɗauki wani turarw oud ya fesa a jikinsa kana ya ɗauki wani abun baki mai fitar da ƙamshi strawberry ya shiga fesawa cikin baƙinsa ɗan lumshe tsumammun idonsa yay sbd daɗin da yaji yana ratsa shi,jikin sanyin jiki ya ƙarasa wajan wadrope ɗinsa ya ciro wata jallabiya fara tas ya zura a jallabiya ganin jam'i ya huce sa ya shimfiɗa dadduma ya data sallah mai cike da zallar nutsuwa. Lili Bayan ta gama wankan haɗi da shirya kanta ta sanya wata ƴar duguwar riga iya laps ɗin tare da saka wani 3guater hakan ya basa ɗan ma dai-dai cin hips ɗinta fituwa yay zamansa cikin ƴar rigar data saka,daga sama rigar tana da ɗan faɗi hakan ya bawa rigar damar zama a faffaɗan ƙirjinta gashin ƙanta ta tattara haɗi da ɗauresa da ribbon ya sauka tsakiyar bayanta a hankali take mutsa ƙaramin bakinta ta shiga rera waƙar wait for me,wayarta ta ɗauka tare da shiga wajan messages wata number ta shiga wacce aka rubuta Soulmate ta fara typing kamar haka. _i can't live without you, without you what's my worth,if i get separate from you than I will get separate from self (my world) because you are the only one i most love madly,you're the only one my eyes want see you, my ear want hear ur voice, i love you more and more most._ Tana gamawa ta tura masa fuskarta ɗauke da zallar farin ciki ta kusa samun muradin zuciyarta,wani black plate shoe ta ɗauka tare da zura cikin ƙafarta,a haka ta fice daga cikin ɗakinta babu ɗankwali tana ɗan tsallanta na ƙuruciya ta ƙarasa daining area don a nan ta kejin maganar mutanan gidan tana zuwa ta ƙara wajan Dad tayi masa sumba tare faɗin"barka da dare my lovely"kanta ya shafa tare da faɗin"yau mamana bakya son saka kallabi a kanki baki jin tsoron jinnu ko?"turo baki tayi gaba ba tare da tace komai ba ta nufi wajan Mamy tare da shigewa jikinta jinjina kai Mamy tayi kafin tace"our Mama ni ba za'a gaidani bako?"ɗan lumshe ido Lili tayi kafin ta ware manyan idanun nata akan Mamaynta tace"ayya Mamy nina isa kece fa rayuwarta"dry sukayi gaba ɗaya kafin Mamy ta ƙara cewa"to ɗagani mana mutum ya girma baisan ya girma ba haba"ɗan buga ƙafata tayi a ƙasa kana ta juya idanunta kasancewar bata son magana yasa taja bakinta tayi shuru,gefenta ta kallah taga Najama ta zabga tagumi ɗan zugurarta tayi tare dayi mata alama da idanu tace"lpa dai beb?"da idanu Najma ta bata amsa da "i'm ok"jinjina kai Lili tayi kafin tace"i'm gland" ƙamshin da taji yana dukan hancinta tun ɗazu yasa ta ɗaga manyan blue eyes ball ɗinta takai duba zuga kujerar dake farcing ɗinta,A hankali ta sauke ganinta a kansa yana zaune ya sadda kansa ƙasa yana latsa wayarsa sosai yay kyau cikin sky blue ɗin singlet ɗin daya saka tare da wando 3guater cikin sanyi murya tace"Boobi barka da hutawa"jice lips ɗinsa yay dan baiyi tunanin zatai masa magana ba haka kuma baya jin zai iya ɗago kai ya kalleta dan haka kawai ya jinjina mata kai,idan ka ganshi zaka ɗauka wayarsa yake dannawa amma garesa babu abinda yake sai santala-santalan fararen legs ɗinta ya zuba ido ta ƙasan daining babu abinda yake bashi mamaki a jikinsa sai yawan gargasar dake kwance jikin ƙafarta sunfi luff-luff abin sha'awa fatar ƙafar sai shaining take. Mamy ce ta ɗauki spoon haɗi da ɗebo fatan dan kalin turawan daya sha kayan lambu haɗi manyan kifi sai zabga ƙamshi yake,babu inda ta nufa sai bakin Lili wacce ta lafe jikinta tana jan numfashi alamar zatai bacci,cikin sauri Lili ta janye bakinta tare da shagwaɓe fuska kamar zatai kuka,Dariya Dad yay kafin yace"kinsan cewa Mamana ba tacin abinci da spoon saida hannu"Mamy ma dry tayi sannan ta ajjiye spoon ɗin tayi bisimillah tare da saka hannun cikin plate ɗin ta ɗebu abinci tare da kaiwa bakin Lili bisimillah Lili tayi sannan ta amshi abincin tana lumshe idanunta. Saida kowa ya gama cin abinci sannan Daddy ya gyara murya tare da kallon yaran nasa sauke idonsa yay akan Fahad da babu abinda ya taɓa sai coffee da Mamy tayi masa,Maida idonsa yay kai Lili sannan yace"Mamana nayi maki abinda kikeso kamar yadda kika nemi buƙata a wajana dole na cika maki ita,a zahiri kinji anyi aurenki da Faisal wannan a gsky al'amari ba dake aka ɗaura ba da ƴar uwarki Najma aka ɗaura Faisal aure"wani ihu Lili tayi tare hantsilawa ta faɗi ƙasa daga kan cinyar Mamy.. *_Nimcyluv ce😘_* *Wattpad@Nimcyluv* *Tue/Dec/2020 3:43pm* 08119237616 *JUYAYI* *E 6* _NIMCY SARAUTA😘_ .....A zaune Faisal ya samu mahaifin nasa da sallama ya shiga bedroon ɗin kasan cewar ya nayin sanyi ya suma,A gefen bed ɗin ya zauna tare da ɗura kansa a shoulder ɗin Papa,Sosai ya kejin faɗuwar gaba haɗi da bugawar zuciya wayarsa yaji tayi ƙara alamar Notification ya shiga yasa ya ɗan zame daga jikin Papa ya ɗauki wayarsa dake cikin aljihu gana shiga yaga alama new messge cikin sauri ya buɗe saƙon ganin sunan BEBY BOO na yawo,Wani ƙawataccen murmushi ya saki mai tsadar gaske karanta saƙonta dai² yake da wanke damuwar da tayi maƙale a zuciyarsa wani sanyi yaji na ratsa shi yayinda ya kejin a kashi ɗari na damuwarsa kasu wajan 90 sun tafi,Yafi 10min ya kallon specail luv messge ɗin da akayi masa kafin yaji saukar muryar Papa a kunansa "Faisal bani hankalinka nan" jin abinda Papa yace ne yasa ya ajjiye wayar hannunsa tare zubawa masa ido,A sanyaye Papa ya kalli ɗan nasa wanda yake alfahari dashi yana jinsa har jini da tsukar jikinsa baya son abinda zaizo ya juya masa lissafi dalilin hakan yake ta fargabar tayaya zai masa magana baya so ace sai ankawo masa yaga kamar anyi masa ba dai² ba,Numfashi Papa yaja kafin yace. "Faisal khalil Jibaɗo shine sunanka da kake alfahari dashi kuma kamar yadda kake alfhari da sunanka nasan haka kake jin dukkan wata maganata kuma nasan ina da ikon da zanyi maka zaɓan abu domin nayi imani da tarbiyar dana baka ba zaka taɓa watsamin ƙasa ka kunyatani jama'a ba,Nasan baka da burin daya huce Auren Lubna amma ka sani zanen ƙaddararka data Lubna ba ɗaya bace dalilin hakanma aka samu matsala wajan aurenku inda aka juya maka aurenka akan ƴar uwarta Najma,Ina son ka amshi ƴar mutane da amana kayi haƙuri ka samawa kan nutsuwa Har abada Lubna ba zata taɓa zama mata a wajanka ba ina fatan zaka amshi wannan auren hannu biyu". Wata zufa ce ta shiga zubuwa Faisal lokacin ɗaya jikinsa ya ɗauki rawa yayinda dukkan wani tunaninsa ya tsaya cak baya jin akwai wani abu mafi muni wanda yake ƙoƙarin sa zuciyarsa bugawa irin wannan,Tabbas banda mahaifinsa wanda ya haifeshi ne ya bashi wannan labarin da babu abinda zaisa yaƙi ƙaryata shi,ganin baya da wani abu da zaiyi a ɗakin Papan yasa ya miƙe a hankali ya nufi flat ɗin zuciyarsa fal tunanin abinda suka aikata shida Lilinsa ɗazu. Bin bayansa Papa yayi da ido yana mai tusayin Ɗan nasa wanda baya iya riƙe damuwarsa a cikin zuciyarsa,Glass ɗinsa ya mayar saman idonsa yaci gaba da duba Jaridar hannunsa yana yiwa yaron nasa addu'ar samun juriya a cikin zuciyarsa. Faisal na shiga flat ɗin nasa yasa key ya rufe ƙofar bedroom ɗin nasa duguwar Jallabiyar jikinsa ya zare darect wajan wata drower ya ƙarasa yana zuwa yasa hannu ya jawo drower tare da saka hannu ya ɗauki wani Tablet na Effective Relief from pain and fever kana ya ɗauki ruwa a glass cup yasa maganin tare da kafa bakinsa a saman ruwan ya shiga kwankwaɗa saida ya shanye sannan ya miƙe lokacin zufa ta gama wanke masa jiki,Banda harbawa babu abinda kansa keyi masa ya najin wani matsanancin ciwon kai wanda yake bara zanar tarwatsa tunaninsa na kamashi ga yadda mararsa keyi masa azaba haɗi da raɗaɗi tamkar zata fashe a haka ya sulale ya faɗa kan bed lokacin da ƙyar yake buɗe idonsa sbd tsabar damuwa da tunanin daya gama ratsa brain ɗinsa,Banda juyi babu abinda yake gaba ɗaya Papa yasa tunaninsa a JUYAYI ya shafe 30min kafin baccin ɓarawo ya samu nasarar ɗaukesa. Rano's family Jin maganar Dad take tamkar saukar ruwa'n sama da ba'a shirya masa gaba ɗaya tunaninta ya tsaya dan ba tayi tunanin Dad ya ɗauki maganarta da gaske ba harya zartar da hukunci akai kasa cewa komai tai sai numfashinta daya shiga ɗaukewa hakan ya nuna alamar ASMARTA nason tashi,Dama ace mafarkine ta keyi ba gasky ba dama ace idan ta farka zata ganta kusa da farin cikin ranta jin yadda zuciyarta ke beating ga yadda kanta ke juya yasa lokacin ɗaya ta fita a hayyacinta,Me zata cewa Dad ya fahimcita tunda ita da bakinta tace bata son Faisal a bawa Najma shin idan ta yiwa Dad tawaye ta kyauta masa kowa?,Maganar Dr Layler ce ta faɗu mata musamman inda take cewa "Ki zama mai tsaya akan ra'ayinki kada ki bari wani yazu ya shiga tsakaninki keda mijinki" Wasu hawaye ne suka shiga zuba daga cikin idonta yayinda ƙirjinta keyi mata zafi da kuma raɗaɗi babu abinda yafi zama da masoyi daɗi sannan babu abinda yafi rabuwa da wanda kakeso ɗaci tabbas tasan rabuwa Faisal tabkar rabuwa da numfashinta ne,Amma tasan Najma bata son Faisal ta fahimci akwai wanda ta keso tunda daɗewa dan haka zata nemi taimako wajan Yayarta Najma. Najma kam lumshe ido tayi lokacin da taji abinda Dad ɗin yake faɗa lokaci guda ciwon data keji acikin zuciyarta ya tafi,Wani silver mai daɗi ta haɗiye wanda ya huce da wani abu daya tukare mata maƙoshi wasu kyawawan hawaye ne suka zubu daga cikin idonta wanda bata san kona mene ba,Ɓangare guda kuma na zuciyarta tana ji kamar abune mai wahala taci Amanar ƴar uwarta ba zata ita zama da Faisal a matsayin miji ba kuma ba zata iya bijirewa umarnin mahaifinta ba,Mai ya kamata ace tayi yanzu lumshe ido tayi tana sauraran yadda zuciyanta suke mata shawara kala-kala,A hankali kyakkyawan idonsa ya fara yi mata yawo cikin idonta cure jikinta tare waje guda lokaci ɗaya tsigar jikinta ya mimmiƙe nan take ta farajin wani abu mai kama da feelings ƴar yamm haka taji a jikinta lokacin data tuna yadda tattausan lips ɗinsa ya shige cikin bakinta sosai ta lula duniyar tunani sama-sama taji maganar Dad nayi mata yawo cikin kunanta. "Nasan dukkanku bana da wani matsala daku ina neman alfarmar daku zama masu biyayya a dukkan umarnin dana shimfiɗa maku nasan ko bayan babu raina ba zaku taɓa dana sanin abinda na zaɓa maku ba,Mamana kece ƙarama dan haka nafi jin rayuwarki ta tsaya musamman yadda Ubangiji ya jarabceki da cuta mai wahalar gaske a kullum ina maki addu'ar samun sauƙi cikin rayuwarki,Najma ki shirya dukkan wasu kayanki zuwa gobe da yamma za'a miƙaki gidan mijinki Allah ya baki ikon yi masa biyayya kamar yadda Mamynki keyimin shi aure ɗan haƙuri ne sannan ki zama mai haƙuri da kuma kawar da kai" Mamyce takai dubanta ga Lili wacce take zaune zamar dirshen a ƙasan carpert ɗauke Mamy tayi domin tabbas Lili zata shiga damuwa dan ba ƙaramin so ta kewa Faisal ita kanta tasha mamakin wannan abun lokacin da Dad yake sanar da ita tayi shuru ne kawai dan bata da wani power abinda Dad ya yanke dashi ake aiki babu wanda yake masa musu,A hankali Mamy ta miƙa hannu ta ɗago Lili wacce take zaune ta sadda kanta ƙasa kamar mai tunani amma ita kaɗai tasan abinda ta keji a ranta,Lafewa tayi jikin Mamy tana sauke numfashi. Boobi kam duk yadda ka kai da karantar halayar mutum da wahala ka fahimci halinda yake ciki wayarsa kawai yake dannawa tym to tym yakan ɗan shafa kwantaccen sumar kansa tunda ya zauna ko mutsi bai yi ba haka babu abinda ya taɓa na abinci sai coffee ɗin daya sha shima da ƙyar yake iya haɗiya. Ganin lokaci yaja yasa Najma miƙewa a hankali ta yiwa iyayenta magana tare da shige flat ɗinta,A hankali ya ɗaga shanyayyun idanunsa wanda suke a lumshe kamar maijin bacci ya mannasu akan Dad dake duba wayarsa,Kujerar da yake kai yaja zuwa baya a hankali ya miƙe tare dayin wajan Dad yana zuwa yaɗan rungomesa ta baya tare dayi masa peak a ƙoshi a hankali ya ware laɓɓansa yace"sweet dream Dad" ya faɗa lokacin da yake lumshe idanunsa wanda suke ɗanyi masa zafi sbd baccin da baya samunyi akan lokaci,Murmushi Dad yay yace"and you too miskilin Dr"ƙara lumshe idanunsa yay tare da shafa tulin sumar kansa Mamy ce ta kallesa tare da faɗin"My Dr a taimakawa Mamy akai Lili ɗaki mana" fuska ya ɗan ya mutse tare da fiddo idanunsa dan baiyi tunanin abinda za tace ba kenan,Shuru yay baice komai ba tamkar baiji abinda tace ba,Dad ne ya ƙara cewa"Dr matata kakeson wahalarwa ko kasan Lili tayi girma fa ba kamar lokacin da kake ƙasar waje bane,Pls maza ɗauketa Mamy ta huta bansan kalar matar da zaka aura ba amma am sure Mamy zata fita kyau" jinjina kai kawai Boobi yayi yana tunanin ta yadda zai ɗauki miskilar yarinyar nan wajan Mamy ya nufa dan baya son su fahimci komai yana zuwa yay yaɗan durƙusa tare da saka tattausan hannunsa ya ɗauketa zuwa jikinsa,ƙara shige jikinsa tayi jinta samu sauyin waje ta shiga fitar da numfashi a hankali,Taɓe baki yay ganin yadda take shigewa jikinsa kamar mage tuno lokacin da suke vedio call yay always a kwance zai ganta ko kuma yaga ta rungome pillow idonta a lumshe sai tayi magana zai tabbatar idonta biyu amma sai suyi vedio na wajan 30min bata buɗe ido ba,A haka ya ƙara flat ɗin nata yana zuwa ya murɗa handle tare da tura kansa ciki wani daddɗan ƙamshine ya daki hancinsa ƙamshin daya daɗe baiji kamarsa ba,ya daɗe a tsaye yana shaƙar ƙamshin har baisan lokacin daya lumshe idanunsa ba,Wani ya nayine mai daɗi ya fara tsintar kansa a ciki ganin idan baiyi da gske ba bazai iya fita daga ɗakin ba yay saurin ƙarasawa wajan bed ɗin nata yana zuwa ya saketa daya tsaye ta faɗa saman bed yana jin lokacin data saki ƙara baiko juyawa ba yay ficewarsa tare da banko mata ƙofar ɗakin. Boobi yana fita babu inda ya tsaya sai ɗakinsa yana shiga ya zare siglet ɗin jikinsa nan ƙyaƙƙyawan gashin ƙirjinsa ya bayyana ya kwanta yay luf abinsa sai ƙyalli yake murɗaɗɗan jikinsa ya bayyama musamman Arms ɗinsa sosai Boobi yake da kyan jiki mai ɗaukan hankali komai nasa a nutse ya keyinsa baya son hayaniya da son magana daman Lili ce kawai yake jure magana da ita amma tunda wannan Juyayyen abin ya shiga tsakaninsu yaji kamar an ɗaure masa baki ko magana yake idan ya ganta zaija bakinsa yay shuru yayi kamar bai ganta ba,Sosai gabansa ke faɗuwa idan ya ganta yana dakewa ne a matsayinsa na namiji abune mai wahala ka gane damuwar Boobi yana da juriya da kuma haƙuri uwa uba miskilanci baya ɗaukan raini ko kaɗan yana da zuciya fiye da tunanin bai karatu sai dai yana da ɗauke zakai masa abu da yawa ya ɗauke bawai dan bai gani ba sai dan baka gabansa,Ganin tunanin da yake bazai ɗauke masa damuwarsa ba wayarsa ya kunna tare da saka ƙira'ar Sudais cikin suratul YAASIN saman bed ɗinsa ya haura tare da kashe glove ɗin ɗakin ya shige cikin blaget,Lumshe ido yay yana sauraran ƙira'ar dake fita daga cikin wayar tasa a hankali ya shiga bi cikin zuciyar sosai damuwarsa ke raguwa a haka bacci yay nasarar ɗaukesa. _Washe gari_ Misalin ƙarfe 7 na safe Lili ta shirya cikin shigarta ta alfmar wani blue ɗin boyal ne a jikinta anyi masa ɗinki buuba tayi rolling kanta da pink ɗin vail mai kyan gaske gashinta ya sauka har baya kasancewar vail ɗin ƙara mine hannunta ɗauke pink ɗin hand bag kai tsaye compund ɗin gidan ta nufa tana zuwa ta nufi wajan motar ta,Tana zuwa tasa key ta buɗe motar tare da shigewa cikin a hankali tayiwa motar key tare da danna horn mai gadi ya buɗe mata get ɗin ta harba motar ta kan titi sai B.U.K. Bata daɗe a hanya ba ta isa B.u.k lokacin har 8:20 tayi cikin nutsuwa tayi parking a parking space lokaci ta duba taga 8:30 ta kusa kuma shine lokacin ɗaukan darasin Faisal ɗan tsaki taja dan bata jin zata iya saka idonta cikin nasa ganin lokaci na shirin ƙurewa yasa ta buɗe motar tare da zuro da kyawawan ƙafafunta waje zuwa wani ɗan lokacin ta gama fituwa daga cikin motar,Lumshe ido tayi tare da cije jajayen laɓɓanta a hankali ta buɗe bakinta cikin siririyyar muryarta tace" Ya rabb" tana faɗin hakan taɗan ware manyan idanunta tare da juya da nufin ƙarasawa department ɗinsu, ta ɗaga ƙafa ɗaya biyu taji an damƙe hannunta tare da janta da ƙarfi jin hakan yasa ta buɗe baki zata kurma ihu taji an ɗura wani tafin hannu mai sanyi da kuma taushi an rufe mata baki tare da dannata cikin wata mota aka rufe motar,cikin sauri ya koma ɓan garen drever yana shiga yaja motar da wani irin spend yabar makarantar.. *_NIMCYLUV CE😘_* *am sorry for the late update kuyi haƙuri pls ina cikin busy ga kuma wani series film da zan fara rubutawa so kuyimin afuwa kuna raina kada kuyi fushi i knew ban kyauta ba sbd da yawancinku kunata zaman jira na so bana da laifi pls acpect my apologies 🙌🏻 I luv you more and more ku sani a addu'arku mai albarka pls* Masu wattpad pls follow and Comments with Vote ina ganin abinda kuke no Comments no Vote😉😉pls a sauya hali kafin *FAYAL* ta sauya ok *Idan anga typing errow suri hilis😅🙌🏻* *JUYAYI* *E 7* Wattpad@Nimcyluv 🥰🤣am so sorry 2days kun jini shuru it's all ur fault not my💁🏻‍♀️. ....Ihuu Lili ta fara a cikin motar tare da runtse manya-manyan dara-daran idanunta, tana mai jin tsoran buɗesu domin bata san dawa za taci karu ba,Ganin bashi da niyyar tsayawa yasa ta ƙara buɗe bakinta cikin fitar hayyaci ta fara kuka haɗi da kurma ihu,Tsaki ya shiga ja akai² jin kukan nata na damunsa ƙara gudun motar yay gaba ɗaya baya cikin hankalinsa da nutsuwarsa, sanadiyar hakan idanunsa suka sauya launi daga fari zuwa jaa jijiyar kansa tayi raɗa-raɗa sbd tsabar ciwon da kansa keyi masa,Wani wawan birki yaja cikin zafin nama haɗi da ɓacin rai yace. "Kee dallah nine shuru a nan kada ki fasan kunne". ai kamar ƙara mata gudun kukanta yay dan gaba ɗaya bata fahimtar abinda yake faɗa ganinsa take kamar ɗan yankan kai,Wani zazzafan numfashi ya shiga fesarwa ta hancinsa a hankali ya shiga girgiza kansa kamar mai tunanin tabbas abinda yaji yau da kuma abinda ya gani yay matuƙar tayar masa da hankali duk yadda yakai yayi tunanin a kan abinda ke shirin faruwa abin yaci tura,Cikin nutsuwa ya gangara motarsa gefen titi tare da kasheta a hankali ya buɗe side ɗinsa tare da zuro da kyawawan legs ɗinsa waje lokaci kaɗan ya bayyanar da gangar jikinsa,Lumshe gajiyayyun idanunsa yay haɗi da ɗan taune lips ɗinsa,A hankali yake buɗe hancinsa yana shaƙar daddaɗar iskar titi yayinda gefe guda na zuciyarsa yake karantu Sunayen Allah guda 99 a haka ya ɗan samu sauƙin zuciyarsa daga ciwon da take masa,A gaggauce ya buɗe side ɗin baya jin tana tari tare dajan numfashi da ƙyar yana buɗewa ya shiga ya zauna tare da rufe ƙofar ganin yadda take kokawa da numfashinta ya tabbatar masa da Asmarta ya tashi,Ɗan diriricewa yayi gaba ɗaya baison kallonta bare taɓa jikinta a sanyaye ya buɗe baki yace"Kee open ur eyes is me Boobi"ganin tana fisge² da kuma sandarewa ya sashi saurin kai haɗu ya ɗagota zuwa jikinta. Gyara zamansa yay ta hanyar miƙe ƙafafunsa a kan duguwar kujerar dake bayan motar kwantar da ita yayi yaɗan miƙar da ƙafafunta tabi jikinsa luff ta kwanta sai kokawa take da numfashinta dake ƙoƙarin barin gaggar jikinta,Lumshe fitinannun idanunsa haɗi da cije lipa ji yake kamar ana buga masa guduma a kansa sbd rabuwa da jikinta da yay jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa² ga yadda gargasar jikinsa suka mimmiƙe wani sanyi ya fara shiga ƙofofin jikinsa take yaji zazzaɓi na neman rufesa numfashi mai zafi ya shigar fesarwa ta cikin hancinsa. Cikin dauriya da kuma dakiya ya saka tattausan hannunsa mai sanyin gaske ya ɗura bisa ƙirjinta ya shiga danna mata a hankali tare da murza mata tsakiyar forehead,Tsananin azabar data jini yasa tayi wata iriyar zabura ganin hakan yay saurin mai data jikinsa tare da mannata a ƙirjinsa ya shiga tufa mata addu'oin da sukazu bakins dan gaba ɗaga brain ɗinsa ta tsaya da aiki shi kansa yana buƙatar taimako,Wani bottle water ya gani a gefen daya ajjiye jiya a cikin motarsa sbd ɗan sanyin dake busawa a gari yasa ruwan har yanzu da ɗan sanyinsa a hankali ya ɓalle murfin gorar ya kafa mata a ɗan ƙaramin bakinta cikin sa'a ruwan ya dinga shigewa cikin bakinta saida tasha mai yawa sannan ya cire bakin gorar daga cikin bakinta ya shiga shafa mata ruwan a oval face ɗinta zuwa wuyanta jin yadda,A hankali jikinta ya saki numfashinta ya shiga fita a hankali hakan ya tabbatar masa data samu relief daga pain ɗin data keji gane hakanne yasa shi ɗan zareta daga cikinsa tare da cillata gefe ƙara ta saki sbd kanta daya daki gefen murfin ƙofar motar,Cikin sauri ya buɗe murfin motar tare da ficewa ya koma side ɗin drever bai wani ɓata lokaci ba ya murzawa motar key tare da harbata kan titi ya nufi asibitin Aminu kano. B.u.k Fitar motar Boobi daga cikin makarantar keda wahala aka fara jin saukar Harbin bindigo ta ko'ina,Cikin tashin hankali da kuma firgici students da lectures ɗinsu suka fara neman hanyar tserar da rayuwarsu. Yana kishin giɗe akan luntsumemiyar kujerarsa wacce take office ɗinsa yana tunanin yadda zaiyi rayuwa da wata ba Lilinsa babban tashin hankalinsa da baisan asalin dalilin daya saka aka fasa aura masa ita ba shidai yasan har abada Lili ba zata taɓa cewa bata sonsa ba kuma ya ɗauki alƙawarin bazai taɓa haƙura da ita ba duk yadda zaiyi ya aureta sai yay no matter how,Ɗan tsaki yay tare da duba tym yaga wajan 8:25 mamakin yadda har yanzu bata ƙarasu makaranta ba yake,Miƙewa yay a hankali ya isa zuwa window'n dake manne a office ɗinsa ɗaga labulan window'n keda wahala yaji ƙara kamar daga sama kafin yayi wani tunanin yaji ƙarar bindigu tako ina kafin kuka da ihun students ya ƙara cika makarantar,Ƙara zuge labulan yay sbd wasu manyan mutane masu baƙaƙen kaya daya gani sunke waye wata ash ɗin mota sai harbi suke wajan 30min suna abu ɗaya kafin yaji ƙarar ta lafa cikin sauri ya buɗe ƙofar office ɗinsa ya fita,Gaba ɗaya makarantar tayi shuru baka jin ƙarar komai saita tsuntsayen da suma suka tsorata yana fita yaci ƙaro da lecture Bilal shima da fituwarsa kenan a tare suka jera tare da ƙarasawa wajan motar da akayi fata-fata da ita sbd ƙarfin da kuma yawan harbin da akai mata Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un kawai Faisal ke furtarwa da sauri² lokaci guda jikinsa ya ɗauki rawa zallar tashin hankali ya bayyana akan kyakkyawar fuskarsa ba komai ya tayar masa da hankali ba sai ganin duk irin harbin da akai ashe motar Lili'nsa ake harbi jikin ƙaraji da fitar hayyaci ya kwarara wani ihu tare da yin wajan motar da gudu yana faɗin "No pls my you are the only one i luv if you go i way i will day"ganin yadda motar ke fitar da wani yaƙi haɗi da ƙauri ne ya nuna gaf take da kamawa da wuta,Cikin sauri Bilal shida Abdull wanda ƙara suwarsa wajan kenan sukayi saurin riƙesa tare da janyesa da sauri nanfa yace sam baisan hakan ba suka shiga kukawa da ƙarshe ya samu nasarar kaiwa Abdul wani wawan naushi cikin sauri suka sakeshi da gudu ya juya ya nufi wajan motar yana zuwa motar na kamawa da wuta,Kuka ya fashe dashi tare da zubewa a wajan me hakan ke nufi sunkashe masa rayuwarsa kenan? Suwaye wa ɗannan ɗin waya turusu meta aikata a garesu har suka zaɓi kasheta? Rauninsa ne ya bayyana akan fuskarsa kamar ance ya juya yaga takalminta cikin sauri ya ɗauki takalmi lumshe ido yay nan wasu zafaffun hawaye suka sakko daga cikin idanunsa zuwa kan fuskarsa bazai taɓa manta lokacin dasu kaje shopping ta ɗauki takalmin sbd yace yay masa kyau,Hannunsa ya tura cikin aljihunsa ya ɗauko wayarsa numberta ya shiga kira tana ringing amma ba'a picking lamarin daya ƙara saka masa tsoro da kuma fargaba kenan,Cigaba yay da kira saida yay wajan five miss call kafin ayi nasarar ɗaga wayar muryarsa na rawa yace. "Hello hear beat where are you" iska mai zafi aka sakar sama ta cikin wayar kafin aja numfashi kamar ba'a son magana daga can ɓangaren aka ce. "She is with me"yana faɗin hakan ya datse kiran...Wata sassayyar ajjiyar zuciya Faisal ya sauke domin ya gane mai maganar wani sanyi yaji ya ratsa masa zuciyarsa,Amma maiya kawo motarta da kuma ta kalminta nan sannan mene ya haɗata da Fahad tunawa da yayi yayanta ne yasa ya share tunanin komai daga cikin zuciyarsa,Miƙewa yay ya nufi inda yay parking motarsa dan bazai iya jurewa rashin ganinta ba ji yake kamar yay hauka sbd rashin ganinta da baiyi ba kwana biyu yana zuwa ya faɗa cikin motar tare dayi mata key ya jata da wani spend yay waje yana fita motar ƴan sanda domin ardy sun samu labarin abinda ya faru. Asibiti. Lokacin daya isa asibitin 1:30 sbd ya tsaya wajan wani shop yayi shopping a hankali yay parking motarsa a parking space jin gina yay da kujerar motar tare da lumshe ƙanƙan tattun idanunsa da sukai jaa sbd tsananin tashin hankali da kuma far gaba duk yadda yasu yay tunani a kan tashin hankalin daya samesa yau amma abin ya gagara zuciyarsa taƙi bashi damar hakan eyes lashis ɗinsa ya ɗaga a hankali idanunsa ya bayya wani wahalallan numfashi ya fitar a hankali yasa hannu ya buɗe murfin motar ya sakko da ƙafafunsa zuwa ɗan wani lokaci gangar jikinsa ta bayya rufe motar yay kafin ya zaga ya buɗe side ɗin baya a shimfiɗe ya ganta sai fitar da numfashi take a hankali gaba ɗaya gashin kanta ya barbazu a kan fuskarta yana jin tsoron barinta cikin mota da babu shakka a cikin motar zai barta harya gama abinda yake,Ɗan juyawa yay yaga yadda mutane ke zirga² a harabar asibitinne yasa shi jan tsaki buɗe motar yay tare da sunkuyawa ya ɗaga kanta sannan ya nemi waje ya zauna,Ɗagota yay gaba ɗaya ya ɗurata bisa laps ɗinta gashin kanta ya tattara waje guda ya ɗaure da ribbon tsaki ya ƙara ja ganin ɗan ƙaramin vail ɗin data ɗauka a haka ya samu ya naɗa mata shi a saman gashin kanta,Juya da ita yay suna farcing juna hakan ya bawa full face ɗinta damar bayyana. Lumshe gajiyayyun idanunsa yay tare da taune lips ɗinsa sosai zazzafan numfashin da take fitarwa ta cikin bakinta yake dukan faffaɗan ƙirjinsa,Murfin motar ya tura tare da ficewa da ita a jikinsa fuska ya haɗe tamau sbd yadda mutane suke ta kallonsa motar ya rufe jikinsa ida da gadara haɗi izza ya fara takawa cike da kuzari yana jin yadda mutane ke gaidashi amma yay burus babu inda ya tsaya sai office ɗinsa,Yana shiga ya shifiɗeta akan duguwar sofa cikin sauri ya ɗaura mata drip tare da injection yana gamawa ya fice tare da rufe ƙofar. Marasa lafiyansa ya shiga dubawa bai samu kansa ba sai wajan 3:45 a gajiye ya turo ƙofar office ɗin a kanta idanunsa suka sauka tana kwance flat numfashinta na fita a hankali hannunta ya kallah yaga drip ya ƙare a hankali yasa hannu ya zare drip ɗin cikin sauri ya shige toilet ɗin office ɗin nasa. Dr Layler. Yadda take buga ƙofar kuma taji shuru shiya sata kanta cikin office ɗan murmushi tayi dan tunaninta yana jinta yay shuru sai taji saɓanin hakan sbd ƙarar shower da taji a toilet ya tabbatar mata wanka yake. Zama tayi a kan kujerar dake office ɗin mutsin da taji a gefenta ne ya sata juyawa cikin sauri ta miƙe tsaya tare da ƙarasawa inda take kwance ƙara mara sauti ta saki tare da dafe ƙirjinta tace "What Lili a office ɗin Dr na?" kafinta ƙara magana taji mutsin fituwarsa cikin sauri ta nufi wajansa bata da yadda murɗaɗɗiyar surar jikinsa ke ɗigar ruwa ba muryarta na rawa tace" Dr wacece wannan mene haɗinka da Lubna? Kallonta yay tare da ɗauke yana jin tambayarta tamkar rainin hankali banza yay mata ya nufi inda ya ajjiye rigarsa yana zuwa ya ɗauki farar singlet ɗinsa yana shirin saka rigar shaddarsa ta ƙara cillo masa wata tambayar "i'm asking you?" taɓe bai yay tare da lumshe idanunsa yana jin maganarta kamar tana watsa matsa wuta sbd yadda kansa keyi masa bala'in ciwo,Kamar baison magana ya wara saffan laɓɓansa yace" she is my biogical sister the same father and mother" cikin tashin hankali Dr Layler tazu wajan Boobi tare da dafe ƙirjinta tace "you mean Lubna is ur blood sister?" kallon sama da ƙasa yay mata kafin ya juya tare da faɗin "yerh that what i mean" yana faɗin hakan yasa hannu tare da matsar da ita daga gabansa. Takaici ne ya kama Dr Laylerh nan take zuciyarta ta fara harbawa,Babu abinda yake mata yawo cikin kunne sai maganganun da sukai ita da Lili daman wannan shine Boobi ɗin shine wanda ya aikata hakan ga ƙawarta ta,Wani kukan baƙin cikine ya kamata ta durƙushe a wajan ta shiga rera kuka,Tausayinta ne ya kamashi dan baison yaga mace tana kuka kuma yasan abinda yake mata baya kyautawa dawowa yay tare dasa hannu ya miƙar da ita tsaye fuska ya haɗe tamau kafin yace"Cry?.. I'm telling you the true kina son na miki ƙarya?"kasa cewa komai tayi sai jikinsa data faɗa ta shiga rera kuka tare da faɗin "Dan Allah Fahad ka soni wallahi zan iya mutuwa idan baka amince dani ba,Ka soni kwatankwacin yadda nake sonka pls kayimin rai ka samamin gurɓi a zuciyarka" zareta yay daga cikinsa tare dayin wani killer smile sandarewa Dr Laylerh tayi sbd wani mugun kyau da yay mata iya kacin rayuwarta bata taɓa ganinsa yana murmushi ba sai yau,Daf da ita ya tsaya tare dasa hannu ya kama tafin hannunta ya murza a hankali kana yace "bana da ra'ayin soyyaya Layerh da ace zanyi soyyaya babu shakka zan zaɓeki a matsayin mata a gareni amma soyayya shirmece da kuma ɓata lokaci ina maki addu'ar samun miji na gari idan kuma nina nagarin saiki ta add'uar samun nawa ina maki fatan alkairi a cikin rayuwarki nagode sosai da soyyayarki"yana faɗin hakan ya sumbaci tafin hannunta tare da juyawa ya nufi inda Lili take kwance hannunsa duka biyun yasa tare sukutarta yay waje abinsa hankali kwance tafiya yake cike da nutsuwa da kuma kuzari yana tafiya ne cike da jarumta sosai yake da kwarjini haɗi da haiba a idanun jama'a musamman ƴan mata. Yana zuwa wajan motarsa ya buɗe tare da kwantar da ita a gidan baya kana ya zauna mazaunin drever cikin sauri yaja motar tare da ficewa daga cikin asibitin. Dr Laylerh kam tunaninta ne ya tsaya cak yayinda tsoro da fargaba ya shiga ratsa zuciyarta,Hannunta daya sumbata shi kawai take kallon kafin ta ɗura hannun saman ƙirjinta tana jin wani daɗi na ratsata ta ɗauki alƙawari kuma taci alwashi indai tana da rai da lafiya babu abinda zai hanata samun muradin zuciyarta,Dole itace matarsa ta har abada babu wata ƴa mace data isa tayi mata shamaki dashi,da wannan tunanin ta fice daga office ɗin tare da rufe masa. Maidoguri road. Parking yay a compund na gidan tare da fituwa hankali kwance ya fitu daga cikin motar tare da shige cikin gidansu,Lokaci ya duba yaga 6:10 kai kawai ya jinjina kafin ya haura saman steps ɗin gidan ya nufi flat ɗin Dad ɗinsu. Da sallama ya shiga a zaune ya sameshi akan kujera yana shan coffee cikin sauri ya ƙarasa wajan Dad ɗin yana zuwa ya zauna kusansa tare da hugging ɗinsa cikin sakakkiyar fuskarsa yace "Barka da hutawa my luv" kansa Dad ya shafa yace "Yawwa Dr na yaya jikin sister ɗinka hope dai da sauƙi? Kai kawai ya jinjina wasu files masu yawa Dad ya ɗauka tare da tamƙawa Fahad ɗin dannan ya ɗauki wata farar takadda wacce akai rubutu a ciki ya tamƙa masa a hannunsa sannan ya dubesa yace "Fahad kayi haƙuri da dukkan abinda zaka gani cikin wanna taƙaddara kasani ƙaddara bata huce kan kowa ba nasu yi maka bayani tunda daɗewa amma ina tsoro,Baka da ƴan uwan da suka huce Lubna da Najwa..Najwa ba abar damuwa bace tunda yanzu da jima a gidan mijinta tun bayan fitarka aka kaita abin damuwa shine Lubna wacce kusan rabin rayuwarta yana wajena wanda a yanzu zai tamƙashi zuwa gareka Kaine babba sai Najma sai Lubna uwa ɗaya uba ɗaya haka kuke dan Allah ka kula da ita fiye da yadda zaka kula da cikinka ka dubi rashin lafiyarta ka bata farin ciki kuma kana da iƙon zaɓa mata mijin aure a duk sanda kasu..Jeka ubangiji yayi maka albarka Allah ya kareka daga sharrin mai sharri da kuma zargin mai zargi"Dad na faɗin hakan ya miƙe tare da fice daga parlon ya nufi bedroom ɗinsa. Jiki babu ƙwari haka Fahad ya ɗauki files ɗin da Dad ya bashi ya nufi hanyar flat ɗinsa,Yana zuwa ɗakinsa ya nemi wata baƙar Jaka ya zuba files ɗin a ciki tare da takaddar haɗi da wayarsa duk ya cillasu a ciki. Misalin ƙarfe 2:30 na daren ranar yana zaune a kan kujerar ɗakinsa yana danna lapton sanye yake da guwan wanda na amy colour ɗin shaddarsa daya saka ɗazu da yay wanka sai farar singlet,kamar daga sama ya farajin saukar ruwan bingidu a tsakiyar cikin gidan nasu,Hankali tashe ya ƙarasa bakin window'nsa ƙirji ya dafe haɗi da tushe bakinsa ganin wasu ƙartin mutane majiya ƙarfi suna haurawa saman flat ɗin su Daddy hannayensu ɗauke da manyan bindigu yana nan tsaye duk jikinsa rawa yake yaji saukar wata ƙarar bindiga wacce ta tafi da sautin ƙarar mutum wanda yana da tabbaci ta Daddynsa ce. Ganin bashi da wani lokaci yasa yay saurin ɗaukar baƙar Jakar daya zuba files ɗin da Dad ya bashi idanunsa taf da kwallar ganin yake kamar shine yay silar abinda ya faru tunda ya kasa tseratar da iyayen nasa,Cikin sauri ya ɗauki key ɗin motarsa a hankali ya haura ta window derect ya kaisa ya harabar gidan yana zuwa yaga motar cikin sauri ya buɗe motar tare da faɗawa cikin motar yay mata key ya fice da gudu shaf ya manta da batun wata Lili na cikin gidan. *_Nimcyluv ce😘_* *idan anga errow am sorry pls👌🏻🙌🏻* *NIMCYLUV MARUBUCIYA* _Assalamu Alaikum_ Hey Guys I hope all of you are fine?,So I want to thank you all for supporting me thank alot may Allah bless you all. I knew most of you are following my new book JUYAYI (the secret issue) right?. So I have a wonderful and amazing game for you guys but only wattpad readers can join the game. Madam if don't have wattpad appilication I want to say sorry for yourself because you miss it, it gonna be 💃🏻👯🏻‍♀️.. Understand? . I'm so sorry naƴi intertement ne GAME ɗin dai kashi biyu ke akwai WRITERS akwai READERS muda kanmu zamu zaɓi wanda za'ai Game ɗin dasu daga writer zuwa readers, dukkan maiso zai iya yin searching ɗina a Wattpad *Nimcyluv* sannan yayi following ɗina ta yadda idan akwai announcement zai gani cikin sauƙi. Kada kayi tunanin shira zamuyi da mutum idan hirana ne muna dasu kala². Akwai Coffee with heroine in english, wanda MaimunaAbdullahi ke gabatarwa da hausawanmu da kuma yare. @⁨+234 816 712 0325⁩ Sai kuma. Zauren MissMeemah on wattpad da ake gabatarwa iya hausa zallah @⁨Kitty😘⁩ . Ina fata zakuyi following ɗinsu, Game ɗina zaizo maku as happy new year idan kinsan baki da wattpad yana da kyau kije ki ɗauko a play store domin har gift zaki iya ci a wannan game ɗin. Ina buƙatar jin ra'ayinku ta hanyar yimin messages 08119237616 Writer or Reader duk kuna da damar bada gudunmawarku a wannan tafiyar🥰🤗. Nasan ba lallai ku fahimci wacce game bace amma indai za kuyi following ɗina zaku iya fahimta ngd sosai da kuka samu damar karanta saƙo na thank for dat. *Wattpad@Nimcyluv* *Sat/Dec/26 9:23pm* *💖JUYAYI💖* *E 8-9* Wattpad@Nimcyluv *Listen guys* you got to understand that some people don't come in your life to love you, They come into your life to see you, They don't come to bring to your life, They come to take from you. They don't see you as a person, They see as a opportunity, These are the type of people that don't love you for you, They love you for what they can take from you. They're not loyal to you, They're loyal to the benefits that Come with you, That's why they never show up. No matter how many times you showed up for them, That's why they never offer help, No matter how many times you helped them😫. No edit 🧐 ......Kasan cewar tsakiyar dare ne ga yadda gare yay shuru da kuma rashin abeban hawa a hanya yasa Fahad ƙara gudun motarsa kamar zai tashi sama,Babu abinda yake masu gizu cikin eyes ball ɗinsa sai fuskar Dad da Mamy iyayensa kuma abin alfaharinsa a koda yaushe wasu zafaffun hawayene suka shiga fita daga cikin narkakkun idanunsa wanda zuwa yanzu suka rikiɗe suka koma few red sabida tsananin tashin hankali da kuma firgici. Lokaci kaɗan ya fita hayyacinsa idanunsa har wani ruwa² suke sabida tsananin fargaba da kuma tension ɗin da yake tun karusa kuma ya faru. Gargasar jikinsa ne suka shiga mimmiƙewa ƙofufin jikinsa suka shiga amsar sayin dake kaɗawa a kan titin,Sannu a hankali raɗa² manya² jijiyoyin kansa suka shiga firfituwa a saman forehead ɗinsa lokaci kaɗan sukai raɗa² a kansa har wani halbawa suke sabida yadda kansa keyi masa matsanancin ciwo tare da bara zanar tarwatsewa gida biyu. ..Sanyin dake kaɗawa a kan titi shine ya ƙara bawa ƙofufin jikinsa damar buɗewa sosai,Lokacin kaɗan sanyin ya gaba ratsa jikinsa wani zazzafan zazzaɓi ya lulluɓesa dreving kawai yake ba tare daya san inda yake cilla kan motarsa ba. Zafin zazzaɓinne ya gama gauraye jikinsa ya shiga rawar sanyi tare da haɗe haƙuransa suna bada wani sauti Ƙas..ƙas..ƙas Ƙirjinsa ne ya bada sauti damm sabida gabansa daya faɗi kan motar yaɗan saki tare da kaucewa daga kan titi ya nutsa motar cikin wani ƙauye lokacin yay tafiya takai ta 3hours domin har amfara kiran farko na sallar asuba. Idanunsa ne suka rufe ruff sabida zafi da a zabar daya keji na ratsa tsakiyar kansa haɗi da gangar jikinsa,Ƙara gudun motar yay ya ƙara nutsa kan motar cikin ƙauye daf da zai huce wata unguwa motar ta tsaya cak alamar mai ya ƙare, Kan staring motar ya ɗura kansa ya shiga fitar da numfashi a kai². .Su Baba Habu da jikansa Mustapha da fituwarsa kenan daga ɗan ƙaramin gidansu zuwa masallaci suna tafe suna lazimi a haka suka ƙarasu gaban motar zasu gifta kenan Mustapha ya dawo da baya jin motar na fitar da wani tiririn zafi hakan ya tabbatar masa da ba'a daɗe da ajjiyeta a nan ba. Ganin Mustapha ya tsaya yasa Baba Habu dawowa da baya tare da tsayawa musan Mustapha yace "ji kana lahiya dai ka tsaya a nan bisa hanya?". Girgiza kai Mustapha yay tare da kunna wayar hannunsa yace " banjin lafiya bari na duba" yana faɗin hakan ya zagawa side ɗin drever tare da haskawa salatin ya fara ganin wani baturen mutum mai kyakkyawar sura daga shi sai singlet da dugwan wandonsa na amy colour ɗin shaddarsa yana fitar da numfashi sama². Baba Habu ya saki salati tare da riƙe haɓa yace "yau naga abinda ya dameni yanzu haka irin samarin burnin nanne masu kidnama😅 da kuma fyaɗe" A ɗan tsora ce Mustapha ya kalli Grandfather ɗin nasa yace. "Haba GF how many times that i talk do you ka daina faɗin haka wa jama'a wallahi matsalar ƙauye kenan akwai kuskuran fahimta" Daƙuwa yaywa Mustapha yace "Ƙaniyarka nace ƙaniyarka ja'irin kawai kaf ƙauyen nan babu wanda ya kai ubanka gidadanci,Kuma kai daga ganin wannan ƙuriyar fatar nan ba mutumin kirki bane". Girgiza kai kawai Mustapha yay dan yaga GF ɗin nasa he never understand,Ƙofar motar ya buɗe tare dasa hannu ya ɗago Fahad wanda yake cikin tsaka mai wuya saurin ɗauke hannunsa yay jin wani a zababban zafi ya daki hannunsa,Ƙoƙarin fitu dashi yay amma ya kasa hakan yasa ya kalli GF yace. "Pls GF i need ur help..taimaƙonka make mena wannan mutumin yana cikin wani hali" badan ransa yasu ba ya ƙara tare da taimakawa Jikan nasa ya fitu da Fahad daga cikin motar babu inda suka tsaya sai ɗan ƙaramin gidan da suka fitu daga ciki wata ƴat bukka suka ƙarasa dashi tare da shimfiɗesa a kan tabarmar Kaba. Ganin yadda yake haɗa teath da ƙarfi ga yadda jikinsa ke rawa alamar sosai zafin zazzaɓin ke shigarsa,Sunkuyawa Mustapha yay tare da sutale singlet ɗin jikin nan yalwataccen baƙin gashin jikinsa ya bai yana yay luff saman faffaɗan ƙirjinsa,Tashi ya ɗauki wani kwano ya siyayo ruwa mai sanyi a cikin Tulo ya shiga shafawa Fahad a saman ƙyaƙƙyawar fuskarsa da kuma naked body ɗinsa,Wata ajjiyar zuciya Fahad ya sauke mai ƙarfi. Arm robbers. Faɗin tuzarcin da kuma cin mutunci haɗi da rashin tausayi da kuma tsantsar rashin imanin da suka aikata a gidan Ahj Mustapha Rano,Bayan sun tabbatar da sun kashe kowa na gidan amma ba suga mutum 2 zuwa 3. Nan take ogansu ya ƙara basu umarnin dukkan inda suke su nemusu sabida muddin aka kashe iyayen ba'a kashe Ƴar ƴan ba to anyi a banza kamar an kashe macijine ba'a sare kan ba. Ƙofar farko ta shigowa cikin gidan ita suka nufa wanda wannan ɗakin ya zama shine mallakin Lili babu irin bugawar da sukai ba'a buɗe ba saima kamar sautin kuka da suke jiyowa daga cikin ɗakin,Ganin ƙofar ba zata buɗe ba yasa suka shiga zazzagawa ɗakin Petir suna gamawa suka cinna masa tare da juyawa suka nufi saman bene inda ɗakin Dad suna zuwa suka tarar da ogansu na shirin fituwa,Idansa ya sauke akan gawar Mamy da kuma Dad wacce suke kwance jini yana malala daga jikinsu,Yayinda Dad yake kwance flat idanunsa a sama fuskarsa ta faɗaɗa da murmushi yayinda Mamy kwance jikin Dad ta ɗura kanta bisa ƙirjinsa a haka rai yay halinsa suna manne da juna. Babu inda basu binka ba sabida dasu ganu inda dukiyar Ahj Mustapha Rano take amma babu ita babu labarinta,Ɗakin da yake ƙashe na gidan suka shiga wanda ɗakin ya zama mallakin Fahad ganin ɗakin tangameme ya haɗu iya haɗuwa yasa suka saki baki tare da bin ɗakin da kallo,Ogansu ne ya shiga dube² nan gaya ƙofar window a buɗe cikin sauri ya ƙarasa tare da leƙawa aikam abinda yake tunani ya gani ga sahun ƙafar mutum nan sabida danshin ruwan dake tafin ƙafar Fahad ya bayya a kan tarazu ɗin gidan. Banbo ya kaiwa naushin cike da ɓacin ganin yadda sukai gagarumin kuskure domin rasa Fahad dai² yake da rasa ransu a wajan Alhji,Wata dower suka buɗe nan sukayi arba da kuɗi masu yawa wanda a ƙallah za sufi dubu ɗari biyar nan kowa yasa hannu ya kwashi nasa rabon,ganin Asuba na shirin yasa suka gaggauta fita tare da yanke shawarar cinnawa gidan wuta sabida basa su subar wata shaida da zata nuna sune suka aikata hakan,Gaba ɗaya suka watsa gidan petir tare da cinna masa wuta cikin sauri suka shiga motarsu tare barin Estate ɗin gaba ɗaya. Maƙota kuka banda kuka babu abinda suke gashi babu damar fituwa kaima kayi silar naka ran amma dukkan Harbin da Arm robbers ɗin suke sunaji,Babu abinda ya ƙara ɗaga masu hankali sai wutar dasu kaga tanaci har saman gidajensu suna ganin hasken wutar,A dai² lokacinne aka fara kiran sallar asuba dalilin hakan yasa mutan unguwa suka firfituwa daga cikin gidajansu lokacin wutar ta gama cinye komai sai motocin da suke compound na gidan sune kawai wutar bata taɓa ba,Nan unguwa ta cika da kukan jama'a sabida kowa yasan waye Alhj Mustapha Rano mutum ne kowa mai son talakawansa da kuma son taimakasu cikin lamuransu kowa nasa ne ya ɗauki kuɗi masu yawa ya bawa mutum ba komai bane kana zaune zaice ya biya maka zuwa Hajji bana,Sosai akai baƙin ciki da rashin a dalin mutum kamarsa da ƙyar aka samu mutane suka shiga masallaci a kayi sallah tare dayi masa addu'a shida iyalansa kowa na faɗin "Allah sarki Najma ita tana da tsahun raine shiyasa tunda safe aka miƙata gidan mijinta wannan yarinyar Allah ne kaɗai yasan tashin hankalin da zata shiga" kowa dai da kwai abinda zaice a haka gari ya ɗanyi haske kafin wani lokacin unguwar ta cika da Ƴan jaridu da kuma manyan Ƴan sanda masu faɗa aji. Ganin babu wata jana'ida da za'ai sabida gama ɗaya gidan ya ƙone ƙurmus haryau da raguwar wuta naci kaɗan² yasa aka rufe gidan gaba ɗaya ta hanyar saka ƙata gwaɗo a gate ɗin gidan zuwa 7 na safe kowa dukkan wata media tasan da labarin mutuwar Alhji Mustapha shida iyalansa gidan T.V,Redio,Wasapp,Facebook,istagram, Da dai² sauransu Addu'a kam sun shata wajan mutane tare da addu'ar bayyana dukkan wanda ya aikata masu wannan ɗan yan aikin,Haka ƴan sanda suka gama bincikensu amma babu wata shaida da zata nuna ga wanda sukai wannan abun. Maidugori road. Tunda aka kaita da idanunta ba zata taɓa cewa taga Faisal ba, any tym tana flat ɗinta dake cikin makeken gidansu Faisal ɗin banda sallah da wanka babu abinda yake tayar da ita a haka har dare yay mata,Daren da yayi mata tsayin a cikin daren ranakun rayuwarta gaba ɗaya ta gasa bacci sai juyi take a tsakiyar bed ɗinta tym to tym gabanta na faɗuwa ƙirjinta na bada sauti tsoro da fargaba haɗi da kuma dana sanin abinda ta aikata ya gama ziyartar zuciyarta,Taci amana ƴar uwarta amana mafi muni tafi kowa sanin shaƙuwa da kuma soyayyar dake tsakaninta da Faisal tabbas idan labarin soyyayar Faisal da Lili zata bawa mutum tana iya yini da kwana bata kammala ba,Idan rubuta labatin zatai kowa zata iya rubuta Episode 50 a haka saidai ya tashi a season tabbas ta zama butulo kuma maci amana cin amanarma ta ƴar uwata ta jini ina zata kai wannan haƙƙin wanne hali Lubna zata faɗa ta sanadiyar hakan? Allah shine kaɗai ya sani domin abune mai wahala mutum ya ganu gaskiyar abinda ke zuciyar Lili duk da hausawa sunce bayanin zuciya a tambayi fuska to ita ko face ɗinta baya showing abinda yake ranta tana da zurfin ciki fiye da tunanin mutum da wahala mutum yay mata abu kaga ta nuna baƙin cikinta ko damuwarta kenan hakan yana nufin na haddasawa Lili baƙin ciki da kuma damuwa a ranta wanda bazai taɓa gogewa ba,Wasu zafaffan hawaye ne suka ƙara sauka daga cikin idanun a lokacin data tuna bawai Lili bace ta wargatsa aurenta sannan kuma ba ita bace ta jewa da Dad akan tana buƙatar a haɗa auren Faisal da kuma Najm ba,ƙara juyawa tayi a kan bed lokacin da komai ya fara dawowa cikin brain ɗinta haƙiƙa tayi wawta da kuma sakalci toshe bakinta tayi jin kuka na neman ƙwace bata,Mai yasa ta aikata hakan meyasa ta rusa rayuwar Lili cikin sauƙi haka tunawa da lokacin da Lili ta shiga ruɗu tayi a lokacin data fahimci kamar Boobi yay rapping ɗinta bata san cewa duk Najma itace sila ba🙀. Wanni ɓangare na zuciyarta kuma yana tuna mata zallar soyyayar data kewa Faisal a lokacin da idanunta suka fara ganinshi a lokacin ta fara ƙaunarsa a ranta ƙunar da bata taɓa yiwa wani ɗan adam ba face iyayenta,Sosai take mutuwar ƙauna da kuma son Faisal har tana jin zata iya komai domin ganin ta mallakesa ya zama nata ita ɗaya,Ta jima tana danne soyyayar Faisal da kuma muradin kasancewa dashi sabida ƙanwarta Lili ba tasu ta fallasa a sirin zuciyarta sabida Lili domin tasan koda zata rasa ranta zata iya haƙura da Faisal ta mallaka mata shi a matsayin masoyi shiyasa tabi komai cikin ruwan sanyi yau gata a ɗakin masoyinta Faisal kuma a matsayin matarsa amma saidai tana jin kamar ta aikata babban kuskure ganin idan bata cire tausayin Lili a ranta ba zaija mata itama ta rasa buri da muradin ranta yasa ta tattara komai ta ajjiye a gefe ya zauna Faisal babu wanda yake mata gizu cikin idanunta a haka bacci yay gaba da ita bacci mai cike da mafarkai mara kan gado. Misalin 7 na safe ta fitu daga flat ɗinta cikin shigarta ta alfarma sai baza ƙamshi take,Tafe take tana ɗan ƙifta ƙananun idanunta sabida yadda ta kejin gabanta na faɗuwa a haka ta ƙara flat Ammi domin gaidata,Tun daga nesa ta kejiyo kukan Ammi sama² cikin sauri ta ƙarasa shiga cikin parlour mutuwar tsaye tayi ganin Faisal yashe gaban Ammi ko motsi ba yayi gefe guda kuma family Doctor ɗinsu ne yake du basa,Ɗaya ɓangaren kuma Papa ne zaune akan sofa ya zabga uban tagumi yayinda idanunsa suka sauya kala daga fari suka koma jaa sabida tension ɗin da yake ciki haƙiƙa rashin Aminin nasa ba ƙaramin ɗaga masa hankali yay ba da kuma da gula masa lissafi yayi ba. A hankali ta ƙarasa shigowa ɗakin lokacin hawaye ya gama wanke mata fuska duk da bata san abinda yake faruwa ba,Ganin Najma a cikin parlour ga ƙara Ammi sautin kukanta domin ta tabbatar idan ta samu labarin mutuwar iyayen nata ba ƙaramin tashin hankali zata shiga ba ko kuma itama zuciyarta ta buga ayi mai gaba ɗaya dan haka suka yanke hukuncin ba zasu faɗa mata ba sai komai ya dai² ta. Zama tayi ƙasan carpert ɗin tare dasa hannu ta shafi sumar kansa a lokacinne wasu hawayen suka ƙara sakkowa daga cikin idanunta zuwa kan fuskarsa,Ammi ce ta goge nata hawayen tare da faɗin "ba kuka ya dace kiyi ba addu'a ita ya dace kiyi a dai² wannan lokacin ki sama ranki cewa akwai ƙaddararsa babu wanda zai ɗauki ƙaddarar wani ya ɗurama kansa,Dukkan abinda ya faru da mutum hakan a tsare yake wajan ubangiju so take it easy kiyi addu'a wa mijinki da kuma iyayenki da suka aura masa ke kiyi godiya garesu ki bisu da addu'arki mai albarka". Shuru Najma tayi tare da zurfafa bran ɗinta wajan yin tunani amma ta gagara tunanin komai zuciyarta da kuma ruhinta mijinta kawai suke fata gani a yanzu curewa waje guda tayi tana mai jin dama daga ita sai shine kawai a duniyar inama ace yanzu iyasu biyu ne babu su Ammi da babu abinda zaisa taƙi kwanciya cikin mijinta ɗumin tayi missed daddaɗan ƙamshinsa haɗi ɗumin jikinsa da kuma sweet saliva ɗinsa lumshe ido tayi ta ƙara cure waje guda tana jin kamar lokacinne yake sucking bakinta tare da zuba mata daddaɗan miyun bakisa mai garɗi da kuma zaƙi. Ƙauyen Yola. Tunda aka shimfiɗe Fahad bai farkaba har zuwa yanzun da ake kiran sallar magrib yana shirin kwana a kwance kuma cikin mawuyacin hali domin ɗagawar da ƙirjinsa keyine kawai zai tabbatar maka yana da rai. Duk wata kulawa daya dace a bashi ayi musamman mustapha shikam Babu Habu kira yake "ka gama kiwansa ya samu lafiya yazu yay kidnama ɗinka wallahi ko sisina bare kuma shanuwana ato,Mutane babu tsoran Allah a ransu musamman mutum mai ƙuriyar fata ka gani satsaɓar shan jinin mutuna har ƙure yake" Ai kamar ance Baba Habu ya Juya yana juya ya gansa tsaye akan ƙafafunsa ga yadda surar jikinsa ta bayya musamman muɗaɗɗiyar damtsen hannayensa ga yadda ƙirjinsa ya ƙara faɗi yawataccen gashin ƙirjinsa yay luff sai gyalli yake nipples ɗinsa sunyi tsini tare da yin red,Da gudu Baba Habu ya saki sandar hannunsa tare da kurma ihu haryana faɗuwa cikin sauri ya shige ƙaramar bukkarsa yana faɗin "Wayyo kayimin rai kidnma shanuwa biyar gareni🤣... *Nimcyluv ce😘* *NIMCYLUV MARUBUCIYA* _Assalamu Alaikum_ Hey Guys I hope all of you are fine?,So I want to thank you all for supporting me thank alot may Allah bless you all. I knew most of you are following my new book JUYAYI (the secret issue) right?. So I have a wonderful and amazing game for you guys but only wattpad readers can join the game. Madam if don't have wattpad appilication I want to say sorry for yourself because you miss it, it gonna be 💃🏻👯🏻‍♀️.. Understand? . I'm so sorry naƴi intertement ne GAME ɗin dai kashi biyu ke akwai WRITERS akwai READERS muda kanmu zamu zaɓi wanda za'ai Game ɗin dasu daga writer zuwa readers, dukkan maiso zai iya yin searching ɗina a Wattpad *Nimcyluv* sannan yayi following ɗina ta yadda idan akwai announcement zai gani cikin sauƙi. Kada kayi tunanin shira zamuyi da mutum idan hirana ne muna dasu kala². Akwai Coffee with heroine in english, wanda MaimunaAbdullahi ke gabatarwa da hausawanmu da kuma yare. @⁨+234 816 712 0325⁩ Sai kuma. Zauren MissMeemah on wattpad da ake gabatarwa iya hausa zallah @⁨Kitty😘⁩ . Ina fata zakuyi following ɗinsu, Game ɗina zaizo maku as happy new year idan kinsan baki da wattpad yana da kyau kije ki ɗauko a play store domin har gift zaki iya ci a wannan game ɗin. Ina buƙatar jin ra'ayinku ta hanyar yimin messages 08119237616 Writer or Reader duk kuna da damar bada gudunmawarku a wannan tafiyar🥰🤗. Nasan ba lallai ku fahimci wacce game bace amma indai za kuyi following ɗina zaku iya fahimta ngd sosai da kuka samu damar karanta saƙo na thank for dat. *Wattpad@Nimcyluv* *Sat/Dec/26 9:23pm* ```💖THE SICRET ISSUES``` 💖 *JYY* *10-11* Wattpad@Nimcyluv *Happy new year* Dear 2021 Be the best new year please, There's so many traggicc happen in. 2020 I hope that in coming 2021. No killings No viruy No War Spread peace and love, we hope that. 2021 will be the best year to come 🙌🏻. *Happy new year to all my Fans and Fam🤾🏻‍♀️* ......Fahad kam sam bai fahimci abinda Baba Habu yake faɗa saima ƙara zuba masa shanyayyun idanunsa yay zuciyarsa fal mamakin abinda ya kawoshi yay yasan kaf a tarihin rayuwarsa bai taɓa saman ƙauye ba,Musamman wannan ƙauyen daya fahimci zallar fulanine a cikinsa lumshe tsumammun idanunsa yay tare ds cije lips ɗinsa sosai kansa keyi masa bala'in ciwo ga kuma yadda zuciyarsa keyi masa zafi. A hankali komai daya faru iyayen masu sonsa da ƙaunarsa ya shiga dawowa cikin brain ɗinsa dama ƙwayar idanunsa,Babu abinda yake damunsa a rai wanda har yanzu yake masa sauti cikin dodon kunnan wato lokacin da ƙarar harbin bindigar ya tafi da ƙarar mahaifinsa wanda ya tabbatar zuwa yanzu ya rigasa gidan gsky. Me suke so?..waya turusu har suka nunawa iyayensa wannan zallar rashin imani da tsusayin,Hannu yasa ya shafi kwantaccen gashin ƙirjinsa wanda yay baƙi siɗik sai ƙyalli yake,A hankali ya ɗura hannun nasa a saitin zuciyarsa tare da murzawa jin yadda take buga masa kamar zata fito waje ji yake kamar yayta kurma ihu amma bazai iya ba sabida baison raunisa ya bayyana har haka,Yasan iyayensa a yanzu ba kuka suke buƙata ba addu'arsa kawai yake buƙata zuwa yanzu baya da burin daya huce ya gano wanda sukaiwa iyayensa haka. Jin an taɓa kafaɗarsa ne yasa ya buɗe gajiyayyun idanunsa tare da ɗurasu akan fuskar Mustapha ko kallan 2min baiyi masa yaja idnunsa ya kulle tare da ɗan jingina bayyansa da bukkar dake kusa dashi "I most go" shine kawai abinda ya faɗa cikin zuciyarsa,"Ga motarka can nasa an petir an zuba maka a ciki" maganar Mustapha kenan wacce ta ƙatse masa tunaninsa,Ware manyan idanunsa wanda wuka ƙanƙance a yanzu yay tare da mannasu a kan Mustapha'n ɗan lumshe ido yay tare da jinjina kansa alamar "Thank you" raɓawa yay ta gefensa tare da bin hanyar da yake tunanin itace wacce zata sa dashi da waje,Cike da kwarjini haɗi da haiba mutanan ƙauyen ke kallonsa musamman ƴan mantan da suke zaune a wata ƙasan bishiya ɗauke da ƙoƙwan nono a gabansa,Ƙara tamke fuska yay tamkar bai taɓa dariya ba koda yake ni kaina bana ce na taɓa ganin dariyar Fahad Mustapha Rano ba. A hankali yake tafiya tare da bada faɗi cikin isa da kuma gadara wacce ta riga ta zama jinin jikinsa a haka ya ƙarasa inda motarsa take ajjiye tsaf da ita sai ƙyalli take da alama tana shan wanki wajan Musty. Yana zuwa yasa hannu ya buɗe motar tare da shiga ya zauna a kan kujerar drever,Lumshe gajiyayyun idanunsa yay tare da fitar da wani huci mai zafi tunawa yay da files da kuma takaddar da Dad ya bashi ne yasa yay sauri juyawa ya kalli gefensa baƙar jakar ya gani ajjiye a gefen kujerar cikin sauri yasa hannu tare da ɗaukan jakar ya buɗe files ɗin ya ɗaukko ya shiga dubawa. Wasu zafaffun hawaye ne suka taru a cikin idanun ba tare da sun zubu ba,taune jajayen laɓɓansa yay yana jin wani zafi da kuma ciwo a cikin zuciyarsa sosai yake baƙin ciki da kuma takaicin rayuwarsa a kan idanunsa an kashe masa iyaye amma baya da ikon hana faruwar hakan,Sosai yay mamakin ganin files ɗin ashe duk ƙadarurin Dad ɗinne hatta A.T.M ɗinsa wajan guda 10 tare da Pin ɗinne kowanne a rubuce jikin wani files hatta Banks ɗinsa da suke ƙasar waje ko wanne da bayaninsa. Ajjiye files ɗin yay a gefe ya ɗauko takaddar daya basi guda biyu ne ashe ba ɗaya ba,Guda ɗaya ya fara ɗaukkowa yaga ansa. _From Mustapha to my lovely son Dr Fahad._ Wani wahalallan numfashi ya sauke tare da ƙara dafe saitin zuciyarsa wacce take ƙoƙarin fasa ƙirjinsa ta fitu,Ɗaya takaddar ya ɗauka tare da dubawa itama rubutu akai a jiki kamar haka. _From Mustapha Rano to Mamana i wish u all the best zanyi kewarki,Insha Allah ko bayan babu raina ba zaki kukan maraici ba kina da yaya wanda yake tamƙar uba a wajanki Mamana kina da gata gaba da baya Booby yana tare dake i love you._ Kansa ne ya buga da ƙarfi yayinda zuciyarsa ta shiga tunanin sunan da yaji an ambata na "Mamana" wace haka tunawa da itane taya jikinsa ya fara rawa jijiyoyin kansa suka shiga miƙewa idanunsa ya sauya kala har wani ruwa² yake sabida tension bakinsa na shaking yayinda teath ɗinsa suke haɗewa suna bada wani sauti ƙas...ƙas...ƙas cikin hawalalliyyar murya yace "Liliana.. She is not OK" ya Kai maganar muryarsa na creating. Yaya akai yabar gidan ba tare daya tuna tana ciki ba? Meya aikata yanzu yaci amanar da Dad ya bashi kenan jiyayi gaba ɗaya duniyar tayi masa girma gaba ɗaya yaji ya tsani rayuwarsa domin idan zai manta da ita tamkar zai manta da kansa ne ko kuma ya manta wasiyar Dad ɗinsa she is to yought she can't life without mentor "Where is she now?" itane tambayar da yaywa kansa ne cikin sauri ya buga kansa da jikin ƙofar motar lokacin daya tuna acikin gidan ya barta shida kansa ya kaita ɗaki ya kwantar saida ya tabbatar ya rufe mata ƙofar ɗakinta sannan ya huce ɗakinsa. Cikin sauri ya ɗauki wayarsa wacce take cikin jakar yay daining numberta abunda yaji yay matuƙar ɗaga masa hankali wajan 10 miss calls yay abu ɗaya ake gaya masa shine "a kashe take" notipications ne suke ta shiguwa wayarsa ganin haka ya shiga B.B.C news sbd yana buƙatar sanin wani abu. News farko shine wanda yafi ɗaga masa hankali ya sashi cikin shiga firgici wanda bai taɓa shiga irinsa ba,labarin mutuwar iyayensa da kuma wutar da aka sakawa gidansu yasa yaji zuciyarsa tayi irin bugawa wanda hasa yay saurin sa hannu ya danne zuciyarsa. Zai jure komai na rayuwarsa amma banda ita domin zannan ƙaddararsa haɗe yake da tata,Rashin kamar tsawar numfashinsa ne ko kuma tawaya a rayuwarsa,idan duk duniya za'ace ta mutu shikam bazai taɓa yarda da hakan ba, she's a life tabbas da bata numfashi da tuni numfashinsa ya daɗe da ɗaukewa. Buga ƙofar da a kaine ya dawo dashi hayyacinsa wani ajjiyar zuciya mai ƙarfi ya sauke tare da ɗaga rinannun idanunsa wanda suka gama yin jaa ya mannasu a kan Musty. Cikin daƙushasshiyar muryar mara sauti yace. "i have to go now". _Abuja private hospital_ A hankali yasa hannu tare da ɗura akan handle ɗin ƙofar ya murɗa ya shiga bakinsa ɗauke da sallama Momma wacce take zauna gefen bed ɗin marasa lafiyar ta amsa masa sallamar cikin muryarsa mai cike da jarumta. Kallonsa tayi ganin bashi da niyar magana yasa tace"Sufyan me Dr ɗin yace?" ɗago kai yayi ya kalleta cikin muryar damuwa yace"he have noting to say Momma kawai mu ɗauki wannan bawar Allah mu tafi da ita gida"...shuru tayi tana tunanin maganarsa sai kuma ta sauke numfashi tare da faɗin"you don't have any problm about this,Ina maganar her condition" zubuwa mara lafiyar ido yay wacce take kwance flat a kan bed ɗin marasa lafiya duk da bata da lafiya tayi kyau sosai kamar ka ɗauke ta ka gudu sabida matsifar yadda tayi kyau da kuma fresh. Dr ne ya shigo hannunsa ɗauke da wani file yana zuwa ya shiga dubata cikin farin ciki ya kalli Sufyan yace. "Any tym zata iya farkawa saika kula naga dukka ruɗe ko?". Murmushi kawai Sufyan yay dan bayajin zaiji daɗi da farin ciki indai ba gani yay ta farkaba. Momma ya kalle yace"you have to go back home saiki turomin da coffee danshi kawai na kejin zan iya sha". Dariya Momma tayi ganin yadda ɗan nata ya susuce akan yarinyar da bai gama sanin wacece ita ba,ita dai tana fata ace bata da aure domin wannan yarinyar abar so ce daka gani zatai haƙuri kuma akwai baiwa a tattare da ita. Miƙewa tayi tare da faɗin"Mijin ƴar tsuntuwa zan tafi gida ka kula da ita"shagwaɓe fuska yay tare hugging ɗinta yay mata peak a kumatu yace"bye Momma take care of ur self". "i will" shine amsar data bashi lokacin da take barin room ɗin,Sufyan juyawa yay tare da zama gefen bed ya kamata hannunta a karon farko ya riƙe cikin nasa wata ajjiyar zuciyar ya sauke a hankali sbd sanyi da taushin hannunta daya gama ratsashi,A hankali ya murza hannunta yace"lovely bbyn my hrt can't stop cry untill u open ur beautiful eyes,lovely bbyn tun lokacin dana ganki i'm madly love with u i knew u love me too u can't say now i knew dat"ya faɗa lokacin da yake sauke idanunsa a ƙirjinta ganin duk saman brest ɗinta ya fitu wajan ya zubawa idanu tare da cije lips ɗinsa shi kaɗai yasan halinda yake ciki sbd yafi kowa sanin waye shi da kuma halinsa haɗi da abinda gangar jikinsa ke buƙata,Lokaci kaɗan idanunsa sukai jaa tare da ƙanƙancewa sabida zallar fitina irinta Sufyan miƙewa yay a hankali tare da ƙarasawa saman kanta sunkuyawa yay tare da sakar mata lafiyayyan peak a forehead ɗinta tare da shafa cute pink lips ɗinta wanda suka haukatasa lokaci guda jiyaye indai ba tsotsesu yayba bazai taɓa jin daɗi ba ganin mood ɗinsa yana sauyawa yay saurin ficewa daga ɗakin ya nufi masjid domin gabatar da sallar magrib. _Maidoguri road._ A hankali ta raɓa gefen Faisal wanda ke kwance kan bed yana baccin wahala sabida ciwon da yaci ƙarfinsa,sabida zazzafan zazzaɓin dake jikinsa yasa aka zare masa ƴar farar singlet ɗin dake jikinsa daga shi sai ɗan ƙaramin boxer wanda ya kama jikinsa,Zare blaket ɗin dake rufe a jikinsa tayi ido da zuba masa tana jin wata wutar sonsa na ƙara ruruwa a cikin zuciyarta da dukkan wata gaɓa ta jikinta yayinda ta cire babu tunanin Lili da kuma tausayinta a ranta domin a kan mijinta zata iya komai hatta rayuwarta zata iya sadaukarwa. Zuwa yanzu babu mutumin data tsana kamar Lili ganin duk silarta ne mijinta ya shiga wannan halin da yake ciki na ciwo da ace tana da iƙon sadaukar da farin cikinta a kan nasa da tayi,Da ace zata iya haƙura dashi ta bawa Lili da tayi hakan amma rashinsa cikin rayuwarta tamkar rasa numfahinta ne da kuma cikar burinta. Ta ɗauki alƙawarin shida ganin Lili sai dai a mafarki badai a gaske ba amma muddin tana raye shida ita har abada kai har gaban abada ma idan akwai _(Fatima Ali Adam the you think Najma zata iya cimma burinta kowa🤔?)._ A hankali ta ɗura hannunsa saman ƙirjinsa ta shiga shafa sumar da tayi kwance a ƙirjinsa sannu a hankali ta kwanta a jikinsa tare da hugging ɗinsa kamar zata shige cikin jikinsa lips ɗinsa ta shiga shafawa tana jin wata wutar sha'awarsa na cinta kamar ta mutu idanunta sun jaa sun ƙanƙance sabida tsananin ciwon mara wacce ta ƙulle mata sabida wata zuma da Ammi ta bata tasha tayi ladamar shan zumar dan alokacin ji tayi kamar tai hauka babu wani abu da take buƙata a rayuwarta sama da Faisal domin shine kaɗai maganin damuwarta. Bakinta ta ɗura saman nasa ta shiga tura tongue ɗinta in his mouth wani shock taji ya shigeta sabida haɗuwar ɗumin bakinsa ya shiga wargtsa mata lissafi. Ganin ya datse bakinsa babu yadda za'ai ta iya kama nashi halshan yasa ta cafki lips ɗinsa na ƙasa ta shiga sucking,saukar bakinta cikin nashi ne yasa yaji ƙamar an watsa matsa wuta a zuciya sabida baƙin ciki babu wanda yaywa tana din hakan sai Lilinsa gashi yanzu bata raye kuma yay alƙawarin shima sai dai ya mutu a haka ba tare daya san mace ba. Yadda take shafa naked body ɗinsa ne yasa ya miƙe da sauri tare da mirginta ta faɗa saman bed ɗin yayinda shi kuma ya faɗa samanta yay mata rumfa🏃🏻‍♀️. _Ƙauyen Yola._ Cikin saurin Fahad ya gama shirinsa na barin gari sbd ya sami ticket a nan Yolan sosai yaywa su Baba Habu Alƙairi kafin yay wanka ya ɗauki kayan da Musty ya bashi ya saka alfarma ya nema a kan musty yazu ya rakashi airport babu musu ya amince aikam caraf Baba Habu yace"Ubangiji ya ƙaddarar saduwarmu Musɗapha nidai ko shanuwa ɗaya bazan bayar ba na gaya maka mutuminnan ɗan Kidnama ne kaƙi ka duba girman rigar nan kaf cikinta babu da kalar shuɗin mutum sai wannan mutumin Allah kai ɗai yasan kawonan mutunan daya ci ƙila ma ɗan damana🤣( wai ɗan daba)" . Shidai Fahad bai saurari maganar shirman tsuhun ba yay gama abinsa zuwa wajan motar,Ganin bashi da wani ƙauri yasa Musty ya zauna side ɗin drever tare da murzawa motar key da wani irin spend ya jata suka nufi airport. Suna zuwa ana ƙiran persinger da ɗan harama ya gama cike komai tare da damƙawa Musty key ɗin motar yace "yaje ya barmasa"sosai Musty yay gdy ya juya tare da barin harabar wajan. A gadarance ya shiga cikin airplane ɗin ya zauna a can side baya domin shine waje na musamman lumshe ido yay tare dasa hannu ya ɗaura jikin blet numfashi ya sauke tare da ƙara kulle idanunsa ya lulaa duniyar tunanin a dai² lokacin da jirginsu ya fara lulawa zuwa ƙasar Pakistan. _Abuja Private hospital_ Tun daga bakin ƙofa yake jiyo shassheƙar kukanta wanda baya fita sosai sabida muryarta data ƙoma very low,Cikin sauri ya ƙarasu bakin bed tare da zama kusanta ya riƙe hannunta tare da faɗin"Lovely bbyna wannan kukan yana hurtting zuciyana pls stop it"ganin da gaske kukan take yasa yay azamar mannata da ƙirjinsa ya shiga shafa gashin kanta tare da bubbuga bayanta bakinsa ya ɗura a kunnan ya shiga wura mata lafiyayyiyar iska tare da sakar mata sumba cikin kunnanta,Maƙale shi tayi ta shiga sauke ajjiyar zuciyar ita kanta tasan tana buƙatar rarrashi domin bata fata ta tuna abinda ya faru a daren shekaran jiya dare mafi muni a cikin daren data riska na rayuwarta bata komai yanzu bata da kowa sai wannan bawan Allah wanda take masa kallo irin na yayanta Booby sannan take masa na masoyinta abin alfharinta Faisal sannan take masa kallon HELPER. Dara-daran idanunta ta ɗaga tare da saukesu a full face ɗinsa ƙoƙarin cire jikinta take ya ƙara matseta bakinta ta shiga mutsawa tare da mamula a ƙoƙarinta nason furta wani abu amma ta kasa. Ganin yadda cute pink lips ɗinta ya jiƙe da silver ga yadda mamularsu yasa Sufyan fita daga mood ɗin cikin saurin ya manna bakinsa a kan nata. *Nimcyluv ce😘* ```Muje dai zuwa🤾🏻‍♀️naga ruwan comments gobe kuka posting aƙi comments na kwanta nayi bacci abuna🤣😘``` *1/1/2021 3:42pm* _The sicret issues_ *💖JUYAYI💖* *12-13* *WATTPAD..* https://my.w.tt/YwoNkzV5Icb or *Nimcyluv* *i'm not perfect.. but I'm perfect about what I'm doing 🤾🏻‍♀️* اللحمد لله رب العالمين *JUYAYI* ba readers ba koni da nake rubuta shi zan yabesa duk da kasancewar bashi kaɗai na rubuta ba amma ya zamutu garkuwa a gareni domin saƙon wata *Reader* dana amsa daga cikin saƙonnin masoyana kuma masoya littafina ya ƙara farkar dani da kuma ƙara bani ƙarfin yin rubutu a duk lokacin da buƙatar hakan ta tasu🤗👌🏻, bana zance labarin yaya ko bai yiba domin karɓarsa da readers sukai ya tabbatarmin da hakan domin labari da kuma tsaruwarshi shine yake saka ya yaɗu wa jama'a ma'abota karatun littafi. *Kira ga readers* ```Kuci gaba da antayomin Comments tare da share ɗinsa ya yaɗu media domin wanda basu karanta ba su nema su karanta👯🏻‍♀️sabida kada ayi babu ko salon labarin da kuma ma'anarsa nada banne🤾🏻‍♀️ ga dukkan mai so a yau na bashi dama yaymin magana private ان شاء لله zan tura masa``` No edit🧐 ......Yadda ya sakar mata nauyin jikinsa ne yasa ta shiga fitar da wani wahalallan numfashi,Idanunta ta rufe ruf sabida wani hurt feelings daya tasu mata amma tasan ku zata mutu ita da Faisal sai kallo domin ta fuskanci yay mata tsana mafi muni tsanar da bai taɓa yiwa kuwa irinta ba,Baƙin ciki dake da irin rayuwarta a yanzu domin zama da mijin da baya sonka babu abinda yake haddasawa a cikin zuciya sai zallar baƙin ciki. Da ace tana da iƙon cire soyayyar Faisal daga cikin zuciyarta babu shakka da tayi hakan amma Ubangiji ne ya ɗura mata wannan matsananciyar soyyeyar da ba tayi tunanin zatai irinta ba. Sai yanzu ta yarda cewa ba mutum ne ke faɗawa soyayya ba,Soyayyace ke faɗawa zuƙatan mutanan a duk lokacin da taga dama. Ta so Faisal a lokacin data fara ganinsa yazu wajan sister ɗinta,Ta shiga tashin fiye da tunanin dukkan mai tunani babu abinda ya ɗaga mata hankali ya kuma tsaya mata a rai saida ta fahimci da gaske Faisal sister Lubna zai aura ba itama. Lumshe idanunta tayi lokacin wasu zafaffun hawaye suka shiga sauka daga cikin idanunta,Lokaci guda tsanar Lila ta ƙara shiga cikin zuciyarta domin a ganinta sabida ita Faisal yaƙi accept ɗinta a matsayin matarsa,Tanaji a ranta ƙo zatai yawo tsirara I most separate them koda hakan zai zama shine abu mafi muni da zan aikata a rayuwa i'm ready to do anything indai akan Faisal ne zan iya bada abinda na mallaka indai zai zama nawa forever and ever. Baƙin cikin da yaywa Faisal yawa ne yasa ya kasa cewa komai saima sakar mata nauyinsa da yay,Wani yawo ya haɗiye mai ɗacin gaske sabida he lost his appetite. A yadda ya kejin zuciyarsa na bugawa ga wani baƙin ciki dake ziyartarsa yasa yay saurin ɗaga ta tare da hankaɗa ta..ta faɗa bayan bed tabbas idan yana ganinta a cikin zuciyarsa zai iya yi mata illah. "Lubna" zata iya sadaukar da komai nata sabida farin cikin ƴar uwarta amma ita son zuciya da kuma ruɗin shaiɗan yasa ta farauci abinda ƴar uwarta take da muradi haɗi da fatan kasancewa dashi kasancewarma irinta har abada ɗinan. Yana da yaƙini haɗi da tabbacin Lilinsa na raye a nan gidan duniyar bugawar zuciyarsa kaɗai ta zama shaida a wajansa,Hannu yasa ya dafe kansa tare da girgizawa kaɗan a kasalance yace "i'm always love you YES i'm crazy about you Lubana zanta jiranki untill the end of my life". Cikin saurin Najma dake bayansa ta ƙarasu wajanta tare da faɗawa jikinsa ta ƙanƙameshi ta saki wani kukan baƙin ciki bakinta na rawa tace. "Wlh baka isa ba danni aka hallieka ba Lili ba nice matarka ta har abada kuma kaida ganin Lili saida a mafarki wannan alƙawari na ɗauka zuciyata kuma dukkan abunda na faɗa saina tabbatar maka dashi dole ka zauna dani as ur wife". Cikin ɓacin rai yasa hannu ya wanketa da mari kafin ya nunata da yatsa tare da faɗin "Stay away for me how many times i told you i don luv u anymore,Zannan ƙaddararta yana haɗe da nata u need to understand dat" Kanta ta girgiza haɗe da tiƙe waist ɗinta tace"Nice ƙaddararka kuma zan tabbatar maka da hakan"tsaki yaja mai sauti haɗi da faɗin "Getout u datti girl"yana faɗin hakan ya shige cikin bathroom tare da sakarwa kansa shower wajan 10min ya ɗauka yana kammalawa ya fitu tare da shiryawa cikin cotton boyal mai ƙyan gaske key ɗin motarsa ya ɗauka tare da ficewa daga cikin gidan gaba ɗaya. Compound ya ƙarasa yana zuwa ya shiga cikin motarsa tare dayi mata key ya fita,A masjid ya tsaya tare da gabatar sallar magrib ya daɗe ƴana addu'ar ubangiji ya bayyana masa Lubna kafin ya bada sadakar kuɗi yace a ta yashi da addu'a. Tunda yabar masjid ɗin yake yawan neman Lili amm no more new information about Her. Najma. Tana fita tayi hanyar flat ɗin Ammi ciki da kissa da kuma munafurci ta ƙara wajan Ammin tare da share hawayen fuskarta ta rusuna har ƙasa ta gaida Ammin. Cikin kulawa Ammi tace"Najama lafiyanki ɗaya?" fashewa tayi da hadda sujan majina,Sosai hankalin Ammi ya tashi tana tsoron cin amanar marainiyar Allah cikin kaɗuwa tace"Kiyi shuru ki gayan damuwarki wannan kukan is no good for u". Tsagaitawa tayi da kukan ta shiga sauke ajjiyar zuciyar kamar wacce ta shekara tana kuka,ɗaga idon ta tayi tare da saukesu a kan Ammi cikin rawar muryar ta shiga faɗin "Ammi ina son Faisal amma zamana dashi baya da amfani kullum cikin baƙin ciki da kuka nake,Bansan maina aikata a garesa baya kulani baya cin abincin da nayi ko naje wajansa kurata yake,Ammi ki taimaka kisa Faisal ya sallamemin ban sani ba ko dole akai masa ya aure ni ina son Faisal Ammi amma bazan iya zama dashi yana nuna ƙyama a gareni kullum cikin tunani yake dan Allah Ammi ki taimaka". Takai ƙarshen maganar ta rushewa da wani irin kuka wanda cike yake da kissa da kuma kisisina irinta mata. Idan ran Ammi yay duba ya ɓaci nan take zallar damuwa ya bai yana a kan fuskarta cike da takaici yace. "Nina yafi Faisal kuma nai maki alƙwarin daga rana irinta yau kin daina fuskantar wani problms daga wajan Faisal zaki farin ciki da aurensa kuma dukkan abinda yay maki inaso kizu ki gayamin maza tashi kije ina nan zaizo ya sameni". Wata ajjiyar zuciya Najma ta sauke tare da ɓoye farin cikin dake ranta tace. "Allah ya ƙara girma Ammi nagode" tana faɗin hakan ta miƙe tare da komawa flat ɗinta...Tana zuwa ta daga tsalle tare dayin juyi ta shiga faɗin"ni banda damuwa in har zan buɗe ɗan idanuna na kalleka gaka daf dani tome zaya damu ƙalbina🤾🏻‍♀️💃🏻"haka tai tayi waƙa tare da juya ganin burinta ya cika cikin sauƙi babu wata wahala,Tayi imanin indai kissa da kuma kisisina haɗi da makirci yana ƙwatarwa mace ƴan cinta babu shakka dole Faisal ya zama nata ita ɗaya babu wata ƴar mace da zata samu damar ƙwace mata shi babu boka babu malam amma zata nuna masa zallar makirci irin nata. Da wannan tunanin ta shige bathroom cike da ɗokin ganin Faisal dan yau tasan bed ɗaya zasu kwana taji ɗumin jikinsa. 11:30 yay parking a parking space na gidansu idanunsa cike da bacci sabida gajiyar da yayi a haka yaci gaba da jefa ƙafunsa yana layi tamƙar ɗan ƙwaya,ganin parlon shuru babu mutane yasa kai tsaye ya nufi flat ɗinsa,Yana gaf da shigewa yaji saukar muryarta a bayansa kasa juyawa yay sai tsayawa yay cak ya fasa shiga bathroom ɗin nasa. Ganin ya tabbatarwa da Ammi yaji maganar kawai zunzurutun miskilanci yasa bazai amsata ba. Bata damu da hakan ba sai gyara tsaiwa da tayi cikin kakkausan Lafazi ta fara faɗin. "Idan harka yadda ni mahaifiyar kace kuma ka yarda ni nayi rainon cikinka na tsawon wata 9 da ƙwana 99 kuma na shayar da kai ruwa nonona na tsawon shekara 2 cif ban yarda ba kuma ban aminci ka ƙara kwana a wannan bathroom ɗinka ba ka koma flat ɗinka kaida matarka kuma duk ranar da Najma tayi kuka ta silarka wallahi wallahi wallahi kaji na rantse maka za kaga fushina wanda baka taɓa gani ba i will make my promise" Tana faɗin hakan ta juya cikin flat ɗinta cike da baƙin cikin abinda Faisal ɗin ya aikatawa marainiyar Allah. Zubewa yay a wajan ya shiga fesar da wani zazzafan numfashi kansa ya dafe wanda yake juya masa,baƙin ciki da kuma takaici Lafazin Ammin yasa shi fidda wata ƙwalla Lafazin Ammin dai² yake da rugujewar rayuwarsa haɗi da daƙushesar Muradin ransa. A nan ƙofar bedroom ɗinsa ya baje tare dayin flat ƙirjinsa ya shiga sama da ƙasa tayaya zai iya kwana da wannan emty head ɗin God forbid. Yana yin yadda ƙirjinsa keyi masa zafi tamkar ana rura wata ya sashi fara yin wani tari wanda ya keji kamar da numfashinsa yake fita ganin tarin yaci ƙarfin sane kuma bai son kuwa na gidan yaji yasa yay saurin saka hannunsa ya rufe baki jin wani abu mai ɗumi ne yasa yay saurin cire hannun nasa tashin hankali abinda ya gani yay matuƙar firgitashi jinin hannun nasa ya shiga bi da idanunsa jin tafiya a bayansa ya sashi saurin ɓoye hannunsa cikin aljihun wandonsa. _Folato city in pakistan_ Misalin 7:25 jirginsu ya sauka a filin tashi da jirgi dake Folato airport,Mutane da yawa ne suka shiga fituwa daga cikin jirgin cikin nutsuwa da kuma izza haɗi da gadara ya tsaya a bakin ƙofar jirgin tare da lumshe ido ya shiga shaƙar sanyi dake fita a wajan sabida weather su is very high taune lips ɗinsa yay yana jin wani mood nada ban na shigarsa ba wanda yake ciki ba,Tattausan hannunsa yasa a tulin sumar kansa tare da shafawa yaɗan hargitsa sai tayi kamar Daada numfashi ya fesar ta cikin bakinsa tare da buɗe mayatattun idanunsa wanda suka ƙanƙance sabida zallar damuwar da yake ciki wacce taƙi barin zuciyarsa yana jin zafi da kuma raɗaɗin rashin iyayen nasa musamman rashin ganin fata da kuma muradin zuciyarsa wacce ya keji baya da ita a kaf duniyarnan rashin ganinta dai² yake da wani daƙushewar farin ciki gani yake kamar dukkan abinda ya sameta shine sanadi ya manta da ita a lokacin da take neman taikonsa,Taimako kuma mafi muhimmanci a rayuwarta,Ina take? A wanne ya nayi take? Yaya jikinta da ciwonta? Wannan sune tambayoyin da suke ƙasan zuciyarsa wanda a kullum dasu yake kwana yake tashi amma yana hope a kan she's a live tana raye tana rayuwa kamar ko wanne mutum haka tana shaƙar numfashi wanda yake da tabbacin baya fita saida tunaninsa wanda ita kanta bata san da hakan ba. Cikin mutuwar jiki da kuma ƙonar rai yaja ƙafafunsa tare da jan trolly ɗinsa ya fara sauka daga steps ɗin benen ɗin jirgin. Tun daga nesa yake hango Fuwaz amma yay burus dashi kamar bai gansa ba,yanayin yadda yake tafiya rigarsa jikinsa na kaɗawa sabida tsabar rashin nauyinta da kuma tsananin sanyi dake kaɗawa saika rantse sanyi baya damunsa amma a zahirin gaskiya gani yake tamkar yafi kowa jin sanyi domin har laɓɓansa ne suke mannewa wajan guda yayinda tsigar jikinsa ke mimmiƙewa sabida sabuwar weather data samu kansa a sunkuye ya ƙarasa wajan motar Fauwaz. Da murmushi Fauwaz ya tari baban abokin nasa sabida ardy yasan da zuwansa tun jiya sabida sun daɗe suna magana dashi ta Email. Hugging ɗin juna sukai Fauwaz fuskarsa cike da farin cikin abokin nasa a haka suka ƙarasa mota suka nufi Folato Estat gidaje ne masu kyau da tsari wanda basu fiya tsayi da girma ba,a ƙalla za suyi gida wajan ashirin a jere ko wanne gida da number a jikinsa. Cikin nutsuwa Fauwaz yake murza kan motar har suka ƙarasu wani gidan mai number 5 get aka buɗe masa yay parking a ma dai² cin compuond ɗin gidan,A tare suka buɗe ƙofa suka fitu tare da jerawa suka shige cikin gidan Fahad gaba Fauwaz na biye dashi da trolly ɗin kayansa a wani ƙawataccen parlo suka zube tare da sauke numfashi. Surutu ya fara yiwa Fahad yayinda shi kuma yaja bakinsa yay shuru ya lulu duniyar tunanin wanda ya zabe masa nada ban da sauran tunanin da yake babu wacce ta faɗu masa a rai sai Dr Laylerh ganin duk wani tunani bazai ka masa ya tattara dukkan wata damuwarsa ya sata a gefe babu abinda yake tunani a yanzu sai yadda zai ya gano criminals ɗin da suka kashe masa iyayensa da kuma idan zai gano farin ciki da fata haɗi da muradin rai da kuma gangar jikinsa da wannan tunani wani nauyayyen bacci yay gaba dashi a kan duguwar sofa dake parlon. Gani hakan yasa Fauwaz ya miƙe tare da ɗaukan trolly ɗin Fahad ya shige da ita cikin wani ƙaramin bedroom mai kyau da tsari wanda yaji kayan italian. A gurguje ya fice daga cikin gidan yana fita ya nufi wani gida mai number 7 wanda yake jikin gidansu,mai gadi ya gani nan suka gaisa wayarsa ya ɗauka tare da kiran wata number ringing biyu aka ɗauka cikin sauri yace. "sweetie ina compund maza fitu ina sauri"yana faɗin hakan ya katse kiran tare da zubawa wata green ɗin flower ido some minute ta fito cikin wata pech ɗin abaya tari rolling kanta da vail ɗin a bayar murmushi fal fuskarta ta gaidashi tare da zuba masa ido cike da farin ciki. "I hava a guest a haɗa masa wani speacil dinner mana saiki kawo masa keda Afnerh". Daf dashi ta ƙarasu kamar zata shige jikinsa sai kuma taja baya tana tare da faɗin. "shikenan yau bana da tym ɗin shira farin cikin raina kenan ko" . Shagwaɓe mata fuska tare da tsuƙe bakinsa ya hura mata kiss iskar bakinsa ta daki fuskar saurin lumshe ido tayi tare da waresu da manna a kansa cikin sanyi murya tace. "I love u with all my heart i really love you my husband to be" murmushi yay mata tare da faɗin "I luv u too wify na"yana faɗin hakan ya juya tare dayi mata bye da hannunsa. Cike da soyyayarsa Fannerh ta shige cikin gidan nasu domin ta samu Afnerh su shirya dinner kamar yadda ya bata izini. Tun daga ƙofar parlo ike jiyo bige-bige da haɗi ƙaraji kamarna kumurcin zaki cikin sauri ya ƙarasa cikin parlon abinda ya gani yay masifar ɗaga masa hankali. Da gudu yay kan Fahad ganin yadda yake ta buga kansa da jikin bango jini sai zuba yake yayinda duka jikinsa yake rawa kamar ana kaɗa masa mazari saukar hannun da yaji ne yasa yay saurin juyowa cike da bacin rai ido rufe yasa hannu ya hanƙaɗa Fauwaz cikin rashin sa'a Fuwaz yaje ya daki jikin bango wata razananniyar ƙara ya saki tare da zubewa a wajan babu numfashi😱(jama'a Fahad yay kisan kai). _Abuja private hospital_ Saukar bakinsa cikin nata yasa ta zaro ido waje tare da mannasu akan kyakkyawar fuskarsa domin wannan shine karan farko da wani ɗa namiji taɓa kissing ɗin bakinta,kanta ta shiga girgizawa tare da ƙoƙarin zare jikinta daga nasa domin abinda yake matane dake ganinsa tamkar wani magic banda haka tayaya wani ƙato zai haɗa bakinsa da nata bayan tana da wanda ya fishi ta riga data sallama soyyayarta ga wani dan bata jin a ko wanne hali na rayuwa zata iya matawa da soyyayarsa gani take kamar taji amanar zuciyar data gama yarda da ita. Ɗumin bakinta yasa Sufyan firgita domin a iya tarin rayuwarsa bai taɓa jin wani kissing da yay masa daɗi fiye da tunaninsa ba sai yanzu,yayi kissing da mata da yawa amma wanda yay da Lili nada banne hakan yasa ya kejin wani hurt feelings a kanta cikin shauƙi ya ƙara tura tongue ɗinsa in side her mouth tare da cafke nata halshen yaci gaba da sucking tare da goga mata sajen fuskarsa a kan tata fuskarsa. Sosai abinda yake mata yake ƙara dagula mata lissafi amma babban abin mamakin bata ƙara yunƙurin tashi ba saima luff da tayi a jikinsa ta shiga sauke numfashi mai zafi amma ƙasan zuciyarta wani ƙunci da baƙin ciki ta keji tana jin tamƙar ta mutu ta huta da baƙin cikin rayuwa babu abinda keyi mata gizo cikin idanunta sai kyakkyar fuskarsa haɗi da sexcy eyes ɗinsa. Saurin buɗe idonta tayi cike da tsoro da kuma far gaba ganin a wannan karon ba fuskar data saba gani bace cikin idanunta ta bai yana cikin ruɗu da tashin hankali ta ƙara rufe idanunta domin tabbatarwa kanta abinda take gani. Wani ihu ta saki tare da ƙwace kanta cikin sauri ta shiga girgiza kanta tare da faɗin. "Why Booby how can that happen i lost him mutumin da baya raye ya mutu kamar yadda iyaye na suka mutu mai yasa zai dingayi mata gizo cikin eyes ball ɗinta". Ganin yadda jikinta yake rawa gaba ɗaya ta fita hayyacinta yasa Sufyan saurin tashi yana isa wajanta ya mannata da jikinsa tare da ƙanƙantar da murya yace. "Nine ko lovely bbyn"yana faɗin hakan ya sakar mata wani lafiyayyar sumba a dugun wuyanta. Sanyin laɓɓansa data ji a skin ɗinta yasa tayi saurin maƙalesa tare da tura kanta cikin ƙirjinsa. *_Nimcyluv ce😘_* Only ur comments i need👌🏻. Littafan Nimcyluv. Ƙaddarar mace. Ashe ƴar babata ce. Lamrat. Sai na aureta 200c Raino ne sila. Difference calture (izzar so)200. Jiddah(Heart beat) 👇🏻 The sicret issues *JUYAYI* Masu zuwa nan gaba 👇🏻👇🏻 *Uncle ne* (Age is just a number). *Kuyanga Zarina* (The new Emir). *Ƴar aikin gida* E.t.c _The sicret issues_ *💖JUYAYI💖* *14-15* *WATTPAD..* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb or Nimcyluv Accept your self the way you are be kind ur self 🥰🙇🏻‍♀️.. ......Sosai kukanta ke ƙara dagula masa lissafi a kwanta biyun da yay da ita wata muguwar soyyayarta ce ta gama shiga zuciyarsa babu abinda yake buri irin yaga ya kasance da ita,yana jin zuciyarsa na gaya masa cewa akwai ƙaddarori tare da ita amma babbar ƙaddarata shine kasancewa dashi yayinda shi bai damu da hakan ba shine dai kawai ta kasance mallakinsa Ƙara cusa kanta take sabida fargaba da kuma tsoro daya gama cikata babu abinda yake mata a cikin eyes ball ɗinta sai shi tunani ne fal a ƙasan zuciyarta amma brain ɗinta yaƙi bata damar yin tunanin da yake ranta da kuma zuciyanta, "Meyasa na kejin bugun zuciya idan na tunasa? Mai yasa tunaninsa ya fara addabar zuciyata? Hakan yana nufin yana raye ba kamar yadda mutune suke tunanin shima an kashesa?" wannan tambayoyin shine kwance a zuciyarta amma babu damar furtasu sabida babu mai bata amsar tambayarta. Ya nuna mata so ya fifita fiye da Najam ya danu da duk wata damuwa tata a lokacin da yake U.S mai yasa komai ya sauya a lokacin da take buƙatarsa mai yasa yay nisa da ita danta tabbatar yana yare domin wannan bugun zuciyar a kansa kawai ta keji ko Faisal bata bugun zuciya a kansa sai yayanta "Booby"..."why" no amswer shine abinda ɗaya zuciyarta ta bata amswer. Sufyan kam gaba ɗaya yanayin sane ya sauya gefe guda na zuciyarsa najin matsanancin wani irin firgitattan hurt feelings akanta sosai smooth skin ɗinta ke zautar dashi da kuma dagula masa lissafi,jin ƙirjinta na beating so past ne yasa a hankali ya shiga bubbuga bayanta tare da faɗin"shuru kinji lovely bbyn..nine ko ban iya jurewa ina sonki da yawa pls ki amince min i will give you anything u need". Mamaki ne yaci kata wai "SO?" kalmar da a bakin mutum ɗaya kawai take mata daɗin saurare shine kawai bata gajiya dajin dadaɗan kalamansa masu sanyaya mata zuciyata mutumin da har yau dake da hope a kansa kuma take jiran dawowarsa gareta,soyyayarsa ta riga ta zama jinin jikinta bata jin zatasu wani mutum bayansa koda ace bazai zama mallakinta ba. Kallonsa kawai take ko ƙiftawa babu cikin rawar muryarta mai daɗi da kuma sanyi tace. "Booby" shima kallonta yay jin sunan data ambata fuska yaɗan ɗaure tare faɗin "i did get u"girgiza kanta tayi tare da zare jikinta daga nasa a bakin bed ta zauna tare da lumshe dara-daran manyan idanunta wanda duk baƙin ciki da kuma shiga damuwa da wahala kiga sunyi jaa saidai su rage girma,Cije lips ɗinta tayi tare da murza ƴan yatsun hannayenta ganin idan ba tayi da gaske ba damuwa na iya tarwatsa mata zuciya da kuma saka rayuwarta cikin wani hali yasa a hankali ta shiga karanta sunayen Allah guda ɗari babu ɗaya. Nutsuwa taji ta fara saukar mata da kuma sanyi a cikin ranta a hankali taci gaba da karanta يا حي يا قيوم tare da انن لله وإنا إليه راجعون اللهم عجلن فل مسيمت و اكلين شيرن منه Sosai ta kejin tsuwa na ƙara shigarta haɗi da raguwar bugun zuciyar wasu taƙwayen ajjiyar zuciya ta shiga saukewa tare da cure jikinta lokaci guri guda. Kaɗaici data samu kanta a cikine da kuma rashin hayaniya ya sata lulawa duniyar wanda babu komai acikin sai baƙin ciki da kuma zallar damuwa. Jin ambaton sunnan Booby da yaji a kunnansa yasa Sufyan daskarewa a wajan tare da jin gina jikinsa da jikin bango "BOOBY" ya ƙara maimaitawa cikin ransa zuciyarsa yaji ta bada sauti damm domin jin sunan wani a bakinta ba shiba dai² yake da rushewar duk wani plan ɗinsa baƙin cikinsa ɗaya ace sunan data ambata na boyfrined ɗin tane babu shakkar bazai iya jurar hakan ba kuma dole ya gabatar da maganar neman aurenta wajan Alhji domin shine fata da kuma muradin ransa itace macen da tayi dai² da tsarin rayuwarsa. Ganin yadda ta cure waje guda ga kuma yadda jikinta ya saki yasa shi ƙarasawa wajan a nutse yana zuwa ya zauna kusanta tare da kiran sunanta cikin muryar dashi kansa baisan yana da ita ba sai yanzu. "Lovely bbyn"..ya ƙara mai²ta sunan a karo na biyu jin babu respond yashi saka hannu a hankali ya taɓa shoulder ɗinta baya yaga tayi zata faɗi yay saurin tareta ta faɗa jikinsa baki ya buɗe yana tunanin yadda bacci ya ɗauketa a ƴan minutes ɗinan. Gyara mata kwanciya yay a jikinsa tare da juyo da fuskarta garesa nan full face ɗinta ta baya,wani ajjiyar zuciya ya sauke wani irin magaɗisun hurt feelings ɗinta ne ke ratsa zuciyarsa da kuma gaggar jikinsa haɗuwar jikinsu waje guda tamƙar haɗuwar ruwan sanyi da kuma na zafine domin sosai yake samu realif a wajanta musamman idan ya shaƙi dadaɗan turaren da Momma ta fesa mata. A hankali ya saka hannu tare da ɗurashi akan innocent face ɗinta ya shiya shafa fuskarta ta zuwa dugun wuyanta mai ɗan ma dai²cin tsayi. Kasa contorl kansa yay har baisan lokacin da laɓɓansa suka sauka a gefen kunnanta ba wani lafiyayyiyar sumba ya sakar mata cikin daƙu shasshiyar muryarsa da kuma wani sauti wanda yay kala da sexual sound yace. "Lovely bbyn u are mine forever and ever kece tawa nima nine naki babu wani ɗa namiji dazai shigo rayuwarmu na rabu dashi never indai ina numfashi sai naga bayansa a komai ni winner ne bazan taɓa zama loser ba this is my promise i make my world true" yana faɗin hakan yay mata wani shegen kiss a gefen lips ɗinta mai tsayawa a zuciyar duk wata ƴar mace da akaiwa bare kuma su Lili da suke sabbin ƙinƙisa😂. Ƙarfe 6 na yammacin rana aka sallamesu zuwa gida babu ɓata lokaci suka shirya komai nasu tare da shigewa mota suka nufi unguwar G.R.A dake Abuja some minutes ya kasuwa unguwar mai cike da kyau da kuma tsari babu tarin jama'a ko yahaniya balle ya damu mutane hakan yaywa Lili daɗi domin sab bata buƙatar takura domin hakan na haddasa bata ciwon kai. Yanzu ma shuru tayi tare da lafewa jikin Momma tym to tym tana sauke ajjiyar zuciyar da ita kanta bata san ta mece saidai tasan ita ɗin ba wata aba bace a yanzu domin bata da wani gata da kuma mai tamaƙonta a yanzu sai HELPER ɗinta wanda take masa kallo kamar na yayanta "Booby" saidai shiɗin abinda yake mata yafi kama dana farin cikinta da kuma muradin ranta "Faisal" me hakan yake nufi? Shine abinda take ranta amma babu wanda zata tambaya. A haka motarsu tayi parking a lafiyayyen harabar gidan mai kyau da kuma tsari cikin ƙwarewa Sufyan yay parking a parking space tare da fituwa ya buɗewa Momma ƙofar side ɗinta fituwa tayi hannunta riƙe dana Lili wacce kanta yake sunkuye ko gidan bata tsaya gani ba hakan ya nuna masu gidan data tashi yafi wannan domin duk wanda bai taɓa ganin gida irin nasu ba dole idan yazu ya tsaya kalle²,da wani mayataccen kallo Sufyan ya bita dashi ganin yadda faffaɗan hips ɗinta ke motsawa jikin abayar da Momma ta saka mata ga yadda gashinta ya sakko ta ƙasan vail ɗin dake kanta,wani wahalallan miyau ya haɗiye tare da shafa ƙirjinsa yana jin wutar sonta na ƙara yawan cikin zuciyarsa. Da wannan tunanin suka kawo baban parlon gidan daga nanne kuma za kaga ƙofar shiga bedroom ɗin mamallaka gidan,da gudu su Yusrah suka ƙarasu wajan tare da kama hannun cike da murna take kallonta ganinta samu ƴar uwa dama ita ɗaya ce acikin gida domin yayan nata Sufyan bai fiya zama a gidan ba. "Yawwa Yusrah maza jeki da ita ki haɗa mata ruwan wanka ki bata kaya tasa tayi sallah saiku fitu kuyi dinner"cewar Momma ta faɗa tare da shigewa flat ɗinta Sufyan ba flat ɗinsa ya shige yana jin babu daɗi cikin ransa domin yasu a bashi ita su zauna a flat ɗinsa🤔amma yasan koyasha giyar wake babu mai yi masa haka abu guda zaisa ta zama mallakinsa idan igiyar aure ta shiga tsakaninsu cikin sauri ya shige flat ɗinsa don a yau yake son gabatar da maganar aurensa da Lovely bbynsa. Yusrah na shiga bedroom ɗinsu ta saki hannun Lili tare da shigewa bathroom ruwa mai zafi ta haɗa mata tare da fituwa ta kalli Lili tace "Sister maza shiga wanka" ita dai Lili da idanu kawai take kallon Yusrah domin babu abinda yake bata mamaki da ita sai zallar kirkinta komai nata a nutse saidai tana da surutu sosai wanda yake damun Lili domin har tsakiyar kanta ta kejin maganar Yusrah tana daurewa ne kawai. Cikin sanyin jiki ta shige toilet ɗin bakinta ɗaike da addu'ar shiga ban ɗaki "Allahummaa innii auzuu bika minaal kubuusi walkabaa isii"tana gaba faɗin hakan tasa ƙafarta ta hago tare da shige toilet ɗin. Kayan jikinta ta cire tare da tare da saƙalesu a hanger gaban tafkeken madubin dake banne a toilet ɗin ta tsaya tare da zuba ƙyaƙƙyawar surarta kallo ta cikin madubi sosai Allah yaywa Lubna tsari da halitta mai kyau komai nata speacial ne musamman yalwataccen gashin kanta wanda yake har baya sai kuma ƙyaƙƙywar innocent face ɗinta mai ɗauke da yalwatacciyar gira mai kyau gashin yay luf a saman idanunta sai kuma zara-zaran lashis ɗin idanunta wanda sukai mata ƙawanya saman idanunta. A hankali take kallon maya-mayan sexcy eyes ball ɗinta tare da dubawa ƙwayar idanunta kallo ganin kamar sun ƙara blue,turo baki tayi tare ƙwaɓe fuska ganin yadda saffan brest ɗinta suke tsaye curr tasu pink nipples ɗin sai sharning suke ita sam baya birgeta hasalima kunya ta keji sai taga kamar ita kaɗaice mai shi musamman ita da bata damu da saka brezia ba(kuskure kenan rashin saka brezia yana saka brest zubewa sannan kwanciya rufda cikima yana saka brest ya zube,kina budurwa mai jini a jiki brest ɗinki ya zube ya zama irin nazu gwaggo da ina masu shayarwar yara biyar ko bakwai aida matsala😱mata a farka domin akwai masu irin wannan halin ki sani wani namiji shine kawai ya birgesa a jikinki🥰hattara a tashi a gyara). Idanunta ne suka cicciko da hawaye ganin duk wannan baiwar da Allah yay mata ba zata taɓa zama mallakin sanyin idaniyarta ba,sosai ta keji zafi da kuma raɗaɗin rasashi amma idan ta tuna ya zama mallamin ƴar uwarta Najma ta kanji daɗi sa sanyi a ranta domin ita da Najma abu guda ne. Buga ƙofar da akene yasa ta dawo cikin nutsuwarta tare da zubawa ƙofar idanu ta shiga motsa ƙaramin bakinta a sonta na furta na wani abun amma ta gagara cewa komai sabida nauyin da laɓɓanta sukai mata. "Sister Momma na jira be past" jinjina kanta kawai tayi tamkar Yusrah na gabanta a kasa lance ta shige cikin Jakuzzie tare da sakin ajjiyar zuciyar zuciya sabida ɗumin ruwan daya ratsata. Sosai ruwan yay mata daɗi har wani bacci ne ya fara ɗaukanta ganin jiranta ake yasa tayi saurin yin wankan tare da yin brush ta gabatar da alwala. Wani long ash ɗin towel ta ɗauka tare da ɗaurawa a jikinta saida ta tsane sumar kanta tare da busar da ita sannan tasa hannu tare da fituwa daga toilet ɗin. Da kallo Yusrah take binta dashi tare da mamakin baiwar sumar da Allah yay mata musamman leg ɗinta da gashi yake kwance baƙi siɗik sai gyalli yake ko'ina yay luff dashi,cikin sauri ta gama shiryawa tare da gabatar da sallah wani ƙaton hijab ta saka harjan ƙasa yake tana gamawa Yusrah ta riƙe hannunta sukayi waje. Tun daga nesa ya zuba mata mayatattun idanunsa ko ƙiftawa ba yayi yana jin wani irin magaɗisu na ɗibansa a kanta lumshe idanu yay tare lashe laɓɓansa kamar wani maye. Kanta a sunkuye suka ƙarasu daining area ɗin duk da jikinta ya gama gaya mata kallonta yake amma saita basar tare da zama nesa dashi cikin baƙunta da kuma sanyin murya tace "barka da gida Momma da Alhaji" kamar yadda taji suna faɗa fuskarsa fal murna yake kallon Lili domin nutsuwarta ta gama yi masa yaji ta kwanta masa fatansa Allah yasa ta amincewa Sufyan kamar yadda yay masa bayani. "Yawwa ɗiyata yaya jiki?"ya faɗa tare da zuba masa idanu,ido ta lumshe tare da buɗewa kana ta cije bakinta tare da taunesu sai kuma wasu hawaye suka shiga fita daga idanunta ganin Alhajin ya tuna mata da Daddynta. Cikin sauri Sufyan ya miƙe tare dayin wajanta amma hararar da Momma ta watsa masa ya sashi sosa kai tare da shigewa flat ɗinsa domin bazai jure ganinta haka ba. Babu wanda ta ƙara cewa komai sai abincinsu kawai suke ci Lili babu abinda ta iya ci sai fruit salad ɗin da Momma ta haɗa mata,saida suka gama ci sannan Alhaji ya kalli Lili tare da faɗin. "Ɗiyata yayanki Sufyan yazumin da wata buƙata a kan yana neman alfarmar a bashi auranki ni kuma na amince da hakan domin yanzu matsayin uba nake a wajanki kuma keɗin amanace a wajanmu kuma zamanki haka bazai yiwuba tunda Sufyan yana sonki sosai kuma kema kina buƙatar mai kula dake a halin yanzu so I already make my decision to be his wife " a mugun kiɗime Lili ta ɗagu tare da zubawa Alhaji idanu yayinda wasu hawaye masu zafi suka ɓallemata tare da bin kan fuskarta,Kanta ta shiga girgizawa bakinta ya shiga rawa cikin suɓutar maki tace. *Gadai yau ɗinnan ko suwaye ya suyi na sara tsakanin SARAUTA PLACE da JUYAYI FANS💃🏻🎉🤾🏻‍♀️ ina zuba idon ganin Comments ɗinku* F@y@l _the sicret issues_ *💖JUYAYI💖* *16-17* Wattpad@Nimcyluv *PEOPLE* may destroy your image, stain your personality, but they can't take away your good deeds because no matter how they describe you, you will still be admired by those who really know you matter. *Dedicated to* Ummu aymana Alkairin Allah ya tabba gareki naga saƙonki ina gdy sosai Allah ya saka da firdausi🙌🏻thanks for the ƙauna Sarauta na maki sonso🥰😘. No edited🙇🏻‍♀️. ......"Na amince Alhaji" itace kalmar data faɗa lokacin da wasu siraran hawaye suka shiga zubu mata daga cikin idanunta,gefe na zuciyarta kuma tana yi mata wani irin ciwo haɗi da raɗaɗi da kuma baƙin cikin kalmar data faɗa wanda ita kanta bata san ta faɗe ta ba,Tayi hakanne sabida taimakonsu a gareni inaji suɗin alkairine tunda har suka amince da zamana a garesu rashin amincewa tamkar yankewar zamana a garesu. Bana da kowa bana da komai su nake gani a matsayin ahalina Momma matsayin Mamy yayinda Alhaji yake matsayin Dad,Yusrah matsayin Najma sai kuma babban jigo wanda tayi rashinsa a lokacin da komai ya ƙare mata tayi kukan rashinsa lokacin da take buƙatarsa yay mata nisa when all is gone ta rasa madafa bata da nutsuwa farin ciki yay ƙaura daga gareta ina zata ganshi domin ya taimaki rayuwarta. Har abada tunaninsa shine a ranta domin ta fahimci da jininsa take rayuwa duk wani bugun da zuciyarta za tayi haɗi da fitar numfashi basa fita saida tunaninsa sai yaushe ne zata ganshi? yaushe ne za taga garkuwarta? A kullum tambayar da take yawan yiwa kanta ne a ɗan lokacinnan amma babu amsa saidai tai ta tunani ita ɗaya wanda kuma tunanin a gareta bara zanane wa rayuwarta amma babu yadda zata iya tunanin shine abincita da kuma ruwanta haka kuma shine abokin hirarta rayuwa dashi ya zame mata dole. Faɗaɗa fuska Alhaji yay cike da farin ciki ya shiga sawa Lili albarka dan yasan she never rejecting his ambition ƙara bata haƙurin rashin iyayenta yay domin ta sanar masu komai ya kuma shaida masu aɗan ƙaramin lokaci za'ai bikin yana fita gobe sai sanarwa da Kawon Sufyan yana gama faɗin hakan ya miƙe tare da shigewa flat ɗinsa. Kifa kanta tayi saman daining ta shiga sauke ajjiyar zuciya rashin iyaye masifane haka mutuwar iyaye tuzarcine tana jin tausayin mara amma bata taɓa jin tausayin wani mara mai tsanani a zuciyarta ba saida ta rasa nata iyaye hausawa sunyi gsky da sukace duk wanda bai iya kuka ba iyayensa basu mutu ba,ta tabbatar yadda ta kejin damuwa da kuma hali na rashin lafiya da tuni Ahalinta sunyi rufdugu a kanta haka nan ba zata taɓa bacci ba sai a jikin wani nata,saukar muryar Momma da taji ita ta dawo da ita daga dugun tunanin data luula,kasa amsawa tayi sabida laɓɓanta da sukai mata nauyi a hankali ta ɗaga manyan idanunta tare da saukesu a kanta Momma ba tare data amsa kiran sunanta da tayi ba. Ganin hakan ya tabbatarwa Momma Lubna tana ɗaya daga cikin mutana nan wanda basa son surutu haɗi da takura musamman a wajan wanda basu sani ba kuka ta lura Lubna irin mutananne masu zurfi ciki da kuma riƙe damuwa da kuma haƙurin zama da mutane,ta fahimci ita ɗin irin mutananne masu rama alkairi da abun alkairi ta fahimci ta amince da auren Sufyan ne kawai sabida taimaƙonsu gareta bawai ta amince bane dan tana sonsa da kuma son zama dashi ba cikin tatausan Lafazi ga wanda ake son ayiwa magana ya kuma fahimci abinda ake faɗa masa Momma tace. "Soyayya abace mai wahala gaske amma idan kayi dace da masoyi na gaskiya mai yarda da kuma amana haɗi da ɗauke kai babu shakka kayi dace da masoyin gaskiya Lubna,akwai ƙaddarorin cikin Soyayya haka kuma akwai alkairai masoyin da zai ɗauki damuwarki ya maidata tashi shine masoyi haka kuma Masoyin da zai baki farin ciki fiye da yadda zaki bashi wannan shine "ƘAUNA" kada ka taɓa zama da Masoyi domin kancewarsa mai kyau ko mai Arziƙi ko kuma Dangi aa ka zauna da mutum a kan ka amince sabida kana sonsa da ƙaunar sabida Allah ba dan wani abuda yake dashi ba,Soyayya nada daɗi musamman ka samu wanda zuciyarka ta amince dashi amma wasu nayi mata wani kallo a kan a bace mai tarwatsa zuciyoyin mutane tabbas Soyyaya nasa mutum yaji inama baizo duniyar ba dalilin yaudararsu da a kai amma abun fahimtar dukkan saurayin daya rabu da mace Ubangiji ya ƙaddara hakan فمن قددر الله حقا قدره ita ƙaddara ta riƙa fata daman shiɗin ba alkairi bane garesu domin ace Matar mutum kabarinsa,duk daɗewar mace a gidansu da kuma yawan shekarunta batai aure ba wannan ba abinda za'a ɗaga hankali bane domin ubangiji ne bai bata mijin auren ba kuma lokacinta ne baiyi ba domin kafin a haifi mace an haifi mijin aureta..."Numfashi Momma taja tare da zubawa Lubna ido ganin tana fahimtar abinda take faɗa mata tana fahimta Thank God domin duk hankalin Lubna na kanta,numfasawa Momma tayi tare da faɗin. "Wannan fitila na baki keda kanki zaki haska zuciyarki domin tabbatarwa kanki wanda kikeso kuma kike muradi abu ɗaya na sani Sufyan na sonki"tana faɗin hakan ta miƙe tare dayiwa Lili alamar "Goodnight" da hannu wata sassanyar ajjiyar zuciya Lili ta sauke mai ƙarfi tare da lumshe luntsuma-luntsuman idanunta haɗe da taune cute peach lips ɗinta jiki babu ƙwari ta miƙe tare dayin bedroom ɗin Yusrah tana zuwa ta cire zumbulelen hijabin dake jikinta wanda duk ya dameta daman ta sashi ne sabida Sufyan toilet ta shiga tare da ɗaura alwala haɗi dayin brush kana ta fitu tare addu'ar bacci ta shafe jikinta kana ta haye bed ɗin tare da shigewa jikin yusrah ta shiga sauke ajjiyar zuciya duk yadda tasu tayi tunani a kan maganganun Momma amma ta gagara blanket taja masu tare da ƙara shigewa jikin Yusrah domin tana bala'in son ta jita jikin wani few minutes bacci yay gaba da ita. Wasa-wa yau satin Lubna biyu a gidansu Sufyan sosai suke bata kulawa har yaza mana ta manta da wasu abubuwan da suke faru da ita shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakaninta da Yusrah wacce ta kewa kallon Najma komai tare suke abu na farko da zai baka mamaki yadda soyayya mai ƙarfin gaske haɗi da shaƙuwa ta shiga tsakaninta da Sufyan saida ta nuna masa ɓacin rai sosai kafin ya daina taɓa jikinta amma idan ya ganta ji yake kamar yay hauka shiyawa bai damu da zaman gidan ba,yafi zama a office ɗinsa yayinda ya tilastawa Alhaji ya dawo da maganar aurensu kusa cikin sa'a aka mai dashi sati biyu kacal. Hakan yaywa Lili daɗi domin ta gaji da halinda Sufyan ɗin ke nuna mata dan har wasan ɓoye yake wani lokacinma saiya kaiwa Momma ƙararta sannan take fituwa suyi hira amma tunanin ɗan uwanta kuma yayanta yana nan maƙale a ranta musamman yanzu da take yawan mafarkinsa wanda ya zame mata al'ada. **** **** Zafin bugun da Fahad yay masa ya sashi ɗaukewar numfashi na wasu sakanni hannu yasa a saman kansa jin laima nabin gefen fuskarsa ɗan waro ido yay cike da tsoro ganin jini kwance a jikin hannunsa. Yadda yake fitar da wani numfashi mai ƙarfi tare da hurga da dukkan abinda yay karo dashi yasa Fauwaz saurin miƙewa tare dayin wajansa a karo na biyu. Yana zuwa yaɗan ja da baya tare da zubawa Fahad ido sosai yake jin tausayin abokin nasa musamman idan ya tuna bashi da kuwa komai ya ƙare masa,babban abinda yake damunsa ganin har yau bai yarda Lubna ta rasu ba ƙaddara tazu when all is gone,baya da farin ciki,walwala,ƙwanciyar hankali,bashi da komai sai yau tunani gashi murɗaɗɗan mutum wanda sam bai damu da kuwa ba kamar yadda bai damu da asan abinda ke ƙwance cikin zuciyarsa ba,shi ɗin mutunne mai zurfin ciki da wahala ka gane abinda ke damunsa bare kuma face ɗinsa yay showing abinda yake ɓoyewa a zuciyarsa ba. A sanyaye Fauwaz ya ƙira sunan Fahad tare da faɗin "how long zaka kasance a cikin damuwa?damuwa bata kamace ka ba a wannan lokacin ya kamata kana maida damuwar zuga Allah ubangiji maɗaukakin sarki shine ke ɗurawa bawa lalura kuma shine ke yayewa,maimakon ka samu sauƙi a ranka saika ƙara samun damuwa cikin ranka,kai musulmi me yana da kyau ka ɗauki ƙaddararka mai kyau ko mara kyau kasan cewa ƙaddara abace mara tabbas,tabbas ƙaddara lokacine bawai kullum mutum ke kasancewa a cikin taɓa akwai lokacin da zaizo sai kaga kamar ba'ai ba,Fahad imaninka bazai taɓa cika ba saika yarda da ƙaddara kaci gaba da haƙuri da kuma addu'a sai kaga ka fita daga cikin JUYAYIN da kake ciki amma ni kaina wannan sicret issues ɗin yana juya tunani kayi dan Allah tun kafin a haifi mutum an riga da an rubuta ƙaddararsa a jikin allon Lauhil Mahafuz allon da babu wanda ya isa ya goge abinda yake jiinsa". Ajjiyar zuciyar Fahad ya shiga saukewa tare da fesar da wani zazzafan numfashi daga cikin bakinsa,sosai yake ladamar kasancewarsa a raye mai yasa bai tsaya sun haɗa dashi sun kashe ba? Mai yasa Dad ya bashi amanar Lubna?mai yasa Dad ya haɗa dukkan wasu ƙaddarorinsa ya bashi?mai yasa bai duba taƙaddar da Dad ya bashi ba?mai ya kawoshi pakistan mai makon ya juya zuwa mahaifarsa kano?shin da gaske Lubna bata raye? Shin ƴan fashin da suka kashe masa iyaye sun manta cewa sunbar iri wanda zai iya zama shuka harya yaɗu yay furanni tare da zuba ƴar ƴar?mai yasa ya manta ta ƙaddarar da Dad ya bashi ba tare daya duba ba". All this daya faru ƙaddara ne wacce tana iya faɗawa kan kuwa kuma idan ubangiji ya jarabceka da ƙaddara yay hakanne dan gwana imaninka bawai dan baya sonka ba. Lumshe idanunsa yay wanda suka gama sauya kala daga fari zuwa jaa wanda har wani ruwa² suke sabida tsananin damuwar da yake ciki,tabbas idan har yana son cimma burinsa da kuma muradin ransa tare da ɗaukar fansa dole ne ya aro jarumta tare da ƙarfin guiwwa ya sama ransa,a karo na barkatai ya ƙara sakin ajjiyar zuciya tare dasa hannu ya dafe saitin zuciyarsa wacce keyi masa matsanancin bugu a hankali ya suma girgiza kansa wanda yake masa ciwo domin duba ɗaya zakai masa kasan cewa kawai dauriya yake musamman idai mutum ya kalli yadda jijiyoyin kansa suka firfitu tare dayin raɗa² saman forehead ɗinsa. Bakinsa ya shiga mutsawa a ƙoƙarinsa nason furta wani abun amma yadda laɓɓansa sukai masa nauyi ne ya sashi taune lips ɗinsa cikin zuciyarshi ya shiga faɗin."يا الواحد " "ka kawomin ɗauki da gaggawa" yana faɗin hakan ya ƙara lumshe idanunsa wanda suka suma lumshe sabida jirin dake ɗibansa,ganin hakan yasa Fauwaz ya ɗauko masa gorar ruwa mai sanyi baiyi musu ba amsa domin yana buƙatar jin sanyi a ransa murfin gorar ya ɓalle tare da ƙafawa a bakinsa saida yasha fiye da rabi sannan ya cire bakin gorar daga cikin bakinsa ganin ya samu nutsuwa ne Fauwaz ya amshi raguwar ruwan tare da faɗin. "Destiny lots of folks confuse of bad management with destiny, destiny is no matter of chance's it not a thing to be waiting for, it's a thing to be achieved, ur destiny change with ur thought". Wani sanyi ne ya shiga ratsa zuciyarsa tare da ganggar jikinsa zuwa yanzu ya kamata ace ya yadda da ƙaddara kuma ya maida hankalinsa zuwa ga abida zuciyarsa domin yana jin abun a matsayin heart dream first aid box Fauwaz ya ɗauko tare da zama kusa da abokin nasa tare da gyara masa wajan da yaji ciwo ɗago jajayen idanunsa yay tare da mannasu a kan Fauwaz cikin lion voice yace "ka kula da kanka" yana faɗin hakan ya miƙe tare da shigewa cikin bathroom yana shiga ya cire ƙananun kayan dake jikinsa ya sakale saman hanger,tsakiyar shower ya tsaya tare da shakarwa kansa ruwa'n shower'n hannayensa duka biyu ya dafe bango dasu tare da sadda kansa ƙasa ruwan ya shiga duka back naked skin ɗinsa mai kyau da kuma tsari. Ya daɗe yana sauraran dukan ruwa'n shower'n kafin ya ɗago kansa tare da lumshe idonsa ya saida full face ɗinsa tsakiyar ruwan sosai ruwan ya shiga dokan fuskarsa tare da shigewa cikin hancinsa ta bakinsa saiya zamana kamar wata a zabace yakewa kansa,ɗan tari yay tare da janye fuskarsa jin numfashinsa na ƙoƙarin ɗaukewa alwala yay tare dayin brush kana ya saka bathrope a jikinsa ya fitu kansa na zubar da ruwa tare da ƙwantaccen gashin jikinsa. Bedroom ɗinsa ya nufa yana zuwa ya fara gyara kansa cike da nutsuwa da kuzari ɗan lokaci kaɗan gashin kansa ya shiga fidda wani ƙamshi mai daɗi shaƙa sumar tayi luff a kansa har zuwa ƙasan wuyansa bai wani shafa mai ba sabida babu irin wanda yake using dashi ganin akwai body spray ne ya sashi ɗauka yare fesawa a jikinsa domin Fahad yana bala'in son ƙamshi baya wasa da turare,yana kammalawa ga buɗe wadrope ɗin kayan Fauwaz ɗan taɓe baki yay dan baison sharing kaya,cikin sa'a yaga ɓangaren wasu kaya sabbi wata coffie ɗin jallabiya ya ɗauka tare da zurawa a jikinsa ya shimfiɗa prayer mat ya tada sallar magrib. Fannerh na shiga cikin gidansu ta tarar da Afnerh kwance a kan sofa ta zurfafa cikin tunanin da kullum dashi take kwana kuma take tashi har yau ankasa gane abinda yake damunsa cike da zolaya Fannerh tace "pls Hadnerh zoki ta yani aiki mana" ɗago ido Afnerh tayi tare da zubawa Fannerh ido kafin ta murguɗa baki tare da faɗin. "Kin daɗe baki aikin ba"dry Fannerh tayi kana tace"a'a nikam zanyi tunda bake zanyiwa,na fahimci baƙin ciki kikewa My Husband to be sabida ba Heart dream ɗinki bane ko?"tsaki Afnerh taja tare da faɗin "Na you sabi". Ganin idanta biyewa Afnerh zata ɓata mata lokaci ne kawai yasa kai tsaye tayi kichen tana shiga ta tarar da Lami mai aiki cikin girmamawa Fannerh ya gaidata tare dayi mata sannu da aiki. Kayan da zata buƙata ta ɗauka cikin sauri ta shiga yin aikinta wajan 1hour ta ɗauka kafin ta kammalawa pepper soup and white rice sai cipis tare fruits salad sai lafiayyen coconut juice,tana gamawa ta haɗa komai cikin basket tare da barin kichen ɗin daret flat ɗinsu ta nufa tana shiga ta tarar da Afnerh tsaye gaban madubi tana gyara kanta da alama daga wanka ta fitu. "yawwa beb shirya ki rakani" tana faɗin hakan itama ta shige cikin toilet basu wani ɓata lokaci ba suka gama shiryawa cikin abayarsu iri ɗaya Fanner tasa milk wacce take da adon red flowers Afnerh kuma tasa red mai adon milk ɗin flower kasan cewarta chocolate colour sai abayar tayi mata kyau sosai suna matuƙar kama da juna dake suɗin twints ne Afnerh nada tsiwa sosai sannan bata fiya ɗaukan raini ba amma tana da sauƙin kai,yayinda Fannerh take da surutu sosai da kuma kyauta amma tana da nunƙufarci da kuma riƙo a tare suka fitu daga bedroom ɗin nasu inda suka tarar da Mama zaune a parlour tana kallon tashar zee world lokacin sun fara haska fire and ice kallonsu tayi tare da murmushi kafin ta sauke idanunta kan Fannerh tace"2weeks ya rage bikinki amma still baki bar fita ba?"turo baki tayi tare faɗin "Mama alrdy night fa wazai ganni yanzu?" girgiza kai kawai Mama tayi tare faɗin "yaro man kaza be carefull dai"Afnerh ce ta ƙarasu hawa wajan hannunta ɗauke da basket ɗin abincin a tare sukai hugging ɗin Mamansu tare da sakar mata peak a ko wanne kumatunta shafa kansu tare cike da soyayya tace "Allah yay maku albarka"da "Ameen" suka amsa tare da ficewa daga gidan. Da kallo ta bisu tana jin wani zafi da kuma raɗaɗi na damun zuciyarta tana jin har abada wannan baƙin cikin na zuciyarta bazai taɓa guguwa ba dashi zata mutu,ɗauke kai tayi jin idanunta na cicciko da hawaye. Suna tafe suna shirya cikin tafiyarsu mai nutsuwa a haka har suka ƙarasu Get ɗin gidan cikin ladabi Fannerh ta gaisar damai gadi yayinda Afnerh ta ɗauke kanta tare da shige cikin gidan tana gaf da shiga ɗan ƙaramin parlour'n Fannerh ta cimmata tsaki Afnerh tayi tare da faɗin"talkative"girgiza kai kawai tayi kana suka shiga parlon bakinsu ɗauke da sallama. Tsaye suka ganshi gaban t.v yana ƙoƙarin kunnawa shuru yay masu bayan ya amsa sallamar tasu cikin ransa. Sanye yake cikin baƙin wando 3 guater ko riga babu hakan ya bawa ƙyaƙƙyawar surarsa bayyana skin ɗinsa Afnerh tabi da ido ganin ko'ina yalwataccen gashi ne yay kwance luff cikin white sharning skin ɗinsa ga wani sahihiyin ƙamshi dake fita a jikinsa kamar daga zama suka ji saukar daddaɗar muryarsa "stop looking"shine kawai abinda ya faɗa lokacin daya gama kunna t.v Afnerh daskarewa tayi a wajan tare da mamakin mamallakin muryar domin wajan mutum guda ta taɓa jinta cikinsu babu wanda ya samu jarumtar ce masa ƙala duk da cewa basu ga fuskarsa ba amma sosai yay masu ƙwarjini. A hankali ya juyo tare da sauke ganinsa a kansu ƙarar da Afnerh ta ƙwala ya sashi saurin runtsa idanunsa tare da toshe kunnuwansa. Gaba ɗaya jikin tane ya shiga rawa sabida bayyanar ƙyaƙƙyawar fuskarsa wani irin shock ne ya kamata tare da bugawar zuciya hannunta ta ɗaga ta shiga nunasa ganin hakan yasa Fannerh tayi saurin riƙeta tare da jijjita"Afnerh" Afnerh" Afnerh" bakinta ne ya shiga mutsi a ƙoƙarinta nasun furta wani abu amma ta gagara hakan sabida numfashinta daya ɗauke ta saki basket ɗin hannunta tare da faɗawa jikin Fannerh babu numfashi. *DAN GIRMAN ALLAH DA ANNABI IDAN KIN KARANTA KINJI DAƊI KIYI SHARE PLS* F@y@l _The secret issues_ *💖JUYAYI💖* *18-19* *_Wattpad_* nimcyluv Before we ask God for anything we must first thank him for everything 🙌🏻🙇🏻‍♀️ *Dedicated to MaimunaAbdullahi* still waiting for ur hurt coffee I luv u my jerry🥰🌹 Not edited. .....Cikin tsoro da firgici haɗi da ƙaraji Fannerh ta shiga girgiza Afnerh tare za kiran sunanta "Afnerh pls wake up pls Hadnerh,ganin Afnerh ko mutsi ba tayi ne ya sashi taɓe baki tare da juya zai shige cikin bedroom ɗinsa sai kuma yaga rashin da cewar hakan ko babu komai baƙin Fauwaz ne kuma Fauwaz ya zama jininsa bazai taɓa iya wulaƙanta jinin abokin nasa ba. Bak damu da yadda surar jikinsa da take a buɗe ba a hankali ya taka tare da ƙara sawa wajansu cikin muryarsa wacce bata fita sosai sabida tsaɓar rashin son maganarsa,lumshe gajiyayyun idanunsa yay tare cije lips ɗinsa ya ƙara mutsa bakinsa tare da ware laɓɓansa yace. "ke Aljanu gareta halan?" baƙin ciki ne ya kama Fannerh har bata san lokacin data wurga masa wata uwar harara ba tare da faɗin"what Aljanu fa?Allah yay mata tsari dasu"ƙara taɓe fuska yay irin ko'a jikinsa ɗinan "ok farfaɗiya take kenan?"ya ƙara jefa mata wata tambayar cikin sauri Fannerh ta ɗago kanta tare da zuba masa baki ta saki ganin gama ɗaya ya maida hankalinsa kan T.V tamkar bashi yay maganar ba. Ganin ta ɗauke daga garesa ne yasa ta juya tare zuwa wajan freezer tare da saka hannu ya ɗauko gorar ruwa mai sanyin gaske cikin gajiyawa da kukan da Fannerh take ya lumshe idanunsa haɗi da saka hannu ya shafi ƙwantaccen gashin da yay luff a ƙirjinsa a haka ya ƙarasa wajan da suke,tsaki yaka cikin lion sound voice yace "oyya gefe"yana faɗin hakan ya sunkuya tare da riƙe gefen rigar Afnerh ya jawota haɗi da jinginata da jikin sofar dake parlon,murfin gorar ruwan dake hannunsa ya ɓalle kai tsaye ya sheƙa mata ruwan a jikinta. Wata wawiyar ajjiyar zuciya ta sauke tare da ƙanƙame jikinta jin wani a zababban sanyi daya ratsa jikinta lokaci guda a galabaici ta shiga faɗin. "shine wallahi shine tabbashi shine my heart dream shine mafarkin zuciyata a kullum dashi nake ƙwana nake dashi bana da burin daya huce na kanga a gaske,a kansa na guji dukkan waƴanda suka ce suna sona wallahi kaine eyes ball ɗinka sune suka ƙara tabbatarmin da haka,fatana da kuma muradina haɗi da cikar farin cikin zuciyata shine Allah ya bayyana min kai ubangiji kada ya ɗauki raina sai naga wanda zuciyata dake mafarki a kansa sai gashi na ganka when all is gone a lokacin da komai ya ƙare yanzu kaine duniyata kaine jindaɗi na,kaine muradina,kai farin cikina,kaine mahaɗin rayuwata,kaine bangwan da zan jingina naji daɗi a raina,dan Allah ka taimaki zuciyar data mace a kanka tun kafin tasan waye kai"ta ƙare zancen lokacin da take fashewa da wani irin razanannan kuka mai taɓa zuciya. Lallai "SO" masifa ne a duk halin da mutum yake ciki baya hana zuciyarsa bayyana abinda yake so da kuma muradin kasan cewa dashi koda ace bazai samu wannan abunda ƙaddara ta haɗa Afnerh da Fahad duk a cikin mafarki wanda a kullum tana tunanin mafarkinta gaskiya ne dalilin hakan ta sauya sunanta daga Afnerh zuwa "Hadnerh" suna mafi soyuwa a gareta. Lallai marfin Afnerh ya zamantu gaskiya domin gashi ubangiji ya haɗata da mafarkin zuciyarta ko hakan na nufi wani sabon shafin ƙaddarar wani daga cikinsu?. Ganin ta fita a hankalinta kuma ya gama tabbatar da abinda take faɗa gaskiya wanda tasa ƙwaƙwalwarsa ta tafi wani dugun tunani dasun tunasar dashi wani alƙawari da yay a baya wannan wanne alƙwari ne?wa yaywa shi?wannan sune tambayoyin da suke ƙasan zuciyarsa amma babu amsa. Cikin sanyin jiki tare da kasala ha saka tattausan hannunsa tare da ɗurawa saman fuskarta a sanyaye ya shiga goge mata hawayen dake zuba cikin idanunta. Haɓarta ya ɗago tare da zubawa oval face ɗinta idanu kafin ya taɓe baki tare da saurin saki fuskarta,kamar bazai magana ba sai kuma yace. "فاذكروني اذكر كم واشكرولي ولآ تكفرون. (آلبقرة ١٥٢)". "ku ammabace ni zan ambace ku,ku gode mini kada ku butulce min (baƙara aya ta 152). Numfashi ya fitar tare da ɗaure fuska ganin kallon da take masa,lumshe ido yay sosai maganar da yay tayi masa kafin ƙara saki numfashi tare cije lips kana ya ware laɓɓansa tare da faɗin. "mai yasa kika zama mai butulci wa Ubangiji?ya baki komai na rayuwa sai ɗan wani buri dake banne a zuciyarki amma ki kasa yiwa ubangiji tasbihi da kuma neman sauƙi daga wajansa,nayi tunanin kina da hankali ashe sakalyace?kulna ƙarajin kuka domin baya maganin damuwa akwai dubban mutanan da suka fiki shiga damuwa da kuma ƙuncin rayuwa su kuma suce me?idan mutum bai gode ni'imar Ubangiji ba amma ya gode azabarsa,ki zama mai ta wakkali kuma me yarda da ƙaddara ki ɗauki hakan matsayin ƙaddararki da ubangiji ya jarabceki da ita danya gwada imaninki kinji ko? Ajjiyar zuciya ta shiga saukewa tare da zure jikinta waje guda tare kafa masa idanunta tana ji dama ta dauwama a haka tana kallon baiwar zati da kuma surar da ubangiji yay masa. Raguwar ruwan daya zuba mata ya kafa a bakinsa ya shiga ƙwanƙwaɗa saida ya shanye tas sannan ya cire gorar ruwan daga bakinsa. A fili ya saki ajjiyar zuciya sosai ruwan yay masa daɗi maƙoshi tare da magana a zuci"Rabbi ka shayar damu ruwan alkausara". Cikin nutsuwa ya juya tare da zama a kan duguwar sofa ganin gaba ɗaya ya gaji ga wani bacci daya keji ne ya sashi ware idonsa tare da mannasu a kan Fannerh wacce ta zubawa Afnerh ido domin sosai ta kejin tausayin ƴar uwarta ta, saukar muryarsa data jine ya sata ɗago kai tare da zuba masa ido dan baza taɓa iya cewa taji abinda yake faɗa ba. Ya tsuna fuska yay tare da ɗauke kai ya maida kallonsa wa Afnerh wace take zauna ko mutsi ba tayi sai ajjiyar zuciya take saukewa a kai²,Tausayin tane ya kamashi cikin taushasshiyar murya yace. "mai kuka aban abinci ina jin yunwa"cikin sauri Afnerh ta miƙe jikinta har rawa yake dan ba tayi tunanin hakan a wajansa ba,kallo ɗaya tayi masa ta fahimci shiɗin mutum ne wanda bai damu da magana ba sannan shiɗin miskiline uwa uba girman kai amma sam bata damu da hakan ba indai zai nuna mata ƙauna zai zauna da ita zata iya jure duk wata halayya tashi. Basket ɗin abincin ta ɗauka tare da ƙara sawa inda yake zauna tana zuwa ta zauna ƙasan sofar tare da ɗaukan plate ta buɗe wata wamer nan ƙamshin abincin ya daki hancinsa cikin saurin ya lumshe idanunsa wanda hakan ya zame masa ɗabi'a. Zallar chips ɗin tare da ɗaukan wani glass cup ta siyaya masa fruit salad ɗin,cikin rawar murya tace"gashi"yi yayi kamar baiji abinda ta faɗa domin ya fahimci itama bata son magana sosai. Turo baki tayi kamar zata fasa ihu tace"the food is ready"ware manyan dara-daran idanunsa ba tare daya kalleta ba ya zamu da ƙafarsa ƙasan sofar tare da sakkowa ya zauna a kan capert bai damu da zaman da yay kusa da ita ba,dan ko ajikinsa impact bai ɗauketa wata babbar macen dazai damu kansa danya zauna musanta halima shi mata duk kallon maza yake babu wata macen da zaiji wani feelings a kanta. Zamansa kusa da ita yasa taji wani mugun shock ya kamata take wutar sonsa da ƙaunarsa ta ƙara huruwa cikin zuciyarta,tabbas ya cika namijin da dukkan wata ƴar mace ta ganshi za taji ƙaunarsa a lokaci guda,ware ƙofar hancinta tayi tana ƙara shaƙar ƙamshin dake fita daga jikinsa a sanyaye tayi magana yadda shine kawai zai iya jin abinda ta faɗa banda Fannerh da take tsaye sai kuma Fauwaz wanda zuwansa gidan kenan. "kai ɗin gwarzu ne" Girgiza kai kawai yay tare dayin bisimillah ya saka zara-zaran ya tsunsa tare da fara cin abincin,Fannerh tunu taja basket ta zubawa habibinta abinci sunayi suna shira. Fahad bai wani ci abincin da yawa ba ya ture ko fruit salad ɗin bai sha ba ya miƙe tare da shigewa cikin toilet ya ɗauki lokacin kafin ya fitu suna zaune ya fitu sanye da bathrobe jikinsa na ɗigar da ruwa a haka ya ƙarasu wajansu tare da kallo Fauwaz taɓe baki yay shi a dole soyayya yake cikin ransa"ƙaddararka soyayya da underage"a fili kuma yace "boddy goodnight"ɗaga kai Fauwaz yay tare da murmushi kafin yace"Na ɗauka zakuyi hira da Afnerh"kallonsa yay da alamar tambaya sai kuma yace"wani abune haka?"dariya Fauwaz yay tare da kallon Afnerh wacce take turo baki gaba tare da fidda wasu sabbin hawayen ɗauke yay tare da faɗin"eh wata abace gata nan a bayanka ai"tsaki Fahad yaja dan ardy yasan wace Afnerh ɗin tun ɗazu yaji sister ɗinta na kiran sunanta,baice masa komai ba ya juya zai shige bedroom ɗinsa tayi saurin miƙewa tare da sakin kuka danji take zuciyarta kamar zata fashe,waro manyan idanunsa yay ganin kuka baya yi mata wani ƙawataccen murmushi yay lokacin daya tuna da Lili ko magana ce bata gamsheta ba yanzu zata saka maka kuka harda birgima bare kuma faɗa cije lips ɗinsa yay tare da ware laɓɓansa a fili yace"i'm still waiting for u my sunshine bby"jin haka yasa Afnerj da katawa da kukanta tare da zuba masa idanu ta gefenta ya huce ko ƙara kallonta baiyi ba. Sun ɗan jima a gidan kafin su ɗauki basket ɗin tare da yiwa Fauwaz sallama suka koma gida. Da kuka Afnerh ta shiga gidan tana zuwa ta faɗa jikin Mama tare da fashewa da kukan cikin kiɗima ta fara tambayar abinda ya faru,cike da nutsuwa Fannerh ta shiga gawa Mama komai har rashin ko in kula daya nunawa Afnerh ɗin. Da ƙyar Mama ta rarrashi a Afnerh tare dayi mata alƙawarin ita da kant zata amsar mata soyayyarsa. *** *** Wajan satin Najma uku kenan gidansu Faisal dukkan wani jin daɗi Ammi na bata shi,amma batun farin ciki wajan Faisal babu shi kullum rashin kulawarsa gareta ƙara yawa yake. Misalin 7 na dare shiguwarsa daga sallah kenan ya zauna a babban parlon gidan tare da kunna karatun Sudais cikin suratul Maryam,sosai karatun yake masa daɗi kuka yake sashi nutsuwa domin baƙin ciki da damuwarsa suna nan kwance ƙasan zuciyarsa saima abinda ya ƙaru. Lallai Ƙur'ani haske ne aduk zuciyar data ƙawatu da son karanta shi kuma dukkan wanda ya dogarar da alƙur'ani bazai taɓa taɓewa ba. Ƙamshin turaranta daya daki hancinsa shine kawai ya tabbatar masa data ƙarasu parlon ganin tare suke da Ammi ne ya sashi sakin fuskarsa tare da zubawa abin idanu gani yake kamar yau ya fara ganinta idanunsa da suka cicciko da hawayene yasa yay saurin ɗauke kai tare da faɗin"barka da dare my luv"cikin so da ƙaunar ɗan nata ta zauna gefensa tare da shafa sumar kansa tace"yawwa yaya aiki?"..."mungode Allah" shine kawai abinda yace..ɗaga kai Ammi tayi tare da faɗin Najma zauna ma..ruwan hawayen data gani kan fuskar Najama shine ya hanata ƙarasa abinda tayi niya cikin kulawa tace"lafiyanki lau?"wasu hawayenne suka ɓalle mata ta shiga girgiza kanta kafin ta durƙushe gaban Ammin tace"Ina son komawa gidanmu domin na gaji da zama da Faisal,banyi iskanci tun ina budurwa ba haka bazanyi ina matar aure ba,amma yasan da cewa nima mutumce kamar kowa kuma dole akwai haƙƙina daya rataya a wuyansa,bansan mai nayi masa amma baison haɗa gado dani😳hakan kuma illah ce wa rayuwata koda ace bashi da lafiya ya kamata ace ya faɗamin tunda niɗin matarsace bawai zaman dadiro muke dashi ba". Ai maganarta tamkar saukan ruwan dalma haka yake jinsu cikin zuciyarsa baƙin ciki takaici ladama na aurenta babu wanda baiyi ba,hakan kuma ya tabbatar masa bata da kunya ko kaɗan sannan ita ɗin ba matar sirri bace,cikin ɓacin rai Ammi ta kalli Faisal wanda idanunsa yake a rufe ruf tamkar maiyin bacci tace. "ka tabbatarmin niɗin ban isa da kai ba kuma baka ɗauki maganata da muhimmanci ba,ka sani indai ni nayi cikinka nayi naƙudarka kuma na shayar dakai ruwan nono a yau basai gobe ba nakeson ka bawa Najma dukkan wani haƙƙinta da yake kanka idan kuma ba haka ba wallahi Faisal zan sallamawa duniya kai badan kaga mahaifinka baya nan ba kakemin wannan abun to kaje dani dakai za'aga wanda zaici riba". Idanunsa ne yay jajur tamkar gauta sosai kalaman Ammi suka daki ƙawon zuciyarsa meyasa Ammi ba zatai masa uzuri ba?mai yasa ba zata fahimci zafi da raɗaɗin abinda yake damunsa ba? Mai yasa ba zata fahimci abinda zuciyarsa da gangar jikinsa suke muradi ba? Runtsa idanunsa yay da ƙarfi tare da miƙewa cikin zafin rai ya kalli Ammi yace "zanyi dukkan abinda kikeso koda bakan zai baƙanta raina,zanyi abinda kikeso Ammi koda zuciyata zata buga,zanyi abinda kikeso koda hakan zai zama sanadiyar rasa raiana,tabbas inajin hakan shine ƙaddararta kuma shine silar rasa raina,zanbar duniyar kamar yadda Lubna da iyayenta suka bari inaji a raina I think my Lubna is calling me, I think it's time to go tabbas lokacina na zuwa wajan mahaliccina yay Ammi kuma insha Allah indai kece kike haifeni kika kula dani da yardar ubangiji bazan bar duniyar nan ba saina tabbatar maki da kalamanki zanyi tabbas zanyi abinda kikeso Ammi" Yana faɗin hakan yasa hannu ya riƙe Najma tare da janta da sauri a haka suka ƙarasa flat ɗinsu,tsoro da fargaba gaba ɗaya sun cika zuciyar Najma babu kalaman da suma tsaya ma sai "tabbas zabar duniyar kamar yadda Lubna da iyayenta suka bari"me hakan ke nufi wace duniyar zai bari? Ina zaine'inane inda Lubnan da iyayenta suka tafi"tambayoyin da suke zuciyanta kenan amma babu wanda zata tambaya ƙara ta saki sabida cillata da yay kan gado kanta ya daki fuskar bed ɗin a zafafe ya cire rigar jikinsa tare da long jeans ɗin dake jikinsa ya rage daga shi sai boxer cikin saurin ya faɗa kan gadon,babu ɓata lokaci ya zare zanin dake jikinta babu wani romance haka yay bisimillah tare dayin Addu'a ya shiga jikinta. Zafin da raɗaɗin da ta jini yasa ta fasa wata mahaukaciyar ƙara ta shiga ya ƙushinsa tare dayi masa Allah ya isa ganin hakan bazai mata ba ta shiga cizonsa tare daya ƙushinsa. Faisal bai rabu da ita ba saida yay mata lilis yay mata fata-fafa sannan ya zare jikinsa tare da sakin wani mahaukacin kuka kamar mace sunayen Allah ya shiga kira tare da salatin Annabi hannunsa dafe da saitin zuciyarsa wata bugawa da zuciyarsa tayine yasa shi faɗin "La'ilah ha'illahu Muhammadur Rasulillah" wani gudan jinine ya fitu ta hancinsa da bakinsa lumshe idanunsa yay yana mai ƙara jadadda sunayen Allah a zuciyarsa,dai² lokacin da Ammi ta buɗe ƙofa ta shigo yay dai² da lokacin daya saki wata shaƙuwa mai ƙarfi. *Dan Allah dan Annabi kuyimin share dan Allah wlh bbu lokaci groups sunmin yawa sai kuna taimakawa🥰👏🏻luv u all* Team Najma Congratulations🤾🏻‍♀️💃🏻 _The secret issues_ *💖JUYAYI💖* *20-21* *WATTPAD* Nimcyluv *Telegram* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ _Masoyan *NIMCYLUV* ga mahajarmu na telegram yana da kyau kuyi join domin samun littafai cikin sauƙi da kuma amfanuwa da_ *programs* _ɗin daza muna gabatarwa kuma dukkan wani posting ɗina zai kuma can zai zama VIP group ɗina na musamman kuyi share zuwa wasu groups ɗin dan nuna ƙauna dan Allah._ ......Jinin dake fita ta hancinsa da bakinsa ne yasa Ammi saurin fasa ƙara tare dayin kansa tana zuwa ta durƙushewa gabansa ta shiga girgizashi tare da kiran sunnansa "Faisal" Faisal"..ganin ko mutsi ba yaye bare ta saka ran zai buɗe idanunsa har yay magana. Da gudu tayi waje tana rabza kuka ganin halinda ɗan nata ke ciki tana ƙoƙarin ficewa daga parlon domin ta samu ta kira mai gadi ya taimaka mata,a nan sukayi karo da Papi wanda ke ƙoƙarin shiguwa. Ganinta a rikice ne ga kukan da take ya sashi saurin sakin jakarsa tare da jawota jikinsa,kuka ta fashe dashi tare da faɗin. "wacce uwace ni?ina ƙoƙarin kashe ɗana da kaina wlh.."kukan da yaci ƙarfinta ne yasa bata samu damar ƙarasa abinda tayi niya ba. Bayanta ya shiga bubbugawa tare da jijjigata,shi kansa tun safe ba dai² yake jinsa ba fargaba tsoro bugun zuciya faɗuwan gaba shine abinda yake damun ransa dalilin hakan ya tattaro kayansa zuwa gida,cikin dauriya yace. "lafiyanki ɗaya wannan kukan duk na mene?". Cikin firgici ta shiga bashi labari ai bata ƙarasa ba yasa hannu ya tureta da gudu yay flat ɗin faisal,yana shiga ya ganshi yashe a ƙasa bai tsaya jiran komai ba ya sunƙuci ɗan nasa yay waje. Hijab Ammi ta ɗauka tare da rufa masu baya cikin sauri ta shiga motar da wani irin speed Papi yaja motar daman tuni mai gadi ya buɗe get cikin sauri ya halba hancin motar kan titi. Lokacin kaɗan suka isa Amino kano teaching hospital,suna zuwa ma'aikantan asibiti sukayo kansa a haka aka ɗurashi zuwa bed ɗin marasa lpa akai cikin emagency room dashi. A nan ƙofar emagency ɗin suka shiga zirga-zirga sosai zallar tashin hankali ya bayyana kan fuskar Papi tym to tym yakan girgiza kansa tare da fesar da numfashi. Sun ɗauki wajan 1hour kafin likitocin su fitu da sauri Papi yay wajan babban likitan tare da faɗin. "Dr meke faruwa da lafiyan ɗana?" Gomi Dr ta ya share kana ya kalli Papi yace. "follow me" yana hakan ya juya zuwa cikin office ɗinsa,jiki babu ƙwari suka rufa masa baya,glass ɗin idanunsa ya zare kafin yaja numfashi yace. "tunda na ganka nasan ciwon Faisal yayi tsauri kusan kullum yana zuwa amsar magani"cikin rashi n fahimta Papi yace. "kullum fa Dr ka sani a fargaba pls meke faruwa?". Tausayin Ahalinne ya kama Dr numfashi ya ƙara kafin ya maida glass ɗinsa yace. "ciwon zuciya ya kama Faisal kuma ciwo mai tsanani irin na lokaci guda ɗinnan,yanzu mun ɗurashi bisa magana kamar su,H2Blockers, Lisinopril Perindopril Quinapril Trandolapril Angiotensin,ya buƙaci kada na sanar dakai sabida yana saran samun lafiya nan kusa,amma abin mamaki kullum Faisal cikin ƙunci da damuwa haɗi da tunani nayi nayi ya faɗamin damuwarsa yaƙi,yanzu haka zuciyar sace ta buga bashi da wani sauran lokacin sai wanda ya ubangiji ya tsara masa but i'm sorry to say zai wahala ya tashi zuciyansa yaje matakin ƙarshe ta tashi daga aiki". "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shine kawai abinda Papi ya shiga faɗa gaba ɗaya jikinsa rawa yake kansa ya ɗura kan table ɗin dake kusa dashi idanunsa na fitar da wasu ƙwalla na tausayin kansa da kuma ɗan nasa. Ammi kam tsoran da yay mata yawa ne yasa yawa ne yasa ta kasa cewa komai kukanma ya tsaya gaba ɗaya sai kanta data ɗaga sama tana tunani. Miƙewa Papi yay kai tsaye special room ɗin da aka kwantar da Faisal ya nufa yanz ya gansa kwance flat gaba ɗaya jikinsa na'oruri ne sai ƙara suke hannunsa ɗaure da drip,zama yay gefen bed ɗin tare da riƙe hannunsa cikin muryar kuka Papi yace. "Son kada kayimin haka dan Allah ka tashi ka faɗamin damuwarka wlh wlh na ɗauki alƙawarin cika maka ita da dukkan aƙarfina lafiyata aljihuna dan Allah ka tashi na tsani ƙwanciyar nan"ya faɗa lokacin da kuka ya ƙwace masa,ƙansa yaji an dafa hakan yasa Papi saurin ɗaguwa cikin farin cikin ganin Faisal na mutsa hannunsa,hannun ya kama ganin rubutu a tafin hannunsa ya sashi riƙe hannu abinda yaga an rubuta ya sashi saurin runtsa idanun ko shine ya nuna masa ba dai ba,a fili Papi ya ƙara duba rubutun. "I want see her,my eyes want to see my Lili,i knew she's alive itane damuwata pls". Cikin damuwa da kuma aro jarumta Papi yace. "tabbas tunda zuciyanka yaƙi baka Lubna ta rasu babu shakka akwai wani ɓoyayyen sirri akan hakan,zanje insha Allah zanyi ƙoƙarin naga na haɗaka da muradin ranka"yana faɗin hakan ya fice daga cikin room ɗin. Najma Baƙaramin wahala tasha wajan Faisal ba domin ba tayi tsammanin hakan ba,ta ɗauka abin zai ƙayatar za taji daɗi fiye da yadda ake fasallata mata daɗinsa,ta ɗauka zai mantar da ita duniyar da take cikin ta hanyar dulmiyar da ita a cikin salon nasan ƙwarewar,ta ɗauka zai jiyar da ita daɗi da kuma farin cikin da'a taɓa yiwa wata ƴar mace ba,amma saiya shayar da ita gubarsa da kuma ɗacinsa haɗi da azabartar da ita ya dasa mata tsoran abun. Da rarrafe ta shiga toilet ruwan zafi da haɗa tare da zare rigar jikinta cikin ruwan ta shiga azabar data jine yasa ta fawa ihu tare da ƙanƙame jikinta waje guda,sosai take kuka cike da muradin rama abinda yay mata danta ɗauki alƙwarin nemo maganin dake saka feelings in five minutes,wanka tayi tare dayin wankan tsarki tare da ɗaura towel a jikinta tana tafe tana kwala ƙafa,ta kusa zama kan bed ta hangi wani dairy ɗauka tayi tare buɗe shafin farko da manyan baƙi taga an rubuta MY BEBY BOO kafin a rubuta wasu zafafen kalaman soyayya a haka ta shiga duba sauran shafukan har tazu last page inda aka rubuta "WHEN ALL IS GONE" tashin hankali wanda ba'a saka masa rana jikin Najma ne ya shiga ɓari tare da karkarwa yayinda wata zufa ta shiga ƙeto mata dai² lokacin da tabbas baya nan da Faisal ya rubuta ya gama tabbatar mata Dad da Mamy haɗi da Fahad sun jima da rasuwa kuka ne ya ƙwace mata ta rerawa saida tayi mai isarta kafin ta duba bayanin ƙarshe. _ko kowa zai yarda kin mutu babu ni domin zuciyata a kullum da tunaninki take bugawa,ina nan ina zaman jiranki daga nan har ƙarshen rayuwata,kece farin cikina muradin raina da sonki nake ƙwana nake tashi i luv u i luv the rest of my life i luv soo much i'm always be ur side my Bby boo mu'ahh💋_ Wani ƙyaƙƙyawan murmushine ya suɓucewa Najma cikin farin ciki tace "Mutuwarki ya zama abu na farko daya sanyaya miƙe daya daɗe yana damuna shekara da shekari kin ƙwace komai nawa ƙyau ilimi farin jini gata muradin raina hankali nutsuwa komai dai kin ƙwace why Lubna i lost everthing because of u pulish gril i hate u tsana mai yawa,koda baki mutu ba na ɗauki al'ƙawarin ra baki da ranki kamar yadda kika rabani da dukkan wani farin cikina zuwa now he is mine for rever and ever". *** *** Abuja. Idan tace abun duniya bai isheta ba tayi ƙarya gaba ɗaya cikin firgici take kullum a tsorace take,ita kanta bata san meke damunta amma ƙasan ranta tana ji akwai wani baban kuskure data tafka kullum ciki tunani da zullumi take yayinda a koda yaushe ƙyaƙƙyawar fuskarsa keyi mata gizu a cikin dara-daran manyan idanunta waye shi?a ina yake wannan shine tambayar dake damunta wacce a kullum take son furtawa wa wani ko zata samu sauƙi a ranta amma babu dama,babu wanda zata gayawa taji daɗi,Yusrah da take matsayin ƙanwar wanda zata aura ko kuma Momma dake matsayin uwa a wajansa ko kuma shi ɗin kansa zata tambaya tace zuciyarta wani take muradi bashi ba? Lumshe idanunta tayi hakan ya bawa hawayen cikin idanunta damar sakkowa daga cikin idanunta zuwa kan fuskarta,lumshe ido ta ƙara cike da muradin son ƙara ganin fuskarta duk da har yau ba full face ɗinsa take gani ba amma ganin fuskar tasa ya fiye mata komai a yanzu domin sosai takesa zuciyarta nutsuwa da kuma dai² tuwar bugun zuciyarta,ɗan cije lips tayi ganin ba taga abinda take muradin gani ba hakan yasa ta fashe da wani irin kuka haɗi da cusa kanta cikin fillow ta shiga rera kukanta,sai yaushe ne zata daina jin abinda ta keji a cikin zuciyarta,yaushe ne zata daina kukan rashin Ahalinta?mai yasa ƙaddara take juya rayuwarta kamarta samu ƙwallo a cikin fili. Bata ji a wannan karan zata iya rauninta domin damuwar sosai take son fallasa abinda yake cikin zuciyarta cikin sauri ta miƙe tare da sakin siririyar ajjiyar zuciya,Tunawa da yayarta ta ya zama wani garkuwa a gareta ya kuma zama wani farin cikin daya samu gurbin raƙe mata damuwar ranta. Ƙatun hijab ɗinta ta ɗauka tare da kallon madubi ya mutsa fuska tayi ganin yadda fuskarta ta faɗa sai idanunta daya ƙara girma ga ƙyan fuskarta ya ƙara fituwa babu abinda ke birgeta a fuskarta sama da cute peach lips ɗinta daya ƙara ɗan tudu da kuma sharning sosai take samun kulawa wajan Momma da kuma gogan nata Sufyan. Ficewa tayi daga ɗakin ta nufi parlo a nan ta tarar da Momma sai Sufyan da shiguwarsa kenan sosai yay kyau cikin shigar blue ɗin t.shirt sai long dark black jeans dake jikinsa yana zauna yana danna waya,ƙamshin turarenta ya kawowa hancinsa ziyara lumshe idanunsa yay tare da buɗesu ya mannasu akanta sosai tayi masa kyau yana jin ina babu Momma awajan da babu abinda zai hana ya shaƙi daddaɗan ƙamshin turarenta. Jikin Momma taje ta lafe tana ji tamkar a jikin Mamynta take bakinta na rawa tace. "Momma ina neman izinin zuwa kano wajan sister na tuna da ita ina buƙatar ganinta". Kanta Momma ta shafa tare da faɗin "Lubna kin faɗa a ƙorarran lokaci gashi jibi jirginmu zai tashi suwa bikin ƴar uwar mijikin a can za'a haɗa ai naki keda Sufyan" Turo baki LILI tayi tare da ƙara shigewa jikin Momma ta shiga sauke numfashi ita sam ta manta matsayin uwar miji take,cike da zallar shagwaɓa tace. "pls Momma i want see her ita ɗaya nake da"murmushi Momma tayi tare da zare jikinta daga na Lili tace. "babu damuwa kuyi magana da Sufyan gobe da safe saiya kaiki"gdy tayi mata. Miƙewa yay ya dawo inda take zaune kallonta yay sosai kafin ya maida idanunsa kan lips ɗinta ganin ya fara fita on his mood domin sosai ƙamshin turarenta yaƙe ƙara masa wutar sha'awarsa harya matsu sati ya zagayo domin ta zama mallakinsa. Miƙewa yay tare da kallonta yace "7 zamu bar gida so don't keep me waiting"yan faɗin hakan ya shige cikin flat ɗinsa jin wani hurt feelings ɗinta na tasu masa. _The secret issues_ *💖JUYAYI💖* *22-23* *_Wattpad_* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb or Nimcyluv *_Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ _Just follow me,follow my pen,be with me,luv my story🥳rubutu yanzu muka fara karantu yanzu kuka fara fas masoya i solute you maƙiyama i solute you🤾🏻‍♀️_ بسم الله الرحمان الرحيم اللهم صل وسلم على سيدنا محمد رسول الله عليه و سلم. ......Lumshe lulu eyes ɗinta tayi tana jin wani irin ya nayi na ratsa sassan jikinta,peach lips ɗinta ta shiga taunewa tana me fitar da wani zazzafan numfashi,a hankali ƙyaƙyawawan sexy eyes ɗinsa suka shiga bayyana cikin idanunta ƙara curewa tayi waje guda tare da saki wani ƙawataccen murmushi mai cike da nuna “SO” da kuma “ƘAUNA” daga zuciya zuwa zuciyar da aka amince da ita,babu abinda yake faranta irin taga ƙyaƙƙyawar fuskarsa nayi mata gizo wanda har yau bata gama ganin his full face ba kuma tana ganin rabi sometimes afi ɓoye mata fitinannun idanunsa wanda tafi muradin,tunaninsa ya zama patner ɗinta bawai yanzu aka fara hakan ya samu a saline wajan 7year back da suka shuɗe. Cike da tunaninsa da kuma kewar wani haɗaɗɗan bacci yay gaba da ita a nan kan sofa,sanyin asuba tana A.c sune suka data da ita daga dugun baccin data tafi,a sanyaye ta miƙe tare da shigewa bedroom ɗinsu tana shiga ta huce toilet ta haɗa ruwa mai zafi a hiter cikin sauri tayi wanka tare dayin brush ta ɗaura alwala,jallabiya ta mata ta zura a jikinta tare da saka hijab ta shimfiɗa prayer mata ta data sallah raka biyi (Raka'atul fijir)lazimi ta tsaya yi kafin ayi Assalatu ta miƙe tare da gabatar da sallah ta daɗe tana yin addu'a tare da neman zaɓin uban giji a kan auren,duk da haryau bata baƙin ciki da auren kamar yadda bata ɗauki Sufyan matsayin abokin rayuwa ba,amma ta ganin ƙimarsa cikin sanyi jiki ta ɗaga hannunta sama idanunta na fidda ƙwalla ta fara addu'a. _Ya Allah kaine ka halicceni kuma kaine ka ɗuramin duk wata ƙaddara dake zuwarmin badan baka sona ba sai dan gwada ƙarfin Imani na,tabbas na amince wlh na yarda ƙaddara mai kyau da mara amma zuciyata bata ƙwari mai rauni banjin zata iya ɗaukan lukutar ƙaddarar,inajin zuciyata nayimin zafi da raɗaɗi ubangiji ka kawomin ɗauki Allah ka haskamin zuciyata domin fahimtar abinda ta keso,Ya Allahu ya Samadu Ya Malikil mulkuzul jalalu wal'ikram ka bayyanin sayin idaniyata kuma ka nunamin cikakkiyar fuskarsa ko Allah zan ganshi a gasken gaske kuma a zahiri,shiɗin garkuwa ne tabbas bangone na rayuwata Ya rabb kasa ya zama muradin rai da ruhi haɗi da gaggar jikina,Allah kayi iyayena sakayya tun a nan gidan duniya Allah ka kawo makamin da zai taremin ƙatun yaƙin dake gaba na Ameen ya rabbil alamin_ Lumshe idanu tayi tare da fitar da wasu siraran hawaye,sosai take jin matsanancin kewa haɗi wutar son ruhin cikin idanunta shiɗin farin cikin tane, murmushi tayi tare da faɗin "Allah sarki Faisal luƙutar ƙaddara mai zafi ta rabani dakai ubangiji yasa Sufyan ya zama mai hqr da sanyi hali irin naka,Allah ka raba Sufyan da zafin rai da miskilanci haɗi da kafiya irin na Boobyn" Ganin lokacin naja yasa ta miƙe cikin ƙaramin lokacin ta gama shirinta cikin wata lafiyayyiyar duguwar riga ta atamfa ɗinkin Ashap gashin kanta ta gyara tare da tufkewa bata wani saka ɗan kwali ba ta ɗauki milk ɗin beby hijab ta saka wata ya dace da milk and cofie ɗin atamfar data saka,babu wani tarin make up a fuskarta sai bby peach lipstic data saka a lips ɗinta,sabuwar wayarta ta ɗauka tare da saka cikin hand bag ɗin hannunta kana ta kalli Yusrah dake bacci har yau bata tashi ba kasan cewar ba sallah take ba. Zaune tasa mesu a parlo ya gama shirinsa cikin shaddarsa mai kyau yana danna wayarsa,wajan Momma ta ƙarasa tare da shigewa jikinta,murmushi Momma tayi tare da faɗin "Amaryar Sufyan an fitu maza ku tafi tym is not our side kusan gobe zamu ɗaga yana da kyau kuyi sauri"jinjina kai Lili tare da sakinta "oyya muje ko"ya faɗa tare da ficewa daga parlour'n. Lokacin data isa harya shiga mota yay mata key ita kawai yake jira,side ɗin mai zaman banza ta zauna tare jingina jikinta ta jikin kujera,cije lips yay tare da ɗauke kansa taga kallonta, key ya ƙara yiwa motar tare da cillata kan titi ya farara sharara gudu daman sam bai iya dreving a cikin nutsuwa ba,few hours suka ƙarasu garin kano ta dabu tubbin giwa ko dame kazu anfika. *** *** Duk yadda Fahad yasu zillewa Afnerh abun yaci tura kullum cikin kuka take masa akan yay hqr ya nuna mata so amma taƙi yarda duk yadda ya keson fahimtar da ita illar hakan idanunta ta rufe yanzu da safe saida yay mata tsawa tare da alƙawarin zaizo kiranda Maman take masa sannan ta hqr ta barshi ya tafi hospital ɗin daya samu aiki domin duba marasa lpa. Shiguwarsa kenan ya watsa ruwa tare dayin sallar la'ar ya kwanta saman duguwar sofa bacci fal idanunsa gashi sam baison tunani da zarar ya rufe idanunsa firgitattiyar surar jikinta take masa yawo cikin idanunsa duk yadda yasu yaga fuskar mamalkin tsarkakkiyar surar abin yaci tura,shi kaɗai yasan wahalar da zuciyarsa kesha idan surarta ta gama haukata tunanin wani lokacin a kan Fauwaz yake hucewa yayta surfa masa ƙatuwar masifa a haka harya gaji ya daina,kuma abin mamakin yana gama masifar zai dawo jikin Fauwas ɗin ya shigesa yayta sauke ajjiyar zuciya a haka bacci yake ɗaukesa wani lokacin. Ƙara lumshe tsumammun idanunsa yay tare dajan sajen daya ƙawata zagayayyiyar fuskarsa mai cike da kwarjini da kuma haiba haɗi da hasken addinin daya gama rasa zuciyarsa da gaggar jikinsa,baiji shiguwarta ba sai hannunta da yaji ya sauka a kan fuskarsa,ko mutsi baiyi domin ta fara bashi haushi sam baisan raini kuma ya fahimci tana dash,turo baki Afnerh tayi tare da faɗin "Allah ka tashi bafa bacci kake ba"still shuru ya ƙarayi kafin ya ankara ta fasa masa wani ihu aka,cikin firgici ya miƙe tare da jawota ya ƙanƙameta danshi tsakani da Allah ya ɗauka wani abunne ya bata tsoro koya cijeta. Lafewa tayi jikinsa ta shiga rera kuka ganin babu komai iskancinta ne yasa hannu ya janyeta jikinsa tare tsuke fuska ya miƙe tsaye,da sauri ta riƙe hannunsa tare da faɗin"ka Manta kiran Mama?"hannunsa ya zare tare dayi mata kallon sama da ƙasa da ƙyar ya wara laɓɓansa ta hanyar cewa. "Ban hanaki koda wasa ki ƙara taɓa jikina ba?keko kunyata baƙya ji"tayaya zan soki ina son mace mai kunya da kamala da kuma riƙo da addinin Annabi muhammadu S.W.A,kije darajarki ta ƴar mace idan kina son naga ƙimarki kira kuma zanine ai dan haka ɓace daga ɗakin nan kafin na ƙwarfeki" Yana faɗin hakan ya shige cikin toilet few minutes yay taken shower ya fitu ɗaure da towel a waist ɗinsa jikinsa na ɗigar da ruwa,sosai yay mamakin ganinta a tsaye taurin kai yay mata yawa,tsaki yaja tare da shigewa cikin bedroom ɗinsa,cikin saurin ya shirya tare da saka dark blue ɗin yadi mai ƙyan gaske da manyan zane sosai yadin ya amshi farar fatar jikinsa har singlet ɗin jikinsa ana iya gani,sumar kansa ya gyara tare da ɗaukan mayataccen turarensa na Ohud mood mai daɗin ƙamshi farin glass ɗinsa ya ɗauka tare da mannashi a fararen manyan idanunsa wayarsa kawai ya ɗauka ya fitu,a nan parlour ya tarar da Fauwaz yana shan coffe,zuba masa ido yay na wani lokaci kafin yaɗan ya mutsa fuska sosai maƙoshinsa keyi masa zafi sbd da maganar da Afnerh ta sashi ɗazu. "oya Man tashi" sarai ya gane nufinsa amma ya share yace "inafa nikam na gaji"haɗe rai Fahad yay tare da matsawa bakin ƙofa yace"banzon tantirance"dry Fauwaz yay tare da ajjiye glass cup ɗin hannunsa ya miƙe suka jera suna tafe yana jansa da shira kasan cewar shiɗin ba gwanin shira bane sai yaja bakinsa yay shuru saidai kawai ya jinjina kai,a haka suka isa bakin get ɗin gidan cike da mutuntawa Getman ɗin ya buɗe masu ƙofa. A compound na gidan suka tsaya Fauwaz ya ɗauki wayarsa ya kira Fannerh lokacin ana tsaka dayi mata gyaran jiki taji wayarta na ƙara Afnerh ce ta ɗauka tare dasa a speaker"gamu a compound hope dai Mama na nan dan yace bazai daɗe ba baijin daɗi" dry Afnerh tayi farin ciki fal zuciyarta danta tabbatar yau Mama zata amsar mata soyayyarshi kamar yadda tayi mata alƙwarin. "ok come in side mana"shine abinda Fannerh tace tare da kashe wayar dan ita ɗagawar Fahad ɗin mugun fusata ta keyi fushinta ya kusa kufcewa a kansa,da gudu Afnerh ya miƙe taje ta faɗawa Mama ita kuma ta shige bedroom ɗinsu tare da sauya kayan jikinta aka fesa uban turare. Da sallama suka shiga parlour Fauwaz na gaba Fahad na bayansa fuskar nan tasa a haɗe babu yabu babu fallasa,gaba ɗaya suka durƙusa tare da gaida Mama kafinsu miƙe tare da zama kan sofa,"Fahad kaji saƙona wa..."maganarce ta maƙale mata bakinta na rawa ta shiga kallon Fahad tare da nunasa da hannu tace"Fahad kaine..kaine yau a gidana kuma a gabana?"ɗago kai yay cikin sauri zabura yay ya miƙe da sauri ya ƙarasa gabanta tare da faɗawa jikinta a hankali yace "Mamana" sai kuma ya fashe da kuka tare da ƙanƙameta ya shiga rera kukansa a hankali wanda ita kaɗai take iya jin kukansa,lallai ran maza ya ɓaci ba ƙaramin abu zaisa kaga Fahad na zubar da hawaye ba,ita kanta sau ɗaya ta taɓa ganin kukansa lokacin dazai tafi U.S karatu sosai yay kuka kamar ransa zai fita sbd bai son zuwa,bayansa ta shiga bubbugawa tare da shafa sumar kansa "kuka kuma kamar ga ƙwarzon yarona ba ya isa haka nan"ƙara shigewa jikinta yay yana jin kamar ajikin Mamynsa yake,ya jima maƙale da ita kafin ya zame jikinsa ya zubawa Mama idanunsa tare da shagwaɓe mata idan da sabo ta saba da shagwaɓar Fahad. "Mamana ina Uncle ɗina?"hararar wasa masa tare da faɗin"wanne irin uncle ɗinka kaifa nake shirin tambaya coz wajan watansa guda da rabi da tafiya wajan Daddyka why kuma nida nake nan zaka tambaye ni shi"kallon rashin fahimta yay mata tare da faɗin"u mean Uncle na wajan Daddyna how can that happen? Daddy is no more baya raye wajanwa zashi to"kallon maras hankali tayi masa tare da cewa"wannan wacce lukutar magana ce,waye baya rayen? Idanunsa ne suka sauya kala bakinsa na rawa yace "Mamana niɗin marayane mara gata i lost everthing luv,happiness,care,everthing Daddy,Mamy,Lili babu ko ɗaya cikinsu duk an kashesu"cikin firgici da fitar hayyaci ta ɗaga hannunta tare da sharara masa wasu firgitattun mari,tsabar girman mari saida yay maya lokacin hawayen idanunsa suka sami damar zubuwa daga cikin idanunsa,durƙushewa yay gaban Mama tare da kifa kasan in btw her laps ya shiga zauke numfashi mai zafin gaske jikinsa duka rawa yake. *** *** _Maiduguri road_ Horn suka danna da gudu mai gadi ya leƙo ganin sabuwar mota bata gidan ba ya sashi leƙowa tare da faɗin. "yallaɓai wajanwa kake nema?" kallon Lili Sufyan yay kanta ta leƙo dashi waje tace"Anty Najma fa?"jim ya ɗanyi kafin yace"ayya ai ƙaramin mai gida Faisal ne babu lpa suna Emergency na Aminu kano". Faɗuwar gabanta ce ta ƙaru lokaci gudu tsoro ya kamata tare da tunanin abinda ya sami farin cikin nata“Astagafirullah”shine abinda tayi saurin faɗa sanin cewa yanzu ya haramta gareta tunda yana auren ƴar uwarta,hawaya ne ya ɓalle mata ta shiga zubar dashi,Sufyan ne ya leƙa yace"mungode Baba"yana faɗin haka yaywa motar key tare dayin ribers ya jata da gudu tare da harbata kan titi. Lokaci kaɗan suka isa asibitin har lokacin kuka take wanda ita kanta bata san na mene ba,wayarsa ya ɗauka tare da latsata yana sauraran kukanta,ganin bashi da niyar fituwa yasa tayi saurin buɗe ƙofar kafin ta buɗe ya danna mata pin,kallonsa tayi da alamun tambaya"ki tsaya ki gama kukan ko?"share hawayen tayi cikin rawar muryar tace"pls get in"jinjina kansa yay kafin ya buɗe ya fitu itama ta fita, a tare suka jera suka nufi cikin Emergency ɗin. Ɓangaren Faisal kam tunda ya fita bai ƙara shiguwa ba sai cikin dare,yana shiga Faisal na buɗe idanunsa tare da zubasu a kan mahaifin nata,haka ya tabbatarwa da Papi tambayarsa yake game da Lili,zana yay tare da shafa kansa yace. "Kayi ta wakkali Faisal cikar imanin mutum shine yadda da ƙaddara,ka yarda Lubna bata raye kuma kowa na haka ne kaci gaba dayi mata addu'a itane abinda take buƙata indai ka yarda kana sonta Rabbi yasfika Allah ya baka lpa ka rungomi matarka ka ɗauki hakan matsayin ƙaddararka"murmushi kawai Faisal yay domin yasan babu wanda zai yarda dashi a kan Lilinsa bata mutu ba,bai taɓa son Najma ba haka kuma bai taɓa tsanarta ba hasalima tausayinta ya keji ganin bata da kowa amma ta zaɓi baƙanta rayuwarsa da kuma duniyarsa,ta zabi ha ɗashi da mahaifiyarsa har tayi mummunan Lafazi a kansa meye laifinsa kodan ya nuna ƙauna da soyayya wa ƙanwata kodan zuciyarsa taƙi yarda ta amsheta matsayin mata,yayi hakanne sbd bai son ya tafi yabarta da marayun yara dan yana tabbacin bazai taɓa tashi ba. Washe gari da safe Najma ta karasu asibitin tana tafe tana buɗa ƙafa dan sosai tasha wahala wajan Faisal ita yanzu haka maza tsoransu take,wajansa ta ƙarasu tare dajan kujera ta zauna lokacin ya samu bacci zuba masa ido tayi ganin ya ƙara mahaukacin kyau tare dayin wani fari fiye da jiya fuskarsa ta faɗaɗa ta yalwataccen murmushi,wata wutar sonsa ce ta ƙara tasu mata tana jin a duniya tafi kowa dacen mijin ɓangare guda kuma tana jin tsanar Lili fiyeda da,domin ita ta haddasa komai a kanta yaƙi amsarta a matsayin mata a kanta ta shiga damuwa. Ta daɗe a zaune har bacci ya ɗauketa a jikinsa,wata ƙarar na'oura ce ta farkar da ita daga bacci cikin tashin hankali ta miƙe ganin gudan jini na fita ta hancinsa da bakinsa hannunsa dafe da ƙirjinsa,jikinsa gaba ɗaya rawa yake,da gudu ta tayi waje domin kiran Dr tana ƙoƙarin fita suna ƙoƙarin shiguwa Ammi ce sai Papi sai kuma wani ƙyaƙƙyawam namiji a bayan kafin wata mai hijab ta biyo bayansa,cikin farin ciki Papi yac"indai Lubna ce damuwark daga yanzun ta kau,domin ga muradin ranka a gabanka" A hankali ya ware idanunsa tare da zare oxcygen dake bakinsa muryarsa na creating yace "Bby..boo"da gudu ta ƙarasu tare da faɗawa jikinsa ta saki wani mahaukacin kuka mai tsuma zuciya,kanta ya shiga shafawa tare da ɗura bakinsa saitin kunnan ta yace "i luv u more most"ya manna mata lafiyayyen kiss a wuyanta. Kallamar shadar da taji yana faɗa ne yasa tayi saurin ɗago kanta wani ƙawataccen murmushi ya sakar mata fuskarsa ta cika da fara'a kafin yaja idanunsa ya rufe tare da sakin hannunta,gaba ɗaya na'ourorin da suke cikin room ɗin suka shiga ƙara a lokaci ɗaya,kaita shiga girgizawa tare ƙanƙameshi tan faɗin "no pls no Faisal why zakai bacci a lokacin da nake muradin ganinka da son jin muryarka dan Allah ka tashi" Likitoci ne suka shigu da gudu tare dayin kansa suna zuwa suka shiga dubashi tare da girgiza kai wani Dr yace "saidai kuyi hqr Ubangijin daya samar dashi ya amshi abinsa kum... Ihun da Lili tayi shine ya dakatar dashi daga faɗin abinda yay niya kanta tayo ta shiga dukansa tare da faɗin"wlh ƙarya kake bai mutu kuma bazai taɓa mutuwa" cikin saurin Sufyan yazu ya ƙwace daga jikin likitan tare da mannata a jikinsa ya shiga jijjigata"dan Allah Sufyan kace bai mutu ubangiji kasa mafarki nake ba gsky ba"tana faɗin hakan tayi kan Faisal lokacin har an lullubesa da farin yadi,kafin ta ƙarasa taji saukar wani ƙarfe a tsakiyar kanta ƙara ta saki tare da juyawa da hannu ta shiga nuna Najma wacce take tsaye hannunta ɗauketa da wani ƙarfe cikin kuka Najma tace"wlh kema saikin bishi shegiya mayya aida lafiya muke zaune dashi Wlh nice aljalinki kamar yadda kika sani kuka nayi alƙawarin ganin bayanki"ƙara ɗaga ƙarfenta tayi zata ƙwaɗa mata a kai Sufyan yay saurin riƙewa tare da sauke mata wasu lafiyayyen mari,zafi da raɗaɗin ƙarfin dukan da taji ya sata yin baya lokacin jini ya gama wanke mata fuska nanta sulale ta faɗa jikin gawar Faisal babu numfashi.. _Wlh wlh wlh Allah kenan indai yau mutum sama da ashirin ba suyimin comments ba,kuma dukkan wanda yasan yana karantawa baiyi comments babu shakka zai koma na kuɗi duk nayi alƙwarin free ne amma naga baku da halin kai ina ƙoƙarin na ɗauke kai ni ban fiya kace nace balabu ɗaya nake faɗa,wlh duk wanda yake karantawa yau bai comment ba ya tabbatar kuɗinsa zai kuka domin ko biyar na rabaka da ita nadai rabaka da itan🤷🏻‍♀️shawara yana wajanku_. F@y@l _The secret issues_ *💖JUYAYI💖* *24-25* *_Wattpad_* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb or Nimcyluv *_Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ يايهاالذين ءامنوا اذكروا الله ذكرا كثيرا، وسبحوه بكرة وآصيلا. ......Cikin tashin hankali Sufyan yay kanta tare da ɓanɓareta daga jikin gawar Faisal,ɗaukanta yay tare da fitar da ita daga cikin room ɗin gaba ɗaya. Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana tabbas ko wanne bawan Allah saiya ɗanɗani cin mutuwa da raɗaɗinta haka da zafinta,kuma dukkan mai rai mamacine,Allah baya barin wani dan wani yaji daɗi a ko'in kake Ubangiji na iya ɗaukan ranka a duk lokacin daya gadama,Allah daya halicce mutum shike da ikon karɓan ransa saida wani yay sanadi. Papi duk dauriyarsa saida ya zubar da hawaye,a hakan ba ƙaramin ta waƙƙali yay ba domin Faisal yay mutuwa mai kyau mutuwar dako wanne bawa zaiso yay irinta,Ammi kuka tayi harda suma yayinda tsanar Lili ta dira acikin zuciyarta lkc guda tsanarta mai girma ta shiga ko wacce ƙofa ta jikinta,ta tabbatar da baƙin cikin Lilin ya mutu aida bai mutu ba saida tazu,da ƙyar aka samu kan Ammi,Najma kusan haukacewa tayi saida aka yi mata allurar bacci ta wajan 24hours,haka aka ɗauki gawar Faisal aka saka a ambulance suka nufi gida da ita,lokacin mutane sun cika cikin gaggawa aka shiga da Faisal tare dayi masa wankan gawa aka shirya yashi cikin lafiyayyen kayansa kaya na har abada kayan da ya zamewa ko dolen sashi a ranar da zaiyi kwanan ƙarshe a nan gidan duniya,ana gama shiryasa akai waje da gawarsa cikin makara. Sufyan na fita da Lili babu inda ya tsaya da ita sai wani specail room,aka shiga dubata tare ɗinke inda Najma taji mata ciwo,ganin ciwonta na Asma na shirin tashi yasa sukayi mata allura tare da ɗaura mata drip,ganinta samu baccine yasa Sufyan fita tare dayin harabar asibitin ya shiga motar ya nufi gidan da suka baru dan yana da tabbacin nanne gidan da akai rasuwar,tunda yake bai taɓa ganin mutuwa ido biyu wacce ta tsora tasa tare da ƙara masa ƙarfi imani ba irin mutuwar Faisal,sosai yake gudu harya isa unguwar Maiduguri road yana zuwa ana gama sallatarsa mutum biyu ne suka shiga motarsa cikin saurin suka rufawa motar gawar lokaci kaɗan suka isa maƙabartar,lkcn angama haƙa kabarinsa babba da uwar ɗaki,bisimillah akai tare da sakashi a ciki idan nan bai cika ba sai ɗebu ƙasa tare da dannawa cikin kabarin,daga ƙarshe aka ɓallo ƙatun reshan bishiya aka ciccika a cikin kamarin ana gamawa aka shiga zuba ƙasa saida aka gama sannan aka shiga yi masa addu'a tare da kafa allo aka rubuta. _Rest in peace_ _Faisal khalil cibaɗo_ _wed/jan/13_ Ana gamawa kuwa ya shiga mota aka barshi shi ɗaya daga shi sai halinsa,mutuwar Faisal ba ƙaramin girgiza Papi taima amma yay ta wakkali tare da rungumar ƙaddararsa,kuwa ya ganshi sai yaga ramar da yay ya faɗa lkc guda idanunsa yay zuru-zuru,ta'aziya Sufyan yay masa tare da bashi ƙaramin card ɗinsa mai ɗauke da adress haɗi da number waya sannan yay masu sallama a kan zaije ya ɗauki Lili su tafi Abuja kar dare yayi. Sufyan na shiga mota yay asibiti da gudu bai daɗe ba ya isa cikin asibitin,yana shiga daret babu inda ya nufa sai room ɗin da take ƙwance zuciyar cike da tsanar yayarta ta,ƙwance take flat tana sauke numfashi a hankali kana kallan fuskarta kasan bata cikin nutsuwarta musamman idan ka lura da yadda ta haɗe fuskar hawaye yay mata fata-fata a saman innocent face ɗinta,zama yay tare da kama hannunta ya ɗan murza ka ɗan tare da ranƙwafawa ya sakar mata sumba a gefen lips ɗinta cikin sanyin muryar yace. "Lovely bbyn am sorry bansan zaki tarar da ƙatuwar tashin hankalin nan ba daman kawo ki ba pls for give me ban ƙarawa..numfashi yaja tare da shafa gefen fuskarta yana mai jin wani iri a jiki tabbas da ace matarsa a yanzu babu abinda zai hanashi jin ɗumin jikinta,lumshe ido yay yana maijin wani abu a zuciyarsa mai kama da fargaba,ƙara kallonta yay yace"Lovely bby ina kishinki sosai da wannan mamacin amma bana fushi dashi domin shiɗin abin tausayi ne amma banjin zan iya hqr dake komai wahala komai daɗi dama yau igiyar aure ta shiga tsakanina dake da yau saikin tabbatar da zallar ƙaunar da nake maki ruhi da kuma gangar jikina,amma babu damuwa kamar yadda na jure sati huɗu haka zan jure sati ɗayan ban dama bikin waccan sakalya mai zaisa subar gari". Haka dai yayta surutu shi ɗaya kafin ya miƙe ya zare drip ɗin hannun ya saɓata a shoulder ɗinsa yay waje,yana zuwa ya buɗe side ɗin mai zaman banza tare da ƙwantar da kujerar ya ƙwantar da ita akai ya sakar mata wani lafiyayyar murmushi"yi baccinki bbyn zuciyanki na buƙatar hutu akwai lokacin da shayar dake zallar soyayyar zan maki madarar soyayyar da babu wani namiji dazai iya baki ita"gefen wuyanta ya shafa tare da rufe ƙofar ya koma side ɗin drever yaywa motar key tare dayin ribers ya figeta da wani irin speed yay waje yabar cikin asibiti yana fita ya harba motar kan titi sai Abuja. Basu isa Abuja ba sai dab da magrif ganin sun ƙarasu area ɗinsu ya shiga dreving a hankali harya kawo babban get ɗin gidan wani ƙyaƙƙyawan horn yay da sauri Getman yazu ya wangale masa get ɗin,hancin motar ya cilla cikin harabar gidan yana gama parking a parking space ya fitu daga cikin motar tare da ɗaukanta ya nufi cikin gida da sauri jin yadda jikinta ta ɗauki zafi. Da mamaki Momma ta tsaya tana kallonsa bakinta ɗauke da tambaya amma ta share,bedroom ya nufa tare da ƙwantar da ita har ya saka hannu zai cire hijab ɗin jikinta sai kuma ya fasa yaja mata duvet tare da ƙara gudun A.c'n yay waje. A nan parlon ya tarar da Momma ita da Yusrah sai haɗa kayan tafiya suke,daman Alhaji baya gari sai ana ƙwana ɗaya ɗaurin aure zai dawo,zama yay kusan Momma tare da ɗura kansa a kafaɗarta ba tare data kallesa ba tace "Meya faru?" kallonta yay da idanunsa da suka sauya kala sam baison tafiyar nan gani yake kamar akwai abinda zai faru,nan ya shiga labarta mata abinda ya faru,shuru tayi na wani lokaci sai kuma tace. "Allah sarki wannan bawan Allah tabbas naji wannan mutuwar Allah ya jiƙansa,daman aƙwai ƴan uwa masu irin wannan halin jin ƴar nan inda ta tunda murnar ganin ƴar uwarta amma ji abinda ta aikata mata dole a kira Dr yadu bata before mu huce gobe" Jinjina kai kawai Sufyan yayi kafin ya miƙe tare da shigewa bedroom ɗinsa,a daren aka kira Dr yadu bata inda ya tabbatar masu babu matsala amma sai zuciya gobe zata farka sbd tsoro da firgicin data shiga,sallama yay masu sannan ya huce abinsa. Yana fita Sufyan ya kalli Momma yace"amma mai yasa dole sai munyi tafiyar nan ina ganin a hqr kawai ayi auren a nan a bani matana" Harara ta watsa masa kafin tace"idan bakka so babu dole kana iya zama"tana faɗin hakan ta huce flat ɗinta,ya daɗe yana kallon Lili kafin ya sakar mata sumba tare da tsotsar laɓɓanta ya fice da sauri,flat ɗinsa ya huce shima yana shiga ya faɗa saman bed ɗinsa tare da lumshe ido hannu yasa ya shiga danna mararsa tare da shafawa jin yadda ta kumbura tare dayi masa zafi ya daɗe yana juyi kafin ciwon ya lafa masa ya shiga sauke numfashi a haka bacci ya ɗaukesa. *** *** A can Kano kuma bayan tafiyar Sufyan manyan mutane ne suka shiga zuwa wajan Papi ta'aziyya kowa da ƙyaƙƙyawar addu'a a bakinsa,babu abinda za'ace sai halinsa na gari ya bishi domin duk wanda yasan Faisal ansan mutumin ƙwarai ne hankali nutsuwa biyayya uwa uba riƙo da addininsa. Haka akai ta karɓar gaisuwa har dare yay Papi ya koma cikin gida,yana zuwa yay flat ɗin Ammi amma taƙi buɗewa yay yin duniya taƙi buɗe,rabuwa yay da ita sbd yasan condition ɗin da take ciki a yanzu babbar rigarsa ya cire tare da ƙwanciya akan duguwar sofa cikinsa ya shafa jin yana masa zafi da murɗawa sai lokacin rabosa da abinci tun jiya da safe shima tea kawai ya iya sha,tunanin Lili ne ya faɗu masa a zahirin gsky yana tausayinta domin baisan halin da zata shiga ba,batun Najma kam bai fiya damunsa sbd ba ƙaramin haushi ta bashi ba duk da yana jin tausayinta a cikin ransa domin baisan a wanne hali zata farka ba,a haka bacci ya ɗaukesa. Washe gari tun shida na safe Anty Kausar ta sauka sbd tun jiya jirginta ya tasu wajan baƙwai kuma Anty billy ta shigo tun daga waje ta fasa wani kuka mai rikitarwa suka ƙanƙame juna ita ƴar uwarta Anty kausar sosai suke kuka kamar ransu zai fita,da ƙyar Papi ya rarrashesu domin har sukai shuru kallonsu yay yace. "ya kamata kuje wajan matarsa can asibitin"Anty Kausar ce ta turo baki tare da faɗin. "Allah Papi ban zuwa sam ba taimin ba,ba zance ita ta kashemin ɗan uwa ba,amma tunda ya aureta Faisal baya da sukuni bashi da fara'a kullum cikin ƙunci da baƙin ciki yake,ko vedio call muke haka zai sakarmin kuka yin duniya amma bazai faɗan damuwar ba,Papi idan ba ita ba wake da alhaƙin saka Faisal damuwa" Ta ƙarasa faɗa tana faɗawa jikin Papi tare da sakin kuka dan gani dake tafi kowa jin mutuwar Faisal ɗin. Papi ya gama sanin ƴar tasa daka fiya dan haka yace Anty Billy ta shirya ta tafi babu musu ta ɗauki key tare da basket ɗin abinci tayi waje. Rumgome ƴar tasa yay tare da tapping ɗin bayanta ya shiga rarrashinta tare da nusar da ita yadda da ƙaddara da kuma hqr a kan hali da bawa ya tsinci kansa kuma mutuwa nakan kuwa yanzu Faisal addu'arsu kawai yake buƙata a haka ya samu ta shiga sauke ajjiyar zuciya. Anty few minutes da ƙarasa asibitin babu inda ta tsaya sai ɗakin da aka ƙwantar da Najma tana zuwa ta kanta ƙwance sai numfashi take saukewa hannunta ɗaure da drip,juyawa tayi tare da zama kan sofa ta gumi tayi domin sosai take tausayin matar yayan nata duniyar tunani ta lula a haka bacci ya ɗauketa sbd kukan data ƙwana ta nayi jiya. *** *** Tun asuba da suka farka basu koma ba sbd bakwai na safe jirginsu,Momma da kanta ta shirya Lili take ƙwance kamar gawa ta saka mata wata a baya mai blue black ta gyara mata gashin kanta tare da naɗa mata vail ɗin a bayar a kanta ta fesheta da turare,tana gamawa ta fice daman ardy ta gama shiryawa sun zuba kayansu a mota Sufyan kawai suke jira. Cike da ta ƙama yake tafiya harya ƙarasu inda Momma da Yusrah suke zaune gaisheda Momma yay Yusrah ta gaidashi,kallonsa Momma tayi tare da faɗin. "daman kai muke jira kaje ka ɗakko Lili kasa memu a mota kada ka tsaya sakalci". Kai kawai ya jinjina mata tare da nufar cikin bedroom ɗin yana shiga ya lumshe manyan idanunsa tare da buɗe hancinsa ya shiga shaƙar daddaɗan ƙamshin dake fita a cikin ɗakin,can tsakiyar bed idanu ya zuba mata ya daɗe yana kallonta harya ƙarasa wajanta sunkuyawa yay ya ɗauketa tare da matse a jikinsa ya shiga fitar da numfashi ji yake inama zai iya mai data jikinsa babu shakka da yay hakan sosai wutar sha'awarta ke barazana da numfashi da kuma ganggar jikinsa a dukkan lokacin daya haɗu da ita musamman sukai haɗu jiki da ƙyar yake iya jan numfashinsa tare da dai² ta nutsuwarsa,ƙara matseta yay tare da sunkuyawa tare da cafke lips ɗinta na ƙasa ya shiga tsosa,kasancewar bacci take bata san abinda yake aikatawa ba,ƙara shigewa jikinsa tayi ta shiga mamul² da lips ɗinsa sai haka yay kamar tana sucking lipa ɗinsa take,saurin cire bakinsa yay lokacin idanunsa ya kama sauya kala sosai yake fitar da numfashi mai zafi saida ya dai² nutsuwar dankar Momma ta gane kana ya saka kai ya fice daga cikin gidan. Tun daga nesa ta zuba masa idanu domin ganu abinda take tunani haɗe fuska tayi lokacin da tunaninta ya gama bata abinda zuciyarta ke rayawa,yana ƙarasuwa ta zabga masa harara tare da faɗin"sakalan banza Yusrah koma gaba ya miƙomin ita nan"haka akai badan ransa yasu ba ya ƙwantar da ita cinyar Momma sannan Yusrah ta shiga gaba shi kuma ya shiga mazaunin drever,key yaywa motar sannan ya cilla hancin motar waje,da sauri drever'nsu ya nemi napep yabi bayansu sb shine zai dawo da motar. Sun isa fitin tashi da jirgi take garin abuja lokacin har sun makara suna zuwa ana kiransu basu ɓata lokaci ba suka shiga cikin jirgin Momma da Yusrah suna ƙujerar tsakiya yayinda Faisal ke rumgome da Lili a ƙujerar baya,ya matseta a jikinsa tare da zare vail ɗin kanta ya tura hannunsa cikin sumar kanta yayinda ya sauke laɓɓansa a dugun wuyanta, a haka jirginsu ya lula sama. *** *** _Folato_ Ganin yadda ya birkici mata ne yasa ta tsaya da kukanta ta shiga shafa sumar kansa tare da karanta masa addu'ar samun sauƙi a cikin zuciya sun daɗe a haka kafin ta samu jarumtar yi masa mgn"Yarona kana son gayamin ɗan uwana kuma yayana baya yare,kana son gayamin nima na tabbata marainiya mara gata kamarka"ƙara shigewa jikinta yay yana lumshe idanunsa sosai maganganun ƙanwar Daddynsa keyi masa barazana a zuciyarsa sosai ya kejin zafi da raɗaɗin maganganunta amma ƙaddara ta riga fata dashi da ita babu yadda zasuyi da hukuncin ubangiji haka ya tsara masu dole su amshi jarrabawarsu hannu bibbiyu,ɗago kai yay a lokacin idan ka ganshi baza kace idanunsa sun zubar da hawaye ba sosai ya dai²ta nutsuwarsa ɗan ƙwaɓe fuska yay tare da faɗin. "Mamana amma wannan yarinyar fa?" Murmushi tayi tare da shafar sumar kansa tape. "laa yarona ya manta twins sister ɗinsa" ware manyan idanunsa yay tare da faɗin"what twins don't tell me suka dawo haka?" Dry tayi masa tace. "Yarona shekara nawa rabonka dasu tun muna nigeria bama kasan mundawo nan ba sai ƙaddara data kuma haɗamu" "kuma danta rainani shine za tace tana sona kamar wani sa'anta" Shuru kawai Mama tayi masa danza tafi kuwa farin ciki idan hakan ya faru,hannunsa da taji saman fuskarta shine ya dawo da ita daga tunaninta"Lili fa bata mutu ba Mama zuciyata ta kasa yarda sister bata raye inajin zafi da raɗaɗin rashin da ace tana kusa dani da zuciyata ta samu sauƙi daga ciwon da take min,Mamana bana iya bacci ban iya cin abinci ko hospital naje ban iya aiki banjin daɗin duniyar sam ina zan ganta wanne hali take ciki shine ban sani ba" Sassautar muryarta tayi tare da faɗin"idan bata raye tana ina,yana da ƙyau ka ɗauki ƙaddararka a matsayinka ma musulmi ka yarda Lubna bata yare" Runtsa idanunsa yay idan akwai abinda ya tsana bai huci a kira masa Lili da sunan matacciya ba tana raye tabbas tana numfashi a doran ƙasa kamar yadda shima yake numfashi. Haka ya ƙare yinin ranar wajan ƙanwar Mahaifin tasa wacce a yanzu yake mata kallan Mamynsa,tasha taɓararsa duk mutsi kaɗan zaice"Mamana"yana faɗin hakan zaija idanun ya rufe ruf,sai dare ya miƙe tare dayi mata sallama kamar baiso tafiya haka Fauwaz yaja hannunsa suka nufi flat ɗinsu. Jikin shirinsa na fita hospitan ya fitu wata gezner nace mai kalan skyblue tare da black coppet shoe mai ƙyau ko hula bai saka ba,sai sumar kansa da tayi luff tasha gyara sai sheƙi take idanunsa manne jikin farin glass,tun daga nesa zaka san yana tafe sbd wani daddaɗan turare daya saka mai sanya nutsuwa. A hankali yake takawa hannayensa ya zurasu jikin aljihun rigarsa compund ɗin gidan yabi ganin cars sun ƙara taɓe baki yay tare da sanya kansa cikin babban parlon gida bugawar da zuciyarsa tayi ne yasa shi runtsa idanunsa tare da saka hannu ya dafe saitin zuciyarsa a hankali ya ware jajayen laɓɓansa yace “MY SUNSHINE” mutsin daya jine ya sashi ware manyan idanunsa tare da saukesu a kan wani matashin sauri wanda kallo ɗaya yay masa ya fahimci yaro ne dan zai girme masa da wajan shekara uku zuwa huɗu,kallon 3min yay masa ya ɗauke kai,shikam matashin saurayin sosai ya shagala da kallon Fahad duk ƙyansa amma saida ya raina kansa da yaga Fahad baiwar ƙyau da kuma tsarin halittar da ubangiji ya bashi yake kallo ga wani ƙwarijini haɗi da haiba daya gani ƙwance saman fuskarsa uwa uba kuma annuri addinin musulunci daya gani a kan fuskar tasa. Afnerh dake tsaye tace"laa bro Fahad wannsan Sufyan kenan sunzu bikin Fannerh wanda za'a haɗa da nasa matarsama na ciki babu lpa" Tsaki yaja cikin wata murya mai sanyi da daɗi yace"talkative" yana faɗin hakan yaja tsaki tare da juyawa ya shiga mota ya jata d wani irin mauƙacin gudu yabar gidan gaba ɗaya. _wanda yay dai² ya sani gashi nan dai Readmore 4 ne,ƙyautatawar daza kuyimin shine comments da share_ F@y@l _The secret issues_ *💖JYY💖* *26-27* *_Wattpad_* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb or Nimcyluv *_Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ *SELF DU'A🌚👇🏻* ```Ya Allah ka yarda dani,kasoni kasa mala'ikunka su soni,kasanya mutanen kirki su soni,Allah ka rufamin asiri,kabani sa'ar rayuwa da mutuwa,ka samu rayuwata albarka..Allah ka kareni daga sharrin mutum..Aljan..da dabba,Allah na roƙeƙa ka karenu daga sharrin mai sharri da zargin mai zargi da munafunci mai munafurci da hassadar mai hassada,Allah kasa na gama da duniya lafiya Ubangiji ka sanyamin Albarka..``` Not edited🥱 ......Baki Sufyan ya saki tare da jinjina girman jin kai irinna Fahad ɗin,ata rihin rayuwarsa zai iya cewa bai taɓa ganin mutum mai ɗagawa da jijjida kai ba sai yanzu da Ubangiji ya haɗashi da Fahad haka kawai yaji bai masa ba,lkc guda yaji wani matsanancin kishinsa ya dirar maza a zuciya,basarwa yay tare da kallon Afnnerh yace "Muje ki tayani ɗakko kayan matana"washe baki tayi tare da kama hannunsa suka isa gaban wata ƙatuwar mota,bayan motar ya buɗe ya shiga sakko da kayan jiki saida ya gama ya rufe ya ɗibi manyan aƙwatinan ita kuma ta ɗauki ƙanana,yana gaba ta binsa a baya a haka suka ƙarasa cikin parlon,Momma da Mama ne zaune sai kuma Yusrah wacce take kusa da Fannerh,da sallama ya isa yana zuwa ya ajjiye aƙwatinan tare da zama a kan sofa mai ɗaukan mutum guda,Mamace ta amshe da faɗin "Sufyannu manyan yau dake bikin kane ai naganka a gidana ko,gaba ɗaya mantawa kake da gidan ƙanin wan mahaifin naka sbd kirki da yay maka yawa,na tabbatar a hanya ka haɗu da twins ba lallai kasan ka haɗa dangi dasu ba"ƴar dariya yay tare da cewa"yanzu Mama bagani ba and how many time I'm telling you ki daina kirana da wani Sufyanu haba haka nan kamar wani tsohu just say Sufyan shine abun wahala haba Mamana"dry gaba ɗaya sukai. Miƙewa yay tare da zubawa ƙofar bedroom da aka saka Lovely bbynsa a ciki kana ya girgiza kai yay flat ɗin da aka masa. yadda yake dreving cikin fusata tare dajan motar da gudu shi zai tabbatar maka baya cikin nutsuwarsa,why zuciyarsa zatai masa hk,mai yasa a kullum baya jikin nutsuwarsa da tunaninsa?. Ina zan ganki when zuciyana zai daina beating a kanki?. Idan akai da duba da shekarun baya da suka huce ba abin mamaki bane domin ta riga ta zama jinin jikinsa kamar yadda yake da tabbacin itama ya zama jinin jikinta. Motar ya ficika da ƙarfi lkcn da ƙyar yake buɗe idanunsa wanda suka gama yi masa nauyi. Wani ƙawataccen murmushi yay wanda ya ƙawata ƙyaƙƙyawar fuskarsa wacce take zagaye da yalwataccen saje baƙi siɗik zai ƙyalli yake. Tura hannunsa yay cikin tulin sumar ƙansa wacce take ƙwance luff saman kansa. A ƙaro na farko bayan rasuwar iyayensa yaji wata nutsuwa da kuma farin ciki sun saukar masa,bayace ga dalili ba domin shi kansa baisan dalilin hakan ba abu ɗaya ya sani he is in happiness. Lafiyayyun jayayen laɓɓansa ya wara cikin lion voice yace “MY SUNSHINE BBY”. Ƙira'ar sheik Sudais ya saka cikin suratul yaasin,ya shiga bin karatul cikin daddaɗar muryarsa ya nayi yana lumshe idanunsa a haka ya ƙarasu babban asibitin prvt hoptl dake unguwar Folato a garin paskitan. Parking yay a harabar asibitin tare da kashe ƙira'ar dake tashi fituwa yay daka ciki ganin yadda aka zuba masa idanune yasa shi tsuƙe fuska tare da sadda kansa ƙasa yana tafiya cikin nutsuwa. Wata nurse dake gefensa ita da wata mata tace. "wow Rabbi yaban irin wannan mijin a matsayin maɗin rayuwata komai nasa ya haɗu kalli yake tafiya kamar wani ɗawisu". Taɓe baki yay tare da taune lips ɗinsa a ransa yana mamakin mata masu irin wannan halin. Ganin bashi da wani tym ne yasa shi hucewa duba marasa lpa. Sosai ya duba marasa lafiyansa yana shirin fita wani Dr ya shigo da sauri tare da faɗin. "Dr Fahad pls wata zaka duba babu lpa" Numfashi yaja tare da faɗin"babu tym" Cikin sauri Dr ya ƙara faɗin"wlh she is critical condition Asmer ya takura mata" Jin cutar da yaji Dr ɗin ya faɗa ne yasa shi saurin kallonsa. Runtsa idanunsa ya runtse da ƙarfi cutar daya tsana ko sunnanta baison jin cutar data takura masa little sis ɗinsa yana jin tausayin duk mai irin cutar. "where is she?"...yana faɗa tare dayin gaba,cikin rawar murya Dr ɗin yace. "tana Emergency" Yadda zuciyarsa ke bugune yasa shi tsayawa daga ƙoƙarin shiga room ɗin. Dafe zuciyansa yay tare da faɗin"ya rabb" Yana faɗin hakan ya tura kansa cikin room ɗin,tun daga nesa ya kejin ɗaukewar numfashinta zai ƙoƙarin shaƙa mata inhela suke a baki. "oya waje"shine abinda ya samu damar faɗe cikin sauri suka fice,a nutse ya shiga mata taimaƙon gaggawa cikin iƙon Allah numfashinta ya fara dai²ta Oxygen ya saka mata tare da ɗaura mata drip ya zuba injection a ciki. Ganin komai yay nrml ya fice daga ɗakin lkc ya duba yaga 2 saura daɗan sauri ya shiga cikin toilet ya ɗaura alwala. Yana fituwa ya ɗauki key ɗin motarsa yay waje. Motar yaywa key tare da janta da gudu ya nufi masallacin juma'a. *SUFYAN POV* Yana shiga bedroom ɗinsa deret toilet ya nufa yana zuwa yay taken shower cikin sauri ya ɗaura alwala,bai jima ba yazu ya shirya cikin jallabiya ganin da sauran lokaci na zuwa masallaci,faɗawa kan bed yay tare dajan numfashi,rashin kulawar da Fahad yay masa sosai ya tsaya masa a rai,haka kawai ya kejin abin na damunsa"harni zai kalla ya watsar who is he"ya faɗa a zafafe tare da fiddo manyan idanunsa,ƙyaƙƙyawar fuskarsa wace take masa kama data Lovely bbynsa itace ta tsaya masa a rai,sosai fuskarsu ke yanayi data juna musamman eyes ball ɗinsu da yanayin yadda suke lumshe ƙawawan idanunsu,tsaki yay tare da faɗin "whatever dai she's beautiful more than him" ya ƙara jan tsakai na rashin dalili a haka bacci yay gaba dashi ba tare daya sani ba. Waje ne mai ƙƴan gaske musamman idan kayi duba da hasken glove ɗin dake bada difference colour masu ƙawatarwa,jama'ane gota ina duk inda ka juya su zaka gani sanye da fararen kaya tare da furanni a hannunsu,cikin farin ciki ya ƙarasa inda take zaune sanye da kaya na alfarma tayi kyau tare da haske kamar daran goma sha huɗu,yana zuwa ya saka hannunsa tare da miƙar da ita tsaye, murmushi ya saki tare da ƙoƙarin haɗata jikinsa fincigarta akai tare da ɗaukanta aka dannata cikin mota,ihu ya saki gannin yadda aka sace masa mata akan idanunsa a rana mafi muhimmanci a cikin ranakun rayuwarsa,kuka ya saki tare dayin jifa da dukkan abinda ya gani. Some hours ago wata ƙyaƙƙyawar mota tayi parking wani matashin magidan cine ya fitu kana ya buɗe ɗaya side ɗin wata matashiyar budurwa ta fitu cikin shiga mai kyau,da gudu ya miƙe daga durƙushen da yake,hannu yasa zai kamata tayi saurin daka masa wata mahaukaciyar tsawa,sbd yadda idanunsa suka rufe da ganin matarsa yasa sam baiji tsawar da tayi masa ta shigesa ba,saima ƙara tunkararta da yay,ƙaton cikin daya gani a jikinta ne ya sashi sakin wata mahaukaciyar ƙara. A firgice ya farka daga nannauyen baccin daya ɗaukesa gaba ɗaya jikinsa rawa ya firgita sosai da mafarkin da yay,wace wannan?waye ya ɗauketa?cikin waye?wannan shine tambayoyin dake ransa,sanin bashi dame bashi amsane ya miƙe jiki a sanyaye tare dayin toilet ruwa ya wasa tare da saka toilet a jikinsa,cikin sauri ya shirya tare da ɗaukan paryer mat da key ɗin motarsa da take ajjiye a gidan,yana fita ya yaga babu kuwa a parlo sai Mama,murmushi yay mata kana yace"Mama zanje masallaci amma zanga jikin matana"ɗan murmushi tai masa kafin tace"zamani kenan idan kuma aka fasa ita fa?..har kake wani Matana"saurin kallonta yayinda zuciyarsa ya bada sauti da ƙarfi kamar zai kuka yace"ayya Mama babu kyau irin wasanan fa,ita ɗin matana ce"yana faɗin hakan ya nufi ɗakinsu Afnerh ƙwance ya sameta sai sauke numfashi wahala ta faɗa sosai sai fari data ƙara,brest ɗinsa sun ƙarayin sama sam ba zakace tana halin ciwo ba,tsora mata idanunsa harya ƙarasu inda take ƙwance,gefen fuskarta ya shafa haɗi da riƙe hannunta yaɗan murza ya daɗe yana kallonta kafin ya shafi sumar kanta yay waje,yana fita ya nufi compound na gidan tare da shigewa mota ya nufi masallaci. Misalin 4 Sufyan ya dawo daga masallaci saida ya tsaya yay la'asar,a hankali yay parking tare da fituwa ya nufi cikin gidan kai tsaya,a gajiye yay sallama gaba ɗaya suka haɗa baki wajan amsa masa,babu wanda ya kula sai wajan daining area daya nufa yana zuwa yaja kujera plate yaja tare da buɗe wamer ya zuba dambun shinkafa wanda yaji zugale da kifi sai ƙamshi yake zabgawa,cikin sauri ya ɗauki spoon ya shiga cin dambun saida ya gama sannan ya miƙe tare da dawowa parlon dryar Yusrah ce ta ƙwance kafin tayi magana Mama tace"ashe yunwa ta rufe maka idanu ka kusa taƙen ƙafa" dry suka ƙara saki mai kula kuwa ba yaje ya zauna kusa da Afnerh wacce tayi shuru tare dayin ta gumi"wannan tagumin fa?kamar ance maki saurayinki ya fasa aurenki"turo baki tayi kana tace"haba bro wlh ina sonsa kar kayimin baki"kaiya dunguri mata yace"eyee waye haka yay dace yay wuff dake"murmushi tayi sai kuma ta ƙwaɓe fuska tace"i luv him wlh ina sonsa bansan yaya zanyi ba"harara ya cilla mata yace"kaji shirme da wane yace baki sonsa?"hawayen da take ɓuyewa ne ya samu damar sakko mata tace"baya sona bro Fahad ne wanda kuka gaisa ɗazu" zuba mata idanu yay ashe kam zaki mutu wannan mai ɗan banzan mai jida kan,a fili kuma yace"Allah ya kyauta"hannunsa ta riƙe tana goge hawayen idanunta tace"pls bro do something wlh ba kaji zuciyata ba" Allah ya ƙyauta bai shirya ɗaukan wulaƙanci ba ya faɗa a ransa,miƙewa yay tare da shige bedroom ɗinsa ganin magrib ya kawo kai. *FAHAD POV* Tunda ya fita daga asibitin yaje majid bai dawo gida ba sai bayan isha'i,yana shiga Fauwaz ya bishi da idanu yana jin tausayin abokin nasa yasan rabonsa da abinci tun safe indai ba cewa akai ya zauna yaci abinci ba bazai taɓa zama yaci ba,bai taɓa ganin mutun irinsa ba wanda bai damu da lafiyarsa ba,abune mai wahala kaji cikin Fahad ga ɗan banzan miskilanci saiku shafe zama tare ba zaice ƙala,idan aka damesa ma tashi yake yabar wajan,"lafiya dai ka kai wannan daren?"lumshe idanunsa yay tare da buɗewasu a kan Fauwaz kai kawai ya jinjina masa ya shige cikin bedroom,girgiza kai Fauwaz yay tare da faɗin"Allah ya ƙyauta" wayar Fannerh ya kira sbd yazu basa ganin juna wai ana mata gyaran jiki shikam wannan gyaran jikin ya cucesa tunda ya hanashi ganin wafy ɗinsa,sun daɗe suna shira kafin ya kashe wayar,da mamaki yake bin Fahad ganin har yay wanka ya sauya kaya yana latse² a p.c ɗinsa,"yause ka dawo?"banza yay masa yaci gaba da aikinsa shi kaɗai yasan mai yake a gobe ya ɗauki niyar zuwa garin yola tunaninsa acan ya manta takaddun da Dad ya basa,haushine ya kama Fauwaz yace"mutum shikenan fuska babu walwala babu farinci koda yaushe kana cikin ƙunci kamar kaika ɗurawa kanka damuwa wannan fa ba dai² bane bana jin daɗin yadda nake ganinka kullum,na ɗauka ganin Mama zai rage maka damuwa ashe ba haka bane"still bai ɗago ba kuma bai tanka saba,saida ya gama aikinsa sanna ya ajjiye komai ya ɗauki wayarsa yay waje,yana shirin ficewa sai kuma ya tsaya yace"tayaya farinci zai dauma a raina bayan babu silar farin cikin nawa"yana faɗin hakan ya fice daga cikin gidan deret get ɗin gidansu Mama ya nufa daga shi sai wando 3gauter sai black ɗin riga mai ƙaramin hannu hakan ya sanadiyar fituwar murɗaɗdiyar damtsen hannunsa tare da bayyanar faffaɗan ƙirjinsa har tsinin nipples ɗinsa ana gani sbd yadda rigan ya kamasa,hannunsa sake cikin aljihun wandonsa a haka yake typing cikin takunsa wansa yake nuna shiɗin lafiyayyen namijine mai taƙama da ƙyan halittar da bayyawar surar da ubangiji ya bashi haɗi da ƙwarjini,a haka ya isa ƙofar da zata kaisa babban parlo lumshe idanunsa yay haɗi da taune lips ɗinsa kansa ne ya sara sosai jiyaye kamar ya juya sai kuma ya tuna yau gaba ɗaya baiga Mamansa ba,a hankali ya murɗa handle ƙofar tare da turawa ya danna kansa ciki bakinsa ɗauke da sallama. Gaba ɗaya suka juyo suna kallonsa har Sufyan dake zaune saman sofa yana waya,tsaki yaja mai tsauti a ransa yana faɗin "Mayu"yana faɗin hakan yay wajan Mama yana zuwa ya zauna kusanta tare da shigewa jikinta cikin sassayan muryarsa mai daɗi yace"Mamana nayi missed naki"kansa ta shafa tace"na ɗauka nayi laifine ai,yanzu nake shirin kiranka"lumshe gajiyayyun idanunsa yay tare da ƙara lafewa a jikinta,cikinsa ta shafa taji wayan ya lafe kamar zai haɗe da bayansa tayi sauri faɗin"Yarona mai yasa bakkason cin abinci?"Fannerh ta kalla tace"maza ɗauki plate ki cikomin shi da abinci tare da ruwa da kuma juice"Afnerh ce tayi saurin miƙewa bata daɗe ba ta dawo hannunta ɗauke da plate ta cikoshi da dambun cuscus yaji kayan lambu da bushasshan kifi sai ƙamshi yake. spoon ta ɗauka zata kai bakinsa yay saurin riƙewa murmushi tayi ta ajjiye spoon tare dayin bisimillah tasa hannunsa a haka ya fara cin abinci wanda duk rabi sakalcine. Baki Sufyan ya saki ganin sangarta ido biyi ko Yusrah ba zatai wannan taɓarar ba,amma ƙato dashi wajan shekara sama da talatin ya zauna yana wannan shagwaɓar ransa ne ya ƙara ɓaci ya shiga ja tsaki,ƴan matan kam gaba ɗaya idanu suka zuba masa musamman Afnerh da Yusrah wanda komai nasa yake tafiya da tunaninsu haɗi da zuciyoyinsu. Sarai Fahad ya lura da yadda Sufyan yake ja masa tsaki amma shiko a jikinsa,da ƙyar Mama ta samu yaci rabin plate ɗin tare da shan gorar ruwa lemon kam cewa yay a'a,ƙara rungometa yay ya sakar mata sumba a kumatu yay saurin miƙewa jin kansa na sara masa ga yadda gudun zuciyarsa daya ƙaru,yana gab da ficewa daga cikin ɗakin yaji an saki wata mahaukaciyar ƙara daga cikin wani ɗaki,kamar an haɗa baki shida Sufyan suka zura da gudu cikin ɗakin har suna gware. Sorry for the short typing am not ok. F@y@l. _The secret issues_ *💖JYY💖* *28-29* *_Wattpad_* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb or Nimcyluv *_Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ ```About the Night``` Not edited آللحمدالله ....Gudu suke har suka ƙarasa bakin ƙofar dasu an saki ƙara a cikinta,kansa ne ya sara da ƙarfi ya hakan ya bashi damar zubewa a wajan yay saurin dafe kansa tare da faɗin dukkan addu'ar da tazu bakinsa,yayinda ɓangare guda na zuciyarsa ya shiga beating very past hakan ya sanya ya ƙara durƙushewa a wajan tare da sakin wani wahalallan numfashi mai zafin gaske,ganin hakan ya sanya Sufyan sallake Fahad yay saurin faɗawa cikin ɗakin,abun mamakin tana ƙwance sambal a tsakin rayal bed ɗin idanunta na zubawar da hawaye yayinda ƙirjinta ke ɗagawa kamar zai fashe gida biyu,yadda take numfashi daɗan fisge² shi kaɗai zai tabbatar maka bata cikin nutsuwarta,duk da sanyin daɗin bai hana gumi zubu mata gaba ɗaya ta kiɗime ta fita hayyacinta,banda kanta da take fisgewa sai kuma bakinta dake rawa da alama tana son furta wani abu amma ta gagara,idan ka ɗauke waɗannan babu wani abu dake mutsi jikinta,ganin yadda take abu kamar zautacciya ya sanya shi hawa gadon tare da nufuwar inda take ƙwance. Mama da take tsaye tana kallon Fahad tare da mamakin abinda ya samesa lkc ɗaya,cikin sanyin jiki ta ƙarasa wajansa tare da durƙusawa kusansa,kansa ta shafa tare da faɗin"Yarona mene yasa ka shiga wannan halin?"jikinta ya faɗa tare da ƙanƙameta gaba ɗaya jikinsa rawa yake jijiyuyin kansa su fitu sunyi raɗa² saman forehead ɗinsa,ganin kamar baya hayyacinsa yasa Mama fara tofa masa addu'a tare da bubbuga bayansa alamar rarrashi,ƙara matseta yay har sai data runtse idanunta,kansa ya ɗago ya zuba Mama tsumammun firgitattun idanunsa kansa ta shafa tace"Yarona"sharr wasu wahalallun siraran hawaye suka shiga zuba ta cikin idanunsa bakinsa na fara yace "Mamana zuciyata bugawa take ina jin zafi da raɗaɗi a heart ɗina tana beating tana tafiya da dukkan numfashi da tunanina haɗi da farin cikina"fuskarsa ta ƙara shafa jikin sanyin jiki tace"Yarona babu abinda yafi ƙarfin Ubangiji sai dai ba'a ruƙesa ba,ka miƙa lamarinka zuwa mahaliccinka tabbas sai shige maka gaba kuma zai zam gatanka,ka daina saka kanka cikin damuwa sbd bata magani,tabbas da ace damuwa nayin magani da tuni nima tayimin maganin abinda ke raina kayarda da ƙaddara ka ɗauki ta wakkali za kaji daɗi insha komai zai huce"numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa a ƙaro na biyu hawayen da yake ɓuyewa suka ƙara zubuwa daga cikin idanunsa,mai yasa ya bari rauninsa suka bayyana har haka?mai yasa ya kasa riƙe damuwar dake ransa?dole yay hankali ya shiga nutsuwarsa sbd lukutin yaƙine babba a gabansa idan har zai bari rauninsa ya bayyana mutane su fahimci damuwarsa,nauyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke a fili kuma ya fahimci Mama yace"tayaya zan samu sauƙi da sukuni a cikin zuciyata?tayaya damuwa zata bar zuciyata alhalin ita ta cancanta dani,Mama niɗin ban cika Ɗa ba,na kasa riƙe amanar da aka bani na zabi tsiratar da raina fiye dana Amanata,an yarda dani nayi ha'inci Mama bansan ina take ba,bansan inda zan ganta ba,zuciyata kullum na kukan rashin Amanata ina take?ina taje? Shine abinda yafi tsayamin,a ƙaru na biyu nacin Amana na yarda da wata Amanar Mama bansan ina nayar ba,bansan inda zai nemu wannan takaddun ba,tabbas suna da muhimmanci tunda Daddy da kansa shine ya bani na kula da ita tamkar yadda zan kula da cikina,a kullum nazu cin abinci wannan kalaman sukemin yawu cikin kunena na kasa mantasu"tsagaitawa yay da maganar lkcn da kuka yaci ƙarfinsa Allah yasa babu kuwa cikin parlon duk sun shige bedroom ɗinsu,rumgumesa tayi sosai tana sauraran yadda zuciyansa take ɗagawa,sumar kansa ta shiga shafawa tare da bubbuga bayansa sun ɗauki lkc mai ɗan tsayi kafin taji saukar numfashinsa mai zafi saman wuyanta,sai yanzu ta samu damar zubu da nata hawayen bashi kaɗai yay rashi ba,ita kanta tayi rashin babban yayan nata shi kaɗai take da shine jigunta shine bangun da take jin gina taji daɗi amma yau an wayi gari ta rasashi ta hanyar wasu mugwayen mutanan wanda suka nuna rashin imani a garesa da kuma iyalansa,sosai numfashin da yake fitawr cikin hancinsa ke dukan wuyansa gashi yay mata nauyi haka taci gaba da zama dashi a jikinta. Sufyan na ƙarasa hawa saman bed ɗin ya zuba mata idanunsa yana jin matsanancin sonta komai nata birgesa yake shikam ace zai ratsa ai baisan yaya zaiyi ba,babu shakka zai iya saceta ya ɗirka mata ƙaton ciki,idan kayi duba da halayen Sufyan zaka tabbatar mayan matane kuma yasan mace shiyasa tunda ya ɗura idanunsa a kanta lkcn da ƙaddara ta haɗasu yaji babu abinda yake buri da fata irinta,gaba ɗaya ya watsar da batun iskanci soyayyar gsky yake mata,da ace iya sha'awace da tuni ya cimma burinsa a wajanta amma haka yake hqr kullum da matsanancin sha'awarta yake ƙwana yake tashi,ganin yadda take karkarwa ya sashi saurin ƙarasawa wajanta tare dakai hannu zai ta ɓata tayi saurin zillewa tare da buɗe manyan dara-daran idanunta,shuru tai masa tare da kafesa da manyan idanunta,sosai ta fita daga hayyacinta sai kuma ta fashe da kuka tare da faɗawa saman bed ɗin ta shiga birgima tare da buga kanta a fuskar bed ɗin,ƙara matsawa yay kusanta cikin tashin hankali ya kai hannunsa ya jawota cikinsa tare da matseta,jin jikin nasa take kamar wuta ga wani ƙunci da baƙin cikin dake ƙwance a zuciyarta,gaba ɗaya haushi ta keji musamman lkcn data fahimci ba a wajan Faisal ɗinta take ba,ganin ba zata iya ƙwatar kanta yasa ta fashe da kuka tare dakai masa duka,bai kula ta ba,saima rarrashinta da yake ɗan sunkuyar da kansa yay zuwa fuskarta tare da zubawa peach lips ɗinta idanu,bai san lkcn daya sanya bakinsa cikin nata ba,saukar bakinsa cikin nata yay dai² da ƙara jin wata zafaffiyar tsanarsa a zuciyarta,hawaye ne kawai ke fita cikin idanunta jin yana ƙoƙarin tura halshensa cikin bakinta tayi saurin sakar masa cizu,zafi da raɗaɗin da yaji ya saukar masa saman tongue ɗinsa ne ya sashi saurin sakinta ya shiga sauke numfashi,tunanine fal cikin ransa gefe guda kuma ƙarfin sha'awarta gaf take da tarwatsa masa mararsa miƙewa yay tare da ficewa daga cikin bedroom ɗin ya barta ƙwance tana kuka. Yana fita ya tarar da Mama zaune a saman carpet jikinta ɗauke da Fahad tsaki yaja dan gaba ɗaya haushinsa ya keji haka nan,duk lkcn daya ganshi sai gabansa ya faɗi,murmushi Mama tayi masa tare da faɗin "yawwa Sufyanu ta yani ƙwantar da wannan shagwaɓaɓɓan pls"kawai ya jinjina mata dan baison yi mata musu,ƙwantar dashi suka nan Mama tayi masa yamai jiki kasancewar haryau bata ga yarinyar ba,"da sauƙi"ya mata a amsa tare da shigewa bedroom ɗin da aka bashi,remote ta ɗauka tare da ƙaru gudun A.C sannan ta rufe ƙofar parlon kansa ta shafa tare dayi masa addu'a ta shafa masa,flat ɗinta ta huce sbd wani bacci daya cika idanunta,tana shiga tayi wanka tare da ɗaura alwala ta shirya cikin kayan bacci ta ƙwanta tare da kashe glove ta daja duvet ta lulluɓe jikinta. Bayan fitar Sufya sosai Lili tayi kuka harta gaji fillow taja ta rungome a haka tai bacci bakinta ɗauke da sunan “Booby” Ɓangaren Sufyan rai ɓace ya shiga bedroom ɗinsa yana zuwa ya shiga fatali da dukkan abinda ya gani saida yay kaca² da komai sannan ya zube bisa gadon tare da dafe kansa,why komai nasu ya zamu ɗaya rainin hankali rashin son magana sangarta jijjida kai,hatta smooth skin ɗinsa iri ɗaya ne dana lovely bbynsa her eyes the same her eyes,mene hakan ko ƴan uwan junane suɗin?gaba ɗaya hankalinsa bai ƙwanta da zaman gidan ba,kamar yadda hankalin bbynsa da baya ƙwance yana jin someting bad gonna happen to his hrt,ya daɗe yana tunani a ransa kafin ya yanke shawarar da yake ganin ba dai² ce,da wannan tunanin ya miƙe tare da shigewa cikin toilet ya watsa ruwa yana fituwa ya shirya cikin rigar baccinsa yay ƙwace sai juyi yake saman bed ɗin yana ji kamar yaje ya ɗaukota su ƙwanta tare koya rage zafin abinda ya keji haka yayta tunani a ransa daga ƙarashe bacci ɓarawo yay gaba dashi. Misalin 2:30 na dare ta shiga buɗe nauyayyen idanunta da yay mata nauyi tare da ɗan dafe kanta,har zuwa yanzu numfashinta ba dai² yake fita ba hakan yasa ƙirjinta yake ɗagawa,a hankali ta saka hannunta tare da dafe cikinta jin yana ƙarar yunwa ya mutsa fuska tayi tare da miƙewa tana mamakin yadda zuciyarta ke bugawa da ƙarfi sosai yayinda ko wanne bugu baya fita saida tunaninsa,dukkan wata gaɓa ta jikinta baya iya wani ƙwaƙƙwara mutsi saida tunaninsa,ɗan murmushi ta saki tare da matsa ƙirjinta tace “My beautiful boo„ zame vail ɗin kanta tayi tare da bin jikinta da kallo ganin yadda aka sauya mata ƙaya zuwa na bacci,wando da riga ne kalan skyblue wandon riya laps ɗinta sai kuma rigar data sakko zuwa waist ɗinta kasancewar rigar ƙaramin hannune da ita hakan ya bawa ƙyaƙƙywan hannunta fituwa mai cike da gargasa,gashin kanta ta gyara tare da fice daga ɗakin domin samawa kanta abin sha. Juyi yake saman bed ɗin tare da fitar da numfashi hannunsa dafe da cikinsa dake murɗawa,tunda yaje ya sauya mata kaya shikenan hankalinsa ya tashi wata wutar so da kuma sha'awarta suka ƙara nunkuwa cikin zuciyarsa da gaggar jikinsa shi kaɗai yasan abinda ya keji a cikin wannan daren,daren da komai nasa ya kunce miƙewa yay tare da ɗaukan wayarsa ya shiga yiwa Alhajinsa DM ta email ɗinsa yana gamawa ya shige toilet tare da haɗa ruwa mai zafi ya shiga cikin Jakuzzie ɗin yana shiga ya fara yiwa kansa taimaƙon gaggawa ta hanyar yiwa kansa messges lkcn daya samu nutsuwa yaɗan saki wata ƙara mara sauti ya shiga fitar da numfashi. A hankali take tafiya harta kawo ƙofar shiguwa cikin parlon ɗan duhun data ganine ya sata tsaya tare da tunanin inda za taga maƙunnin fitulin parlon,ci gaba tayi da tafiya harta kawo tsakiyar parlon a lkcn ne kuma bugun zuciyarta ya ƙara ƙaruwa fiyeda da,ƙarfta da tayi mata nauyi ta ɗaga tare da sauketa a kan wata tattausar fata,zafin daya ɗan ratsane ya sashi mutsa ƙafarsa kaɗan ba tare daya ɗauke ba,lumshe idanunsa yay tare da taune lips ɗinsa yana mamakin wacce ta fitu a cikin wannan daren shafa zagayeyyen sajen dake fuskarsa yay haɗi da gyara zamansa,janye ƙafarta tayi cike da tsoro saida ta saita nutsuwarta sannan ta ƙara ɗagarta da niyar yin gaba cikin rashin sa'a tayi tuntuɓe da ƙafarsa tare da faɗawa jikinsa,lkc ɗaya suka saki nauyayyiyar ajjiyar zuciya,a lkcn ne zuciyoyinsa suka shiga halbawa a tare,baki ta buɗe zata saki ƙara yay saurin sanya jajayen laɓɓansa cikin bakinta.. _he wattpad idan naga comment da vote da yawa zanyi posting da safe wannan alƙawari nane,pls kuna share ɗin link ɗin pls Anty🥰_ F@y@l _The secret issues_ *💖JYY💖* *30-31* *_Wattpad_* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb *_Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ #Flash back Not edited .....Wani shock ne ya kamata lkcn da laɓɓansa suka haɗu da nata,wani irin sayi da daɗine ya shiga ratsa zuciyoyinsu yayinda lkcn guda wutar kansu ya ɗauke suka shiga fitar da numfashi mai zafi,a lkcn gudu dukkan wasu damuwa dake ƙwancce cikin zuciyar ko wannansu takau,Fahad bada wata manufa ya ɗura laɓɓansa saman nata ba,saidai baison ihu da surutu sbd yadda kansa yake barazanar tarwatsewa gida biyu,a hankali ya zare bakinsa daga cikin nata hannu yasa ya dafe kansa dake ɗan halbawa tym to tym,samun kansa yay da jawota cikinsa tare da ɗura kansa a saitin ƙirjinsa dake bugawa da sauri,wata nutsuwa ce ta saukar mata wacce ta daɗe bata samu irinta ba,bata damu da waye ba ta ƙara shigewa jikinsa tare da ƙwantar da kanta saman faffaɗan ƙirjinsa tana sauraran yadda zuciyarsa ke bugawa very past,sun ɗauki lkcn a haka ta farajin zazzafan numfashinsa yana saukar saman wuyanta lumshe ido tayi tare da taune peach lips ɗinta cikin nutsuwa da ƙwanciyar hankali ta ware laɓɓanta cikin zazzaƙar muryarta tace"Boobyna ka tafi ka barni"ta faɗa cikin muryar kuka mai kama da sangarta sai kuma wasu hawaye suka zubu daga cikin sleepyn eyes ɗinta,cikin baccinsa wanda ya daɗe baiyi irinsa ba,yaji sautin siririyar muryarta ta kirashi da sunan da yay missed ɗinsa sunan da ya daɗe yana muradin son yaji wannan sunan,sanin babu wanda zai taɓa gaya masa wannan sunan idan ba lovely sister ɗinsa ba shiyasa ya hqr amma koda yaushe sunan yana manne cikin zuciyarsa, ɗan tsaki yaja a fili yasa hannu zai zareta daga jikinsa tayi saurin maƙalesa tana shassheƙar kuka,taɓe baki yay yaɗan saka yana ya bubbuga bayansa,jikinsa ne ya ɗauki sanyi ya farajin duniyar na juya masa few minutes idanunsa suka sauya daga fari zuwa jaa,cikin sauri ya hankaɗeta daga jikinsa ta faɗi ƙasa a daddafe ya nemi ƙofar parlon ya buɗe ya fice daga ciki,sosai ta bugu da jikin kujerar amma hakan baisa ta miƙe ta bi bayansa ba,tana gaf da ficewa taji yaja ƙofar da ƙarfi tare da rufewa,ƙofar ta shiga duka tare da kiran sunan “Booby” ganin yaƙi buɗewa ne yasa ta zube a ƙofar tare da durƙushe ta shiga rera kukanta kamar ranta zai fita. Gwaggwaran numfashi Sufyan yaja duk yadda yakai da ɓuye abinda ya keji ya gagara,ya daɗe a tsaye a parlon har lkcn da Fahad ya buɗe ƙofa ya fita duk akan idanunsa,runtsa idanunsa yay da ƙarfi sbd yadda zuciyarsa ke ta fasa,Meye haɗinta dashi? Me suka aikata? Meyasa take danya yafi ya barta?..wanna sune tarin tambayoyin da suke ƙwance a ƙasan zuciyarsa tamboyin da rashin amshoshinsu dai² yake da bugawar zuciyarsa,wani matsanancin kishin Fahad ne ya dirar masa a zuciya,fesar da numfashi yay tare da takawa zuwa wajanta,ya daɗe a tsaye a kanta kafin ya durƙusa dai² da ita har suna iya jiyu hucin numfashin juna a sanyaye yasa hannunsa tare tallafu haɓarta,runtsa idanunta tayi domin bata son tabbatar da abinda take zargi,sam bata son ganin Sufyan bata sonsa babban tashin hankalin ba zata iya cewa bata sonsa ba domin haka babban butulcine,yaya za tayi tayi imani da Allah auren Sufyan dai² yake da rasa nata ran,amma bata da wani zaɓi wanda ya huce zama dashi tayi masa biyayya tunda ita ɗin ba kowa bace face bara gata wacce ta rasa komai nata,zata zauna dashi har lkcn da numfashinta zai tsaya zata zauna dashi domin saka masa da alkairin da yay mata,ƙara runtsa idanunta tayi tare da saurin tashi jin yana ƙoƙarin jawota zuwa jikinsa,kanta ta shiga girgizawa tare daja baya ganin yana ƙara matsuwa gareta yasa ta ƙwasa da gudu ta nufi ɗakin data fitu tana shiga ta murza key tare da faɗawa saman bed ta shiga rusa kuka,ganin kukan baya da magani yasa ta miƙe tare da ɗauro alwala ta shiga gabatar da lafilfili,ta daɗe ƙafin a kira assalatu miƙewa tayi ta gabatar da Raka'atul fijir tana idarwa ta gabatar da sallah asuba ta daɗe tana addu'a tare da neman sauƙi wajan ubanhiji sosai ta yiwa Faisal addu'a harda kukanta, “Allah sarki Anty Najma ubangiji ya baki hqr da dangana ki yafemin da ace nasan zuwana zaisa maki baƙin ciki a ranki da banzu ba,nasan cewa tashin hankali ne ya saki yin haka,ki yafemin Sisina ina kewarki kene kawai kika ragemin kene nake tunawa dake naji daɗi,Allah sarki mutuwa mai yankan ƙauna ta ɗauken iyayene mafi suyuwa a gareni,ta rabani da farin cikina mijin ƴar uwata,ta nisan tani da bugun zuciyata yaushe ne zaka dawo gareni yaushe ne zanganka ina roƙan Allah ya haɗani dakai kafin ɗaukewar numfashi na” kuka ne yaci ƙarfinta ta ƙwanta saman paryer mat ɗin ta shiga rera abinta a haka har wani wahalallan bacci ya ɗauketa wanda bata shirya masa ba. Zubewa Sufyan yay kan sofa tare da dafe kansa dake juya masa,murmushin takaici kawai ya saki dan yana tunanin haryau mutuwar Faisal ce ke damunta,ya daɗe a wajan kafin ya miƙe ya shig bedroom ɗinsa yana zuwa ya shige cikin toilte tare dayin wanka yay alwala ya nufi masallaci,a can suka haɗu da Fahad da Fauwaz,banda kallon Fahad da yake yana zabga harara babu abinda yake yayinda Fahad ko inuwar Sufyan bata ishesa kallo ba yana zaune yana lazibi har aka tada sallah,Ana idarwa ya miƙe yay gida bai jira komai ba ya nufi ɗakin da Lili da ƙwana still yana rufe ya daɗe yana bugawa amma bata buɗe ba haka ya gaji ya nufi nasa ɗakin,bacci ne sosai a idanunsa hakan yasa yana shiga faɗa kan bed lkc kaɗai bacci yay gaba dashi. Misalin 9na safe ta shiga buɗe manyan gajiyayyun idanunta da sukai mata nauyi sbd kukan da tayi a hankali ta shiga karantu addu'ar tashi daga bacci tana gamawa ta miƙe tare dayin toilet ruwan zafi ta haɗa ta gasa jikinta sosai tare da wanke gashin kanta,brush tayi kana ta ɗaura light blue ɗin towel ta fitu,busar da gashin kanta ta fara sannan ta shiga gugawa fatar jikinta lotion mai ƙamshi,tana gamawa ta fesa body spray sannan ta nufi inda taga aƙwatin kayanta buɗewa tayi ta ɗauko wata milk ɗin abaya mai ƙyan gaske ta saka tare da yana mayafin a bayar saman sumar kanta wacce taci gyara ta ƙwanta luff sai sheƙi take,jin tana jin yunwa yasa ta miƙe tare da nufar ƙofa. Can parlour Mama ce da Momma a zaune sai Yusrah wacce take chart a wayarta"Afnerh go and call Fannerh don't forget to tell her mai gyaran jiki tazu ta shirya kafin a gama mata matar Sufyanu ta fitu" miƙewa Afnerh tayi tare dayin bedroom ɗin da suka ƙwana,Sufyan ne ya ƙarasu parlour tare da zama ya gaida Momma sai kuma matar wan Babansa,hira suka ɗan taɓa kafin yace Yusrah ta haɗu masa break fast ya kaiwa Lili dan yaga an buɗe ƙofar,ƙamshin daddaɗan turarensa ne ya karaɗe parlour tun kafin ya shigo ciki,sanye yake blak ɗin boyal wanda akaiwa aiki da red ɗin yadi ba ƙaramin kyau yay masa sbd yadda baƙin boyal ɗin ya amshi farar fatar jikinsa,ya manna farin glass a idanunsa sumar kansa sai ƙyalli take kana ganinta kasan tasha gyara,fuskarsa babu yabu babu fallasa,cikin takunsa na isa da kuma ji da izza wanda ke nuna shiɗin lafiyayyen namiji ne mai jini a jika,cikin hadaɗɗiyar muryarsa yay sallama tare da ƙarasawa kujerar da Mama take ta durƙusa gabanta tare da langwaɓar dakai gefe yace "mrng Mamana" shafa kansa tayi tace "mrng too Yarona"kallon Momma yay ya gaisheta kana ya ɗauke kansa tare da maidashi wajan Mama yace"Asamin Albarka Mamana zani Yola"murmushi ta ƙarayi tace"Koda yaushe cikin sa maka albarka nake Yarona ubangiji ya baka abinda kakeso Allah ya rabaka da sharrin maƙiyya ubangiji ya haneka da son abinda ba zaka samu ba Allah yay maka albarka fiye da tubanka"ta faɗa tana shafa kansa,miƙewa yay yana shirin tafiya tace"Amma zaka dawo before bikin ko?"lumshe idanu yay yace"i'm not sure".."ok ya kamata kaga Matar ɗan uwan naka ai" ƙwabe fuska yay kamar zai kuka yace"no Mamana Allah ya sanya Alkairi bikin naga soon me baifi 5days yay raguwa soni zanyi 1week" jinjina kai tayi kana tace"Allah yay jagora Yarona"lumshe ido yay tare jinjina kai ya zubawa ƙofar side ɗinsa idanu wacce yaji ana ƙoƙarin buɗewa an kasa,ƙafa ya ɗaga zai ƙarasa wajan ƙofar yaji taku a bayansa baki ya taɓe tare dayin gefe ya bawa Sufyan waje wanda yake ɗauke da plate ɗin break fast,sallama yaywa Mama tare da ficewa dan 10:30 jirginsa zai ɗaga. Ta daɗe tsaye bakin ƙofar tana ƙoƙarin buɗewa ta kasa sbd gefen rigarta daya shige,tana gama gyarawa yana turo ƙofar ɓata fuska tayi tare daja baya,ganin tana ƙoƙarin fita kuma yasan Fahad na parlour yay saurin riƙeta tare da rufe ƙofar,nuni yay mata da break fast ɗinta haɗa rai tayi tare da zama ta suma ci hankali ƙwance amma duk wani abinda da take hankalinta na waje,fahimtar hakan da yay ya sanya ya murza key tare da neman waje ya zauna nesa da ita. Fahad na fita ya waje inda Fauwaz yake jiransa babu jimawa ya shiga mota suka nufi airport,wajan 10min ya kawosu lkcn har pasinger sun fara shiga sallama yaywa Fauwaz sannan yaja trolly ɗinsa yay ciki saida ya gama komai sannan ya shiga cikin jirgin can nesa da jama'a ya zauna tare da kashe wayoyinsa ya fiddo mujallar ranar ya shiga karantawa,sanarwa akai kuwa ya ɗaura belt ɗinsa,ɗaurawa yay kana ya jingina bayansa da jikin kujerar tare da lumshe idanun ya luula duniyar tunani kamar yadda jirginsu ya fara luulawa saman gajimare. Haka ta dunga tura abincin badan yana mata daɗi ba sai dan yunwar data keji,duk abinda take yana kallonta yana mamakin sauyawar data yi masa,"Lovely bbyn idan baki sona a hqr da auren" kallonsa tayi kamar ba zatai mgn ba sai kuma tace"idan ban aureka ba, na auri wa kaika taimakeni a lkcn dana rasa komai nawa kaine ka kula dani a lkcn dana rasa mai kula dani,kaine ka bani gata a lkcn dana rasa nawa gatan,bayan wannan ɗumbin taimako da kayemin har ka nemi aure na kake tunanin zan iya fasa aurenka Sufyan"ɗan waro idanu yay dan yaune ranar data fara kiran sunansa a hankali ya nanata sunan cikin ransa “Sufyan” babu ko ɗan karawa,a zahiri kuma ya basar yace"ok wane na ganki dashi ɗazu?"ka faɗa ta ɗaga alamar na sani,gyara zama yay yace"Lubna yaya akai kika kuɓuta daga gidanku har na bigeki akan titi?"cije laɓɓanta tayi kana ta sadda kanta ƙasa tace"bazan manta ranar da yayana yaje B.u.k ya ɗakko ni ba a lkcn ina fama da rashin lpa daga wannan lkcn ban ƙara fahimtar komai ba,sai can cikin dare naji sautin bindigo na tashi a ƙofar gidanmu saurin buɗe idanu nayi tare da toshe bakina sbd kukan daya tawo min,abin mamakin shine ganina da nayi a motar Yayana Fahad hakan yasa nayi tunanin ko shima guduwa yay ya barni? Ko kuma mantani yay cikin motar ya tafi cikin gida,akan idanuna ƴan fashin suka kashe getman ɗin gidanmu kana sukayi cikin gidanmu,kuka na fashe dashi ganin tabbas Iyayena da Yayana suna cikin gidan bana da kuwa saisu,na daɗe a cikin motar kafin na jiyu wani ihu wanda na tabbatar sautin muryar Daddyna ne,hakan yasa na buɗe motar cikin iƙon Allah murfin motar ya buɗe ina fituwa na nufi get ɗin gidanmu da gudu(a zahiri Lubna ta riga Fahad fita daga cikin gidan) gudu nayi sosai kafin na samu wani ɗan lugu nesa da layinmu na fake ina nan tsaye naga motar Yayana Fahad wanda ina da tabbacin Ƴan fashinne suka saceta suka gudu(Rashin sani) wani ihu na fasa lkcn da naga gidanmu naci da wuta hakan yasa na fita hayyacina na shiga gudu akan titi ina wannan gudunne naji wani abu yay gaba dani ban sake sanin inda nake ba sai lkcn dana buɗe idanu na ganni a hospital". Murmushi yay ganin yana son yay nasara akan abinda yake muradi,tashi yay har wajanta kana ya zauna daf da ita saurin ja baya tayi murmushi yay mata yace"Nikam babu abinda zan ƙara taɓawa a jikinki harsai na tabbatar da kin zama mallakina,ina tunanin wani abu akan yayanki Fahad banjin ya mutu hasalima ina tunanin dashi aka haɗa baki wajan kashe iyayenku da dukkan alamu shi ba ɗan gidan bane"a hargitse ta ɗago kai tana kallonsa kafin ta shiga girgiza kanta tana ja baya bakinta ta shiga mutsawa alamar tana son faɗin wani abu amma ta gagara. "control ur self bby harsashe ne am not sure ai take it easy ok,Amma yay akai Fahad ya barki a motarsa? Sannan kaf yawan manyan motocin gidan a rasa wacce za'a ɗauka saita Fahad no akwai lauje cikin ɗani wannan abin aƙwai JUYAYI a cikinsa,lkcn dana bigeki a motata na dawo daga gidan Yayen Mahaifina na nan kano ina hanyata ta kumawa Abuja naganki a tsakiyar titi kina gudu duk yadda nasu na ƙwauce abin ya gagara,tun farkon ganine dake naji kin ƙwayemin banyi wani dugun tunani ba na ɗaukeki na sakaki a mota sai Abuja,kisan Allah bbyn idan akace baki aureni ba babu shakka zan iya aikata abinda ba shikenan ba" Baki kawai ta saki tana kallonsa tare da juya maganganunsa a ranta,tsaki kawai tayi dan bata son ya saka mata wani shakku akan yayen nata,murmushi yay cike da son cusa mata tsanar yayen nata tunda ba saninsa yay ba, gyara zama yay yace"ki manta da komai yanzu ina son sanin tarin rayuwarki domin sanin a salin matar tawa" Fuskantarsa tayi sosai kana ta mutsa bakinta tace Sunan Mahaifina Alhaji Mustapha Rano. _am sorry for the late posting jiya da yau ban samu zama ba,yanzu hakama na katse typing ne sbd uzurin daya tasumin,ayimin hqr aci gaba dayin comments da muhawara hakan nayimin daɗi sosai a raina😍😘_ Fahad and Lubna Sufyan and Lubna Afnerh and Fahad Choose your favorite 😍😍😍and write a beautiful message for them😘a kafta masoyana Juyayi nimcy ta kuce ta Amana no matter what we are together. To me Sufyan and Lili Ina son kalan soyayyarsu tafi shiga rai ka samu mutum mai naci komai sai yay nrml,ƙaddarar Sufyan da Lili daga ubangiji take kuma matar mutum kabarinsa so ni ina Team Sufyan and Lili😍😍💃🏻. _The secret issues_ *💖JYY💖* *32-33* *_NIMCYLUV_* *_Wattpad_* https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb *_Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ *Hey Guys* Ur big writer *MSS FLOWER* pls and be with her follow her on her wattpad accout Check out MssFlower20's profile on Wattpad. https://www.wattpad.com/user/MssFlower20 don't forget to vote and comments, her books *Ƴar so* *Sarki* *Lafazi* and *Gumbar dutse* mss foller ta kuce😘. Speacail gift to *MaimunaAbdullah* my jaruma i lyk ur w hurt coffee and don't forget to wash ur hands and stay Safe😅🙇🏻‍♀️😘only u can relate. #Back to story Not edited ......Haifaffan garin Rano ne shi tun yana yaro Ubangiji ya amshi ran iyayensa sbd hatsarin daya faru dasu,hakan yasa sukaci gaba da zama shida ƙanwarsa Fatima a wajan kawunsu,haka sukaci gaba da rayuwa har girma ya sameshi yaje Cyprus karatu yay karatu mai zurfi kafin ya dawo ya samu aiki acan,aiki mai tsoka kafin wani lkc ya zama shahararran mai kuɗin gske wanda duniya take taƙama dashi,yana da sauƙin kai sosai ga hqr uwa uba ƙyauta abun hannunsa bai rufe masa idanu ba,hakan tasa kullum cikin ƙyauta yake dalilin hakan ya sanya arziƙinsa ƙaruwa,cikin iƙon Allah haɗuwa da wata budurwar mai suna Khadija sosai suke san junansu kamar basa rabu ba,inda aka samu akasi iyayenta basa sonsa dalilin hakan yasa sukace ta rabu dashi,nanfa ta rufe idanunta tace idan bashi ba sai rijiyar,haka suka ɗaura mata aure dashi da sharaɗin koda wasa kada ta sake ta nemesu musamman yayanta da yafi kowa ɗaukan zafi akan abun shida cousin ɗinta Fairus wanda ya nuna mata so tun tana yarinya amma rana ɗaya ta gujesa,haka akai auren inda Alhaji Mustapha Rano ya ɗakko matarsa suka dawo Gida nigeria da zama,shekara na zagayuwa suk haifi ƙyaƙƙyawan ɗansu fari tas dashi,yaro yaci Suna Fahad yarona mai wayon gske kuma mai aiki da ilimi ba daka ba,tun yana ƙarami yake da ƙwarjini da haiba uwa uba cikar zati,yana da juriya domin ko kukannan na ƙuruciya bayayi abu ɗaya ya sani zai zauna yayta zana ƙyaƙƙyawar yarinya a papper yana gama ya rubuta "my sunshine bby" haka iyayen zasita dry,haka rayuwa taci gaba har ya isa matakin zuwa university of Cyprus domin shine ƙasar da tayi masa a karatu,daman tun yana ƙarami aka mai dashi wajan ƙanwar Babansa da zama Fatima wacce ake kira da Momma. Tayi aure inda ta auri abokin yayanta Alhaji Tijjani wambai,sosai soke son junansu kamarsu yime,saidai shuru bata taɓa haihuwa ba hakan yasa aka bata Fahad lkcn Khadija nada ƙaramin ciki. Tasha rigima kafin ta samu yay hqr ya tafi karatun,bayan tafiyarsa da wasu watanni aka haifi yarinya inda taci suna Najma,bayan shekara biyu ta ƙara samun wani cikin inda ta haifi ƙyaƙƙyawar yarinya son kuwa ƙin wanda ya rasa,lkcn ɗaya suka haihu da Fatima,inda ta haifi tagwaye. Ganin bata da wani wanda zai kula da ita yasa ta dawo gidan yayan nata da zama,a tare sukayi rainon Lili da kuma tagwayenta,Lubna ta tasu yarinyar mai hqr da kuma son rashin magana da wahala ta zauna a waje kaga tayi ƙiriniya,a wannan lokacinne Yayan Khadija shida cousin ɗinta suka kawo mata ziyara inda tayi mamaki sosai suka nuna mata komai ya huci,shi daman aure nufine na ubangiji,taji daɗi sosai har saida tayi kuka. Yaransu nada shekera 5 Alhaji Tijjani ya ɗauki matar zuwa Pakistan,inda ta buƙaci yayanta ya bata wani kasu na daga cikin dukiyar da iyayenta suka bar musu,amma yace tayi hqr zuwa wani lkcn aƙwai wani plan da suke shiryawa kan kuɗi,nan tace bata san wannan zance ba,kan dole ya tattara kuɗinta ya bata kana yace duk abinda ya faru babu ruwansa,baƙin cikin hakan yasa tunda suka tafi bata kirasa ba,sannan bata gaya masa address ɗin inda take ba. Sabu mai tsanani ya shiga tsakanin Lili da Fahad kullum suna vedio call a wayan Mamy,lokacin dana da shekara 18 yana da shekara wajan 30 domin akwai tazara mai yawa tsakaninsu,bata bacci sai yay mata waƙa ko kuma ta sashi a gaba taita kuka kamar ranta zai fita ita lallai ya dawo. Soyayya mai ƙarfin gaske ta shiga tsakanin Lubna da Faisal wanda ya kasance lecture ne a makarantarsu ta b.u.k,wata rana yazu zance gidan anan ya haɗu da yayarta Najma,to tun daga wannan rana Najma ta fara daƙon soyayyar Faisal tana dannewa ne kawai sbd kada ƴar uwarta ta fahimta,dan tayi imani da Allah Lili zata iya sadaukar mata da soyayyar Faisal ɗin indai ita zata farin ciki. Ana saura ƙwana ɗaya ɗaurin auren Lili da Faisal,Fahad ya diru garin saukar dare yayi inda yana zuwa ya shige flat ɗinsa bai fitu ba sai wajan 11 na dare,yana fituwa ya tambayi Lili dan itace sanyin idaniyarsa hasalima dan ita ya dawo,ya zama babban likita sosai taku wanne ɓangare ba'a barsa a baya ba. A nan ya samu lbrn bata da lpa sosai ya girgiza dajin cutar da take damun ƙanwar tasa,juyawa yay ya nufi flat ɗinsa domin ɗakko first aid box ɗinsa,kafin ya dawo Najma ta miƙe tare da shigewa bedroom ɗin Lili. Ruwa mai sanyi ta ɗauko tare da zuba wani farin glass cup kana ta cilla wata ƙwaya a ciki tana gamawa ta fice ba tare data bari Lili ta ganta ba. Fahad bayan ya shiga ɗakin ya ɗuki ɗukan abinda zai buƙata na duba Lilinsa,lkcn daya fitu tuni iyayen nasa sun shiga sun dubata ganin mai kula da ita yasa suka tafi flat ɗinsu,yana shiga yaganta flat a ƙwance sai kokawa take da numfashinta,lumshe idanunsa yay dan yau shine rana ta farko daya ganta a zahiri sai a vedio call,zai iya cewa bai taɓa ganin wata halitta ta mace wace tafi ta ta ƙyau ba,sosai zuciyarsa ke zafi aƙan halin daya ganta,ɗan juyawa yay nan idanunsa suka sauka kan glass cup ɗin da aka zuba water a ciki,bai jira komai ba ya kafa a bakinsa saida ya shanye sannan ya nufi inda take tare da zama kan bed ɗin ya zuba mata rikitattun idanunsa,jingina yay da jikin bangun bed ɗin sannu a hankali wata kasala ta fara saukar masa gaba ɗaya ya koma very weak jin yadda take fisge² ya sashi buɗe sexcy eyes ɗinsa wanda sukai masa nauyi,baijin zai iya wani ɗaukan wani abu da niyar dubata kuma ya fahimci sosai take neman taimako,a hankali ya haura saman bed ɗin tare da ƙarasawa inda take ƙwance,a wahalarce ta buɗe manyan idanunta jin mutsin wani a kusa da ita,ƙara ware idanun nata tayi ganin abinda bata taɓa tunanin gani ba,a wahalarce ta miƙa hannu tare da shafa fuskarsa sai kuma ta riƙe hannunsa ƙam cikin nata a lkcnne lumfashinta ya ɗauke,baƙin ciki ne yasa shi fidda ƙwalla ga kayan aikin da zai taimaki ƙanwar amma wata ƙaddarar rashin kuzari ta saukar masa,bai tsaya wani dugun tunani ba ya sanya bakinsa cikin nata ya shiga hura mata iskar bakinsa tare da ɗan danna ƙirjinta kaɗan²,ya ɗauki lkcn kafin ya samu numfashinta ya dawo saidai bata cikin hayyacinta ga wani irin zazzafan zazzaɓi daya gama rufeta,hakan yasa yaɗan zare mata duguwar rigar jikinta ta zauna daga ita sai underwears daman saka beria bai dameta ba,shima jallabiyar jikinsa ya zare domin bani taimaƙon gaggawa bada wata manufar ba,saidai ko hannunsa bai ɗura akai na wani nauyayyen bacci yay gaba dashi,tashin hankali wanda ba'a taɓa sa masa rana farkawar da zanyi na ganni ƙwance a jikinsa gaba ɗayanmu naked muke babu komai a jikinmu,cikin tashi hankali na yunƙura zan tashi naji na ƙasa sbd wani azaba dana keji a ƙasa na,hankali na bai gama tashi ba saida naga jini na zuba ta ƙasa na a lkcn ne na gaba tabbatar da abinda nake zargi na Boobyna yay rappined ɗina for no reason wani jahilin kuka na saki,cikin bacci yaji kukanta yana farkarawa yay saurin jan duvet ya rufe jikinsa ya fara addu'ar da tazu bakinsa,hankalinsa ba ƙaramin tashi yay ba ganinsa da yay naked babu ya shiga tambayar kansa me yayi mai ya aikatawa ƙanwar tasa?akan idanuna ya sanya kayansa yay waje tun daga wannan ranar farin cikina ya tsaya tsanar Yayana ta mannu a zuciyata,dalilin hakan yasa nace na fasa auren Faisal,abun mamakin shine yadda Dr Laylerh ta tabbatarmin am still virgin jinin na meye? Ƙasana da yake ciwo na meye? Meya rabani da kayan jikina? Wannan sune tarin tambayoyin da nakewa kaina a koda yaushe kuma har yau ban samu amsar saba,harna rasa komai nawa,love,happiness,care,mentor,koda yaushe cikin baƙin ciki nake zuciayata na zubar da ƙwallar Rashin ganin Boobyn da banyi wanda nayi imanin yana yare kamar yadda nake raye kuma nake numfashi a doran ƙasa,a taƙaice wannan shine asalin labarina. _Back to story_ Kuka ta saki lkcn data kammala basa tarin rayuwarta,sosai take kuka tare da ƙafarsa tace"Dan Allah dan Annabi Sufyan ka taimakeni idan har son da kakemin gsky ka tayani neman Yaya Fahad,su biyu nake kalla naji daɗi bana da sama dasu ka taimakeni inajin zuciyata na ciwo duk lkcn dana tuna da Booby"durƙushewa tayi gabansa ta saki wani wahalallan kuka mai ciwo a zuciya,kukan da yakewa Sufyan nuni da abubuwa masu yawan gske,zuciyarsa ta cunƙushe ransa yay baƙi faɗuwar gabansa ya ƙaru,dakewa yay yace mata"ok stop cry i will try my best,amma zai wahala idan ba rapped ɗinki yay ba,kema ƙaramar yarinya bace Lubna dukkan wasu alama da zai nuna baki u are not virgin kin gani so why arw u hurting ur Heart akan neman mutumin daya ɓataki sunan kina ƙanwarsa,bazan muzanta yayanki ba amma think about that,yana kula dake tun kina yarinya kinga zai iya zama yana da wata manufar akanki,than ranar daya fara ganin ya rabaki da kayan jikinki ya gama ganin halittar da ubangiji yay maki shin bazai saka ki tabbatar da abinda ya faru dake gsky ne ba? Tun daga ranar baku ƙara zama inuwa ɗaya dashi ba,bai ƙara baki farin ciki ba,tuke tunaninki yana ina kika kasa fahimtar gaky,gsky ya cuceni ya gama dani ba kiji yadda na keji a cikin zuciyata ba,wanina ya sanki bani ba"yana faɗin hakan ya miƙe tsaye tare da ficewa a ɗakin yana mai zabga murmushin cin nasara. Bayansa tabi da kallo harya fice daga cikin ɗakin tana tunani hali irin na Sufyan,amma wani ɓangaren yana son gasgata mata maganganun Sufyan ɗin,Addu'ar neman tsari ta karantu kana ta miƙe tare da ficewa daga bedroom ɗin hannunta ɗauke da plate ɗin abincin da Sufyan ya kawo mata. Parlon yay shuru baka jin ƙarar komai saina T.V wacce take a kunne suna kallan labarai a B.B.C,gaba ɗaya ƴan mata suna ɗaya ɓangaren wanda babu mutane a ciki ana yiwa amarya Fannerh gyaran jiki dan zuwa yanzu baifi saura ƙwana 2 ba a fara event ɗin da aka haɗawa amaren,Mama ce kishin giɗe tana ɗan gyan gyaɗi sbd baccin daya fara ɗaukanta,Momma kam tana can ɗaki tana tsarawa Amare yadda za'a gabatar da Bridel shower,cikin siririyar muryar mai sanyi tayi sallama tare da zubawa Mama idanun gani take kamar ta santa At where shine tunanin da take,Mama wacce cikin bacci taji sallama a kusanta hakan yasa tayi saurin buɗe idanunta,"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" shine abinda yazu bakinta ganin Lilin ba ƙaramin tsoro ya bata ƙara mistsike idanunta tayi ganin tabbas ba gizu take mata ba it real yasa cikin ɗimauta tace"Mamana" ware manyan idanunta tayi jin ta kirata da sunanda mutum ɗaya ne yake kiranta dashi watu Daddy da mamaki ta ware laɓɓanta tace"who are u? How the know my favorite name?"da sauri Mama ta miƙe tare da zuwa wajan Lili ta rungometa tare da faɗin"Allah mai yadda yasu a lkcn dana rasa ɗan uwana sai gashi yaransa na zuwa gareni,Mamana niɗin uwace a wajanki ba lallai ki ganeni ba shekarun da yawa tun kina yarinyar,Masha Allah naji dɗin ganinki Mamana,lallai Fahad yay gsky da yace baki mutu ba"cikin sauri Lili ta kalli Mama tare da maimaita "Lallai Fahad yay gsky da yace baki mutu ba"kenan yana sane cewa tana yare? Yaya akai ya tsira da ransa kamar yadda ta tsira da nata ran,me hakan ke nufi ko mgnar Sufyan gaskiya ne? "no bazai taɓa zama gsky ba nafi kuwa sanin waye Fahad,Boobyn bazai ci amanar zumunci ba,a zahiri kuma ta kalli Mama cikin rashin fahimta tace"so u are familiar? Cikin farin ciki Mama tace "yes my luv niɗin ƙanwar mahaifin kine,yanzu yyanki Fahad yabar gidan nan bansan yay zai jiba idan ya ganki,kullum zuciyarsa cikin kukan rashinki take baya iya dugun bacci baya iya cin abinci,Fahad bashi da walwala Lubna duk a sanadin rashinki cikin ikon Allah gaki kin bayyana a lkcn daya yanke rai da ƙara ganinki"sosai Mama takewa Lili bayanin halin da Fahad ya shiga akanta,kuka ta saka ita dole sai ankaita wajansa ba zata iya zama a inda baya nan ba. Hqr Mama ta bata tare dayi mata alƙwarin nan da 1week zai dawo bayan anyi bikinki keda Sufyan,gaban Lili ne ya faɗi dan a zahiri mantawa take da zatai aure kuma auenma wai Sufyan shine mijin,ganin kukan yaywa yasa Mama ɗaukan wayarta tare da kiran number Fahad amma aka sanar mata a kashe take,haka ta gama rigimarta ta hqr daga ƙarshe tayi bacci jikin Mama. To abu yay abu domin sosai aka shiga gyara amare Fannerh da Lubna wow faɗin ƙyan da lili tayi ba'a magana gaba ɗaya skin ɗinta ya ɗauki kala musamman da aka rage yawan gargasar dake jikinta saita ƙara fari har wani ɗaukan idanu take,tsakanin Fuwaz da Fannerh saidai a waya inda shima yay busy dan yana saran a gobe familynsa zasu sauka daga ƙasa mai tsarki,haka Sufyan ya gagara ganin lovely bbynsa duk sanda yay sa'ar ganinta sai yaji kamar yay hauka sbd wani mugun sha'awarta dake tasu masa ga wani firgitataccen turare mai zautar masa da tunani dake fita a jikinta,banda yaywa kansa alƙwarin daina ta ɓata har lkcn da zata zama matarsa da babu shakka sai yay romantic ɗinta,hakan tasa duk wata hanya dazai ƙaucewa ganinta yake tushewa shi kaɗai yasan tana din daya keyi akanta ya ɗauki alƙwari zai jiyar da ita daɗi zai bata the best sex wanda ba'a taɓa yiwa wata ƴar mace irinsa ba. Ɓangaren Lili gaba ɗaya taƙi ƙwantar da hankalinta kullum cikin kukan Booby take yayinda Mama koda yaushe cikin kiransa take amma amsa ɗaya ne wayar a kashe take,wannan dalilin ya fara baƙanta ran Afnerh ganin yadda Lili ke sakalci akan Fahad. Yauta kamata friday yayinda a ranar ne za'a gabatar da bride shower kamar yadda yake a tsare cikin jerin event ɗin da za'a gabatar a bikin,misalin ƙarfe 4 aka shiga tsarawa amare Make up ta gani ta faɗa(bari na leƙa ɓangaren yayan amarya Fahad😂) _Ƙauyen Yola_ Haba Uwande ke kenan cikin kukan rashin ƴarki kamar ƙaramar yarinya abu yaƙi ƙarewa a wajanki shekara da shekaru sabida Allah,kina nunawa cewa baki yadda da ƙaddara ba kenan ko"sharce hawayen dake bin fuskarta tayi tare da face majina tace"Haba Baba Habu yaya kakeso nayi ita ɗaya nakeda amma na rasata sbd baƙin ciki irinna kishiya"baki ya buɗe zai magana yaji saukar muryarsa mai cike da kamala Fahad na gaba Musty na bayansa ɗauke da jakarsa,haba wani tsalle da Baba Habu yay tare da hankaɗe Uwande dake zaune yay ciki bukka yana faɗin"wayyo Allah kidnama wlh yau na tashi a zawayin da nake babu nama jikina Allah yaywa shanuwata guda rasuwa😅.. *kai haba Ƙwace naje na wuta mana wannan typing kamar me🤣wata ta kawu ɗauki farfesun kai da ƙafa na rago wanda yaji kayan ƙamshi haɗi da daddawa😋saina ɗura* Kada ku manta da comments ya Sarauta na keji👸🏻👸🏻👸🏼idan ba kuyi ba zanje Fada wutun mako guda🥰. F@y@l _The secret issues_ *💖JYY💖* *34-35* *_NIMCYLUV_* ```Wattpad@Nimcyluv``` Ya Allah dukkan wanda zamana dashi ba alkairi bane Ubangiji kayimin maganinsa domin kafini saninsa,Allah ka rabani da sharrin mai sharrin,da hassadar mai hassada,Allah kamar yadda bana ƙwana d wani a raina ina roƙanka daka nisan tani da maƙiyana,ubangiji kayimin tsakani dasu,Ya Allah ka rabi dayi da wani ubangiki ka ciremin tunanin abinda bazai amfaneni ya Amfani ƴan uwana ba🙌🏻👏🏻, *Allah ka ƙarawa maƙiyanmu nisan ƙwana dan suga ci gabanmu😅✋🏼* ......Wayyo Kidnama yana faɗin hakan ya ƙarasa shigewa bukkar tare da rufuta,wani ƙawataccen murmushi Fahad yay wanda a zahiri ya daɗe baiyi murmushi kamarsa ba,sosai murmushin ya ƙarawa ƙyaƙƙyawar fuskarsa kyau zati da cikar haybarsa suka ƙara bayyana,murmushin da yay sanadiyar bayyanar da fararen jerarrun haƙwaransu mai masifar ƙyau har wani ƙyalli suke,murmushin da yay sanadiyar lutsawar beautƴ poits ɗinsa wanda suke iri ɗaya dana Lili,hannu yasa ya shafi gefen sajensa tare dajan ɗan madaidaicin gemunsa,girgiza kai kawai yaya kana ya nemi wata tabarmar kaba irinta fulani ya zauna tare da tanƙwashe ƙafafunsa,lumshe tsumammun idanunsa yay kana ya taune lips ɗinsa some minutes ya ware idanunsa tare da mannasu akan Uwande yace"Adda ina yini"washe baki tayi kana tace"Lahiya walle ya tafiya"Jinjina kansa cikin gajiyawa da maganar yace "Allahamdulillah" miƙewa Uwande tayi kana ta shige ɓangaren shanunsu hannunta ɗauke da ƙwarya,Nono ta shiga tatsu masa wanda ya kasance fresh babu mix tana gamawa ta miƙe tare da ficewa daga wajan,inda Fahad da Musty suke ta dawo inda suke shira ƙasa² wacce duk rabinta Musty ne keyinta,ƙwaryar Nonon ta bashi karɓa yay tare da faɗin "جزكالله" babu ƙyama yay bisimillah tare da kafa bakinsa a ƙwaryar Nonon,lumshe sleepyn eyes ɗinsa yay sbd yadda Nonon yay masa daɗi da kuma garɗi cikin bakinsa,kasan cewarsa babban likita ne wanda yasan makamin aiki yasa ya buɗe cikinsa yasha kindirmun danya san amfaninsa musamman mara mix,saida yasha fiye da rabi dan dama ba wani abin kirkine a cikinsa ba,hamdala yay kana ya miƙawa Musty ƙwaryar karɓa yay dan shima yana so,domin Baba Habu baya bari a tatsar masa nonon saniyarsa,miƙewa Fahad yay tare da nufar bukkar da Musty ke ƙwana yana shiga ya samu ɗakin komai need kamar ba'a ƙauyen fulani ba,rigar jikinsa ya zare ya saƙaleta a waya ƴar igiya kana ya zauna bisa shimfiɗar Musty,numfshi ya sauke tare da shafa ƙirjinsa murmushi ya saki a karu na biyu kana ya cije light red lips ɗinsa cikin sanyin murya mai kama da amo yace “Ruhina” wayarsa ya ɗauka mai ƙirar iphone 11 pro password ɗin wayar ya buɗe cikin harafin “HADNERH” yana gama wayarta buɗe cikin wani irin ya nayi ya zubawa ƙyaƙƙyawa photon ta idanu danyi dake da riga da wando na ball tun tana yarinya tana zaune ta rungome ta ball ɗin a ƙirjinta yayinda gashin kanta da aka tufke mata ya sauka har bayanta,idanunta a rufe yayin data tura small s peach lips ɗinta gaba cike da sha'awa,a hankali wani irin yanayi ya fara saukar masa yanayin da bai taɓa jinsa a kan wata ƴar mace ba sai ita,sanyine ya fara ratsa ƙofufin jikinsa tsigar jikinsa ta fara mimmiƙewa yayinda idanunsa suka fara lumshe a karu na farko kennan a rayuwar da yaji wani irin feelings ya tasu masa wanda bazai iya cewa ga dalili ba,dan bai ɗauki tunanin Lili ne ya haddasa masa hakan ba,yafi bawa zuciyarsa wani abu nada ban,cike da shauƙi wanda yake fisgarsa ya ɗura hannunsa saman cute lips ɗinsa tare da shafa,saurin ɗauke hannunsa yay jin wani abu ya suki ƙahun zuciyarsa,cike da bige ya manna wayar a saitin zuciyarsa tare da rungometa yana ji kamar Lilinsa a jikinsa,cikin lion voice yace “My sunshine bby sai yaushe ne zan ganki,sai yaushe zanyi arba da Amanata ki baiyana gareni zuciyata ciwo babu dɗi pls" ya faɗa yana tura bakinsa tare da langwabar da kansa gefe cike da shagwaba cikin abinda baifi 5min ba bacci ya ɗaukesa cike da begen Amanarsa. Bai tashi ba sai misalin ƙarfe 6na yamma sosai ya bacci dan samun nutsuwar kansa,bakinsa ɗauke da salati ya farka tare da miƙewa zaune cike da kasala yana jima kafin ya tashi yay waje daga shi zai ƴar singlet ɗin jikinsa,a zaune ya samu Musty shida Baba Habu suna taɗi,"kaga Musɗapha kada ka ƙwana da kuran mutuminnan wallahi ɗan jinin da kake dashi sai yasa baki ya zuge tass,koka farka kaganka babu kai"dry Musty yay yace" to indai har babu kannawa tayaya zan farka?"kallonsa Babu yay yana ƙoƙarin magana Fahad ya ƙarasu wajan cikin tausassayiyar murya yace"babu shakka idan na tashi tafiya da kai zan tafi Baba"kafin kace me Baba habu ya saki ihu sai kuma ya saki gudawa a wando sabida tsananin tsoro da fargaba,girgiza kai kawai Fahad yay tare da zama kusan Musty,da saurin Baba Habu ya miƙe tare dayin makewayi,numfashi yaja tare da ƙara lanƙwasa ƙafarsa cikin nutsuwa ya kalli Musty yace"Nikam banyi mantuwar wasu takaddu ba a nan bro?"shuru musty yay kana ya girgiza kai yace"bana jin kayi mantuwar komai sai wannan ƙaramin photo mai ɗauke da zannan flowers i think ƙaramar yarinyar ce a jiki very ncy wlh bro yarinyar aƙwai ƙyau masha Allah dama a bani ita na aura"runtsa idanunsa yay da ƙarfi sosai maganganun Musty sukai masa ciwo a zuciyarsa wai yarinyar nada ƙyau shi bashi da prblms da ƙyau ɗinta,taɓe baki yay yace"abinda aka tambayeka daman abinda kake daban ko?"dry Musty yay yace"Allah da gaske komai naku iri ɗaya ne the eyes ball,the same beauty poits,the same smile everything dai"miƙewa yay jin Musty na neman bashi ciwon kai yana tashi yace"talkative" tare da shigewa bayi ruwa ya watsa a ɗan gaggauce sbd yanayin bayin sannan ya ɗaura alwala jin ana kiran magrib,shiryawa yay cikin wata farar jallabiya mai ƙaramin hannu tare da murza hula tashi ka fiya naci,ya ɗaura baƙin hirami sbd sanyin dake kaɗawa sosai yay kamar wani balarabe a jere suka nufi masallaci,Baba habu bai fitu ba saida yaji fitarsu waje da sauri yay alwala tare da shigewa ɗaki ya rufe Uwande sai dry dake masa,basu dawo gida ba saida sukayi sallar isha'i tare da shiga cikin birnin ƙauyen Fahad yay siyayyar kayan abinci mai yawan gske hadda gas su kayan miya nama kifi lemo ruwa kaya dai masu yawa,shine ke dreving a motar daya bawa Musty cike da ƙwarewa yake jan motar muryarsa na tashi sbd ƙira'ar daya keyi cikin suratul Anbiya'i tym to tym yana lumshe idanunsa sbd yadda karatun keyi masa daɗi,Idanu kawai Musty ya zuba masa danshi kansa yana injoy karatun bareshi dake rerawa tamkar waƙa sosai yay mamaki baiwar ilimin na Fahad dai bai taɓa kawuwa yay karatun addini mai zurfi har haka ba,murmushi Fahad yay kana ya karya kan motar zuwa layin kakannin Musty ɗin"Ka daina mamaki shi addini a zuci yake"yana faɗin hakan yaci gaba da karatunsa har yay parking a kasalance ya fitu daga motar tare da shigewa cikin gidan sbd baccin dake cikin idanunsa,Musty ne ya shiga fituwa da kaya kafin ya gama har Fahad yay bacci shima shiryawa yay cikin kayan baccin tare da ƙwanciya kusa da Fahad ɗin yana jinsa kamar ɗan uwana a haka bacci yay gaba dashi. *** **** Hadaɗdiyar ƙwaliyya mai make up da tsara masa nayin yadda tabi skin ɗin kuwa da special make up ɗin yasa ko wacce ta shiga bada kala,banbancin makeup ɗin a bayyana yake inda aka sakawa Fannerj red lipstic yayinda aka sakawai lubna bby pink lipstick wow ya haɗu da fresh skin ɗinta yay mata kyau,wata red ɗim gwon aka sakawa Fannerh tare da ɗaura mata wani black ɗin head akanta,Lubna kuma farar duguwar riga har ƙasa aka saka mata wuyan rigara mai met ne hakan hakam ya bawa dugun wuyanta damar fituwa,red ɗin head aka ɗaura mata ɗaurin V tare da fitu da gashinta ta baya,kana aka saƙala mata wata red ɗin abu an rubuta bride to be,sai ƙatuwar flower mai ƙamshi fara tas mai ɗan zagayen green aka bata a hannunta ta riƙe,faɗin ƙyan da tayi ma'a magana a zahiri idan kaga Lili zaka ɗauka tana son auren amma dwon hrt ɗinta ita kaɗai tasan abinda ta keji,wani zafi da raɗaɗine yake ziyarta ta a duk sanda da ta tuna wai matar aure zata zama,idanunta ne ya cicciko da ƙwalla amma ta shanyesu dan bata son a gane rauninta,Afnerh da Yusrah ne suka shigo tare da wasu ƴan mata cikin shigar kaya mai colour white and red sunsha ƙyau amma ba wata ƙwailliya sukai ba,photona aka shiga fella masu tare da vedio banda turo baki babu abinda Lili take haka saiya ƙara mata ƙyau,jerawa sukai tare dayin compound ɗin gidan inda aka tsarashi tamƙar hall ya ƙawatu da flowers da kuma ƙwayen masu haske wanda suke bada colour daban²,cikin sanyin jiki da kuma nutsuwa amaren suke tafiya yayinda ƴan matan suke watsa masu furanni masu ƙamshin duk inda dukai camera man na biye dasu yana vedio,suna isa tsakiyar wajan M.C ya saki wata lafiyayyiyar waƙa mai daɗi da kuma sanyi tsuhuwar waƙace ta koredo bello,wani lafiyayyen murmushi Lili ta saki babu wanda ya faɗu mata a rai sai Booby domin wannan waƙar itace foravite ɗinsa acikin waƙoƙi,daɗi da sanyi waƙar ne yaɗe beta cikin sanyi ta lumshe idanunta tare dayin juyi nan take faffaɗan waist ɗinta ya shiga mutsa cikin farar gwon ɗinta,nan fa waje ya karaɗe da ihu camera man yace dawa Allah ya haɗani ba dake ba,ya saita camerar a kanta,duk wani juyi da take baya tafiya saida tunaninsa,haka duk wata kallama dazai fita a cikin waƙar saida begensa,salon waƙar da daɗinta yasa tama manta da cewa bason auren take ba,cikin yanga ta ƙwarewa take juyawa faffaɗan waist ɗinta duk da ita ɗin ba gwanar iya rawa bace ba amma yadda take juyi a hankali tare da ɗan ɗaga hannunta tana sama da ƙasa kaɗan² zaisa ka ɗauka ta shahara a iya rawa,baya taja kaɗan tare da ɗura hannunta na hagu a waist ɗinta tayi wani irin juyi sai wajan ya ɗauki ihu M.c ya ƙara sakin kiɗa danshi kansa yana injoy rawar,juyawa tayi zata bar wajan taji anyi saurin riƙeta tare ɗura hannayensa a waist ɗinta ya ɗan murza kaɗan ganin tana ƙoƙarin guduwa yasa yay saurin mannata da ƙirjinsa.. *😂⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️Allah yasu ku nayi typing amma da wlh ina ƙwance abuna ina hutawa🙇🏻‍♀️masu cewa zasu kawomin farfesu ina nan ina jira kada a manta yaji kayan ƙamshi🤏🏼😋* F@y@l *💖JYY💖* *36-37* *_NIMCYLUV_* ```Wattpad@Nimcyluv``` *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ والذاكرين آلله كثيرا والذاكرات أ عدالله الله لهم مغفرة واجرا غظيما. .....Wani yawun takaici ta haɗiya tare da runtsa idanunta ta shiga kukawa da numfashinta daya ɗauke,yay mata abinda ba tayi zatu ba,yayinda wani shashi na zuciyarta ya cika da kunyar abinda yay mata a gaban mutane,lumshe idanunsa yay sosai ƙamshin dake fita a jikinta ta yafi dashi,ƙara ƙasa yay da kansa zuwa wuyanta tare da tura hancinsa wata ajjiyar zuciya ya sauke wacce take nuni da zallan abinda yake ransa da kuma yanayin dake gangar jikinsa,sosai feelings ɗinta ke neman zautar dashi ya tare da dagula masa lissafi,ware idanunsa yay tare da mannasu akan fuskarsa,a sanyaye yaɗan murza waist ɗinta haɗi da juyata suka shiga fuskantar junansu,yadda ya sanya hancinsa a wuyanta hakan ya ƙara ɓata mata rai zuciyarta ta shiga ta fasa idanunsa ya ƙanƙance kaɗan hakan ya tabbatar ɓacin ranta yaje ƙarshe dan abune mai wahalar gaske kaga idanunta sun sauya,wani huci ta fita mai zafi tare da fincikar numfashinta wanda ya ɗauke sanadiyar murza waist ɗinta da yayi,kasa ɗago kai tayi saima wasu siraran hawaye da suka shiga zuba daga cikin idanunta,yadda hawayen ke fita ta cikin idanunta ya sashi sasauta riƙon da yay mata,hannunsa yasa ya tallafu haɓarta tare da zuba oval face ɗinta idanunsa,bakinsa ya masu daf da kunanta yace"meye na kuka bayan mun kusa cima burinmu?"still bata buɗe idanunta ba haka kuma ta gagara cewa komai sabida wani abu daya tsaya mata a maƙoshi,kalamansa jinsa take tamkar ruwan dalma a zuciyarta. "Meye?" Shine abinda ya ƙara tambayarta a karu na biyu,bakinta ta shiga taunewa haɗi dasa hannu ta toshe bakinta ganin kuka nason ƙwace mata,kai ta shiga girgizawa tare dayin baya,ganin yadda ta ruɗe ta fita hayyacinta yasa yaja baya zuciyarsa a cunkushe ya juya yabar wajansa,wata ƙatuwar ajjiyar zuciya ta sauke tare da dafe ƙirjinta dake ɗagawa,a hankali taja jikinta zuwa wani ɗan luku da babu kuwa durƙushewa tayi a wajan tare fasa kuka mai ciwo,kuka take sosai kukan dake nuna zallar damuwar dake ƙwance a ranta,kuka take mai nuna abinda zuciyarta ke muradi d kuma son kasan cewa dashi,kuka take wanda yake nuna tana cikin kewa da buƙatuwa,ƙara ƙanƙame jikinta tayi tare da cusa kanta tsakanin cinyoyinta ta shiga rera kukanta mai cin rai. A can wajan amarya Fannerh sosai abin yay armashi sunsha rawa tare da cashewa,kana aka yanka cake saida komai ya lafa za'a yanka cake ɗin Lili aka shafa a kaga bata wajan,dariya suka saka Yusrah ta buɗe baki tace"ai kawai mucinye shi daman bai isheni ba tana can tabi mijinta daɗi soyayya Allah dai ya bamu masu sunmu"dry Fannerh tayi tare da faɗin Ameen dai ƴar uwa ga wannan sakalyar ta tsaya son masu wani"da sauri Yusrah tace "kai haba kice ƙaddarar soyayya ta faɗa mata,wama take sone?"taɓe baki Fannerh tayi kana taja tsaki tace "Yaya Fahad wai fa,inda yake dajin kai gashi nan ko kallo bai isheta ba,bama ƙya gabansa,aikin banza ayi mutun ko zuciya babu na fahimci wannan farar fatar da sajen ke ruɗarki"wani tari ne ya suɓucewa Yusrah tayi saurin ɗaukan ruwa tasha,numfashi taja tare da faɗin "Don't tell me guy ɗin da nagani a gidanan?"Afnerh wacce tun ɗazu ba tai magana ba sbd ɓacin rai da kuma baƙin cikin maganganun Fannerh,sosai ta zubawa Yusrah idanu tana son gane mood ɗinta amma ta kasa saima cewa da tayi "to Allah ya ƙyauta" tana faɗin hakan taja bakinta tayi shuru tare da lulawa duniyar tunani,murmushi Afnerh tayi tare da faɗin "he's mine tabbas Fahad nawa ne kuma zan tabbatar maku da hakan idanma wata na tunanin sonsa wlh tayi ƙarya" Babu wanda ya kulata bare tayi tunanin zasu tankata,Khalisat dake gefe wacce tun ɗazu take sauraransu tace "abun babu sauƙi mutuniyata gske zansu naga wannan guy ɗin"gira ta ɗaga mata tare da faɗin "zaki ganshi soon,amma zaki zaucewa sbd ƙyansa am telling u"gaba ɗaya suka rankaya zuwa cikin gida. A parlour suka tarar da Mama da Momma sai kuma wasu mata guda biyu tare da wasu maza wanda shekarunsu masu huce irin 35 ɗinnan ba,zama ƴan matan amaryar sukai tare da gaida baƙin,Mama ce ta kalli su Afnerh tace. "Wannan Yayan mahaifiyar Fahad ne,Sunansa Khalid wannan kuma cousin ɗin Khadija,Mamy kenan mahaifiyar Lili sunzu bikine a matsayinsu na iyayen amarya wanda zasu maye mata gurbin Mahaifiyarta,bayan ta gama bayanin mazan ta kalli matan tace"Wannan kum surukan Fannerh ne basu jima da sauka ba shine suka shigo tare da kawu lefe kamar yadda sukai alƙawari,Wannan yayar Fauwaz ne Suwaiba,wannan ma yayarsa ce sunanta Lawiysat" Sunna kai Fannerh tayi tare da ƙara gaishe su,baki suka haɗa wajan amsawa tare dasa mata albaka sosai suka yaba da hankalinta,sallama sukai masu tare da ficewa suka nufi motar dasu kazu da ita. Fairus ne ya nisa yace "ni ina ƙanwar tawa ne da kuma ɗana,naga ban gansu ba" Mama ce ta kama zancen tare da faɗin "Yarona baya gari dan banjin yana nan za'a auren,Lubna kuma su Yusrah zan tambaya tana ina"munyi tunanin tun dazu tana cikin gida ai bama tare sun fita da Yaya Sufyan" daga bayanta taji ance "wane Sufyan ɗin? Malamai ku tashi ku nemu min matana" ya faɗa yana haɗa ransa. Khalid dake matsayin Uba wajan Lili tunda yayan mahaifiyarta ne yace"aa barsu aiba zata ɓata ba,tunda muna nan ai zamu ganta"baki Mama ta buɗe zatai magana taji Lili tayi sallama,gaba ɗaya suka ɗago kai tare da zuba mata idanu,cikin rawar Murya Mama tace "Mamana meye kike kuka?"da gudu Lili ta faɗa jikin Mama tare da fasa kuka ta shiga dukan Mama kamar mahaukaciya,Cikin damuwa Mama ta ƙanƙameta a jikinta tsam har saida ta daina bige-bigen, cikin damuwa tace "Mamana daina kuka dan Allah hakan yana baƙanta raina,tashi kiga ƴan uwan mahaifiyarki sbd dake sukazu nan" girgiza kai Lili tayi bakinta na rawa tace "Mamana i want to see Booby zuciyana ciwo zan mutu Mam ki kiramin Boobyna" Maganar kamar saukar ruwan sama haka Sufyan yaji wani takaici ne ya kamashi cikin saurin ya buɗe baki zai magana sai kuma ya fasa ya fice daga cikin gidan. Da ƙyar Mama ta lallaɓa Lili akan da kanta zata nemushi,jiki a sanyaye ta miƙe ta nufi bedroom ɗinta kota kan Khalid dake matsayin yayan mahaifiyarta bata biba bare Fairus ya saka ran zata kulasa shida ke matsayin cousin na Mamynta,sallama sukaiwa Mama tare da nufar hotel ɗin da suka sauka,Amarya Fannerh da ƙawayenta suka nufi ɗakinsu yayinda Afnerh tayi zamanta a parlour tunaninsa yabi ya addabi zuciyarta yadda zata mallakesa cikin ruwan sanyi take nema yayinda gefe guda na zuciyarta ya cika da tsanar Lili wanda ita kanta bata san dalilin hakan ba,miƙewa tayi ta shige ɗakinsu. Lili na shiga bedroom ta huce toilet ruwa mai zafi ta haɗa tayi wanka tare gasa jikinta,al'wala tayi kana tayi brush ta fitu jikinta ɗauke da ƙaramin towel,wajan dressing mirrow ta nufa tare da juna handrayer ta busar da gashin kanta,buɗe ƙofar akai aka shigo ɗauke sallama,ganin Mamace yasa ta saki fuskarta,wajanta ta ƙarasa hannunta ɗauke da kaya,zama tayi kan stool ɗin dake gefen dressing mirrow,bata kalli Lili ba ta shiga zuba wani magani a glass cup sannan ta siyaya madara ta ruwa tasa spoon ta juya fuska babu walwala ta miƙawa Lili danta san halinta daƙin magani,ganin yadda Mama ta haɗa rai yasa ta amshi magani ba dan tana so ba,saida ta shanye tas sannan Mama ta miƙa mata wata zuma nanma ta amsa wannan karan hadda tanɗe baki sbd daɗin zumar,Hucewa Mama tayi ta nufi toilet ɗin Lili ta haɗa ruwa mai zafi tare da zuba turare a ciki kana ta dawo ta ɗauki wani ƙwabaɓɓen yellow abu a ruba ta shiga shafawa Lili a naked body ɗinta,Mama irin mutananne da babu ruwansa da batun kunya indai akan harkar gyara ne kanta a waye yake tana da sauƙin kai sosai shiyasa mutane keson zama da ita,bayan ta gama tace"nan da 30mins kije ki wanke jikinki sannan ki shiga ruwan zafin dana haɗa maki,idan kika fitu wannan lotion ɗin shi zaki shafa ga boner ki juna ki zuba turare ki tsuguna ya ratsa jikinki sosai"tana faɗin hakan ta juya zuwa wajan Fannerh. Duk yadda Mama tace tayi saida tayi,hakan yaza mana kamar an sauya mata halittar jikinta banda ƙamshi babu abinda ke fita a jikinta,skin ɗinta kam har wani yellow yake sabida gyaran da yaji ta zamana kamar ƙwai ko ina shaning yake musamman fresh skin ɗinta,a gaggauce ta gabatar da sallah tare da hawaye bed ta rufe jikinta da duvet lkc kaɗan bacci yay gaba da ita sbd gajiya. Bayan Mama ta kammala abinda take tayi wanka ta shirya cikin kayan bacci,dabarar yiwa Fahad MSM ta email ɗinsa ta faɗu mata,cikin sauri ta ɗauki wayarta tare dayi masa tana gamawa ta kashe bacci fal idanunta hakan yasa ta ƙwanta nan bacci itama ya ɗauketa. Ranar Asabar aka gabatar da Henna day yayinda abin yay armashi amare aka tsara masu jan lalle na salatif har zuwa saman ƙafarsu,faɗin ƙyanda Henna ɗin yay ɓata lkcne dake gaba ɗayansu farare ne,haka aka haɗa da traditional wedding aka kama amare,Lili kam kuka tasa akan ita babu mai fesa mata wani turare abarta da abinda ta keji,kowa yay mgn tai burus dashi hatta Khalid saida yazu shiku albarkacin kallo a wajanta bai samu ba,wajan ƙwanansu uku amma ko gaisuwa bata haɗasu ba,saida Mama tazu da kanta sannan ta bari aka kamata kamar yadda ake kama sauran amanare,kuka ta fashe dashi kowa na wajan yasa mata dry ƙanƙame Mama tayi ta shiga rera kukanta"Haba Uwata ta kaina ya isa haka,baza a ƙara ba"ta faɗa tana bubbuga bayanta har saida tayi shuru,ba'a tashi wajan ba sai bayan isha'i. Jikin kuwa a gajiye suka shigu cikin gidan,a gaggauce Lili tayi wanka ta gabatar da komai nata kasan cewar ba sallah zatai ba domin tun safe period yazu mata,tana gamawa ta ƙwanta tare da lulluɓe jikinta. Daman yadda tsarin yake sai anyi ɗaurin aure da yamma kuma ayi mothers day,da daddare kuma ayi dinner Sai award for the best couple. Juyi yake kawai akan bed zuciyarsa taki nutsuwa sai azalzalarshi take yaje gareta,musamman idan yaji mararsa ta murɗa masa,amma idan ya tuna gobe iyanzu ta zama mallakinsa sai kawai ya share,a hankali yake murza mararsa data kumbura ciwo yaci ƙarfinsa,ganin idan bai bawa kansa taimaƙon gaggawa ba kamar yadda ya sama zai iya samu matsala,tashi yay tare da zare dugun wandon jikinsa yay cikin toilet,yana zuwa ya haɗa ruwan zafi tare da cire sauran kayan jikinsa ya shiga cikin ruwan,a hankali a ɗura hannunsa saman mararsa ya shiga jijjigawa,wajan 20mins da fara ya ɗan saki ƙara hakan ya tabbatar masa daya samu sauƙi daga sexcy pain ɗin da yake,wakan sarki yay sannan ya fitu jikinsa ɗauke da towel,kan bed ya faɗa ya daɗe kafin bacci ya ɗaukesa. Ceremony Yauta kama Sunday ranar da za'a ɗaura aure,tun safe ta shige ɗaki ta ɗinga kuka ko abinci taƙi ci a wannan karan ba iya Booby take kira ba,hadda Mamy da Daddy haɗi da Faisal😢ita kanta mama zuciyarta tayi rauni hakan yasa ta shige ɗaki ta fara kukan rashin yayan nata,da ƙyar mijinta ya rarrasheta wanda yay shiguwar cikin dare,misalin ƙarfe baƙwai mai makeup ta ƙarasu inda aka tsarawa amarya Fannerh yayinda Lili tace bata buƙata a barta,girgiza kai kawai Sufyan yaya tare da miƙewa ya nufi ɗakinta,a ƙwance ya sameta sai sakin ajjiyar zuciya take,tana ƙwance daga ita sai towel iya waist ɗinta,numfashin sane ya ɗauke na wani lkcn sosai skin ɗinta da kuma ƙamshin dake fita a jikinta ya nemi zautar dashi,"lovely bbyn nine baki so ko auren yau kikemin hakane ba zakiji tausayina ba?"luff tayi tare da lumshe idanunta ba tare data tankasa ba,haurawa yay saman bed ɗin tare da birkitota ta faɗa jikinta,saurin dafe ƙirjinta tayi haɗi da suma girgiza kanta,wani shu'umin murmushi yay mata kafin ya sunkuyar da kansa zuwa wajan kunnanta,iskar bakinsa ya shiga wura mata tare da tura halshansa cikin kunnanta ya shiga lasa,runtsa idanunta tayi lkcn hawaye ya samu damar zubuwa daga cikin idanunta,cikin rawar murya tace"banso pls kabari"cikin da ƙushewar murya yace"ni inaso bari kawai na mallakeki a nan tunda kinki fita a shiryamin ke nima na samu damar shiryawa naje a ɗaura mana auren"da sauri ta ƙwance jikinta tace "zani wallahi zani"tana faɗin hakan ta zari hijab ɗinta tayi ɗakin da ake makeup ɗin,ya daɗe zaune yana maida numfashi kafin ya miƙe ya nufi ɗakinsa. Ɓangaren ango Fuwaz ba'a magana ya haɗe cikin light blue ɗin shadda wacce taji ɗinki riga da wando da kuma babbar riga,yayensa Suwaiba da lawiysat sai kuma sauran ƴan uwansa,misalin 10:30 abokansa suka shigo tare da ficewa dashi daga cikin gidan domin 11:00 ɗaurin auren,rashin Fahad a wajan ba ƙaramin ɓata masa rai yay ba amma ya share. Sosai aka shirya Lili cikin duguwar riga ta shadda mai kalam milk ɗinki Bubaa yaji zare,idan kaganta sai kazu ƙara kallonta ta kuma kamar ƴar tsana,Sufyan ma ya shirya cikin ash ɗin shadda mai ƙyau babu babbar riga daman bai fiya sonta ba,amma yay ƙyau har ba'a magana. Mutane kake gani kota ina babu matsakar tsinke kowa yana cikin farin ciki,musamman angwaye Sufyan da Fauwaz,addu'a aka fara gabatarwa kana aka amshe neman aure daga ku wanne ɓangare,inda Khalid ya zama Uba a wajan Lili ya bada aurenta wajan Sufyan,yayinda Alhaji mahaifin Sufyan ya bada auren Fannerh zuwa ga kawon Fauwaz,Uncle Mahaifin Fannerh ya amshi auren Sufyan da Khalid ya bashi,cikin farin ciki aka fara addu'oin ɗaurin auren,wata muryace mai sautin da amo ta sauka a tsakiyar wajan,malamin ɗaurin aurenne yace"Yarona lafiya dai" idanunsa da sukai matuƙar jaa suka ɗan rage daga girmansu ya zubawa Sufyan,yayinda Fauwaz kuma ya zubawa Fahad idanu yana mamakin dawowarsa,yana tsaye cikin shiga ta alfarma,sanye yake da farar shadda getzner yasha babbar riga sai walwali yake,haiba da annuri sun cika buskarsa hakan yasa kowa ya gagara ce masa ƙala,cikin tausassiyar murya yace "stop the ceremony" wani mugun kallo Sufyan ya watsawa Fahad cikin fusata yace"waye kai? Wanne matsayi kake dashi? Meye dalilinka daza kace a tsaya da ɗaurin aurena?" ya faɗa lkcn dake miƙewa tsaye ya nufi inda Fahad yake tsaye ya harɗe hannayensa,shima cikin ƙaraji da nuna cewa zuciyarsa a kusa dake yace "because she is my wife". *Dan Allah dan Annabi idan har kinsan na faranta maki rai a wannan shafin ina neman alfarmar kiyi share ɗinsa zuwa groups ɗin da kike👏🏻👏🏻,idan kinsan kinyi farin ciki da abunda ya faru da Allah kiyimin Comment mai ma'ana pls,daga ƙarshe ina neman addu'arku ku tayi da addu'a pls🙌🏻ina maku sahihiyar ƙauna masoyana masoyan Juyayi😘* F@y@l *💖JYY💖* *38-39* ```SARAUTA``` 👸🏼 *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ *Dedicated to* Yaya Mu'az, Bro Muhammad Ibrahim, N.yareema, Fa'at class, Hassan basiru,Muhammad kareem, Al'amee, ```kuna ƙoƙari sosai Allah ya saka da alkairi😍``` 👏🏻 Not Edited ..A hargitse Sufyan yayu kan Fahad,Fahad na ganin hakan ya gyara tsaiwarsa tare da harɗe hannayensa a ƙirji,Wani shu'umin murmushi yaywa Sufyan,cikin kiɗima Sufyan yace"wat are you try to see?"gira Fahad ya ɗagawa Sufyan tare mutsa jajayen laɓɓansa yace "i knw u alry heard wat i'm say" wani mugun damƙa Sufyan ya kaiwa Fahad tare da faɗin" are u crzy matar da zan aura kake kira da ur wife,a wajan ɗaurin aurena da matana zaka kawumin maganar shirme kace matanka ne"lumshe idanu Fahad yay tare dayin wani murmushin gefen baki wanda ya ƙarawa fuskarsa ƙyau haibarsa ta ƙara fituwa,annurin dake fuskarsa ya ƙara bayyana,cikin lion voice Fahad yace "Ka daina haɗa kanka da macen da take mallakina,she's always mine not urs understand"ya faɗa cikin ƙaraji da kuma nuni da gargaɗi,ganin rigima nasun kaurewa tsakaninsu yasa gab ɗaya aka zaunar dasu,Fahad ne ya ɗaga kai ya kalli mutum dake gefensa wanda ko ba'ai magana ba yasan jinin Mamynsa ne,cikin fahimtar juna Alhaji wanda ya kasance uba a wajan Sufyan yace "Dr Fahad yaya akai Matar da ake shirin ɗaura mata aure da wani kazu kace matan kane,Alhalin kuwa yasan cewa ita single ce bata taɓa aure ba"jinjina kai Fahad yay tare da ɗan tafa hannunsa saiga Musty yay sallama tare da shiguwa cikin parlour,cikin muryarsa wacce take ɗauke tada jurumta yace "Musty karanta wasiƙar nan a fili yadda kuwa zaiji" Babu ɓata lkc Mutsy ya buɗe takaddar hannunsa tare da gyara tsaiwa yace. _Na san kuwa zai mamakin yadda Lubna zata kasance mata a wajan ɗana Fahad,Tabbas Lubna matsayin ƴar take a wajena amma a zahiri banine Mahaifinta wanda ya kawota duniya ba,Lubna ƴarce a wajan ƙanwata Fatima ita kanta bata san da hakan ba sai yanzu idan ta samu labari, wata rana kafin raɗin sunan ƴar da mamata ta haifa da kuma twinst ɗin da ƙanwata ta haifa kasan cewar ta dawo wajena da zama kafin arba'in,ta shine daga zaunan na nufi waje tare da shiga mota na amso wani saƙo wajan abokina wanda ya kasance Miji a wajan ƙanwata Fatima,bayan na shiga mota na dawo ina gaf da shiga gida naga wasu mutane sanye da fuska na girgiza sosai ganin gida suke kallo ba tare dason ganni ba,na rufe glass ɗin mota ta kasan cewar baƙina babu mai ganina na gangara gefen titi,abinda naji mutanan suna faɗa yay matuƙar ɗagamin hankali ɗaya daga cikinsu ne ya ƙara faɗin "Dama ɗaya ce garemu dole ne acikin yara ukun nan mu ƙwashe guda biyu,to dole zargi zai shiga tsakanin yaya da ƙanwarsa,kaga zata kaishi ƙara ƙilama a yanke masa hukuncin kisa,daga nan mun gama da ita domin a plan ɗinmu babu ita zamu koma kan matarsa Khadija domin ɗaukan fansa" cikin tsoro na ƙara mai² ta kallamar “Fansa” wacce fansa? Shine abinda nake ta tunanin har lkcn dana rubuta wannan wasiƙar ban samu amsa ba,dan haka Lubna ƴar uwace a gareka Fahad “Afnerh” itace ƴarta amma bama mata kallon ƴar wannan Lubna itace farin cikina jin daɗina,bayan na gama jin abinda suke cewa har suka bar wajan ban kunna mota ta ba,bayan sun tafi na shiga cikin gida ina zuwa na tarar dukkansu suna bacci,ƴarta na ɗauka sannan na shiga ɗakin ƙanwata Khadija na ajjiye na ɗauki ɗaya daga cikin yaranta,kasan cewar kaya iri ɗaya ne a jikin jariran ga kuma yanayin halitta ɗaya abune mai wahala kasan anyi sauyin beby,nayi hakanne kuda sun ɗauke to bafa duk yaranta suka ɗauka ba,na salwantar da ran yarinta bisa farin ciki ƙanwata sbd Dr ya tabbatar ba zata sake haihuwa ba,tun cikin daren na tafi Matata na shaida mata kada ta kuskura kuda wasa ta ɗauki Nono ta bawa yarinyar domin bansan mai gaba zata haifar ba,cikin sa'a ba'a ɗauki beby ko guda ba sai kawai na share aka raɗawa yara suna inda nina zaɓi sunan Lubna sannan na zaɓi sunan ƴarta Afnerh, a lkcn da Mamana ta tabbatarmin ba zata auri Faisal ba saina yanke shawarar haɗa aurenta da ɗana Fahad a ranar da aka ɗaurawa ƴar uwarta aure da Faisal a ranar da daddare aka ɗaura auren Fahad da Lubna_ _Ban baka ita sbd yin kaina ba,a'a na baka ita sbd kasan cewarka jarumin namiji wanda zai zama jagora a rayuwarta,tabbas idan Mamana tayi kuka a dalilinka bazan faɓa yafe maka ba,na maka ita amana duk wahala duk daɗi kada ka sake ka rabu da ita kuda na kwana 2 ne,bare sakin aure,wannan wasiyyace_ _Wasiƙa ta biyu kuma kada ka sake ka buɗeta sai lkcn daka rasa mafita kumai ya tushe maka sannan zaka buɗa, wannan wasiya ce daga gareni_ _Alhaji Mustapha Rano_ _Sun/Dec/2020 10:30pm_ ~MSRN~ Musty na kawowa nan yana ya tsaya tare da jan numfashi,ninke wasiƙar yay tare da maidata aljihunsa,wajanne yay shuru kuwa da abinda yake tunani a ransa,Uncle mijin Mama ne yace"to masha Allah kai Sufyan sai kayi hqr tunda ba'a akan wani auren,daman shi aure nufin Allah ne kuma matar mutum kabarinsa,kuda ka aurenta idan ba baronka bace dole wani dalili ya tasu wajan zaku rabu da juna,Idan babu damuwa sai a maye maka gurbinta da ƴar uwarta Afner" Alhji ne ya amshe maganar tare da faɗin "Ai wannan ba abin damuwa bane da Lubna da Afnerh duk abu ɗaya ne,na amshi tayinka a matsayina na uba a wajan Sufyan" babu kunya wannan karan Alhji ya amshi auren Ɗansa Sufyan na mutane suke shaida ɗaurin auren *Sufyan Sulaiman ƙusawa da Afnerh Tijjani wambai* akan sadaki dubu ɗari cif,ana gamawa aka shiga raba alawa da goro nan akayi photuna taro ya ƙare,Fahad sun gaida da Khalid da kuma cousin ɗin mahaifiyarsa Fairus sun gaisa sama² sbd babu sabu a tsakaninsu musamman Fairus,zaman babbar rigarsa ya gyara tare da watsa wayoyinsa cikin aljihu,yana tafe yana kaɗa key ɗin motarsa,cikin nutsuwa da kamala yana gaf da shiga cikin gidansu sbd inda yake zaune masu wajan sundawo iyayen Fauwaz,yaji hankaɗesa tare da shaƙar wuyansa,cike da jarumta yasa hannu ya kaiwa Sufyan mari,zafin marin da ƙarfinsa yasa yay saurin sakin Fahad,cikin ɓacin rai Sufyan yace. "wlh kayi gaggawar rabuwa da my lovely bbyna idan ba haka ba,ka siyawa kanka tashi hankali wlh bazan taɓa bari ka mallaketa ba bare kayi tunanin ƙwanciya da ita"tunda ya fara magana Fahad ya lumshe idanunsa saida ya kammla sannan ya buɗesu tare mannasu a kan Sufyan murmushi kawai yay danshi kansa yana mamakin yawan murmushinsa yana jin zuciyarsa wasai,yayinda nauyin kansa ya tafe dukkan wata damuwa tayaye ba tare daya san dalilin hakan ba,juyawa yay zai tafi Sufyan yay saurin shan gabansa yace "Ka saketa nace,idan ba....," "Kadaman shirme ban waje naga lafiyar iyalina naji ɗumin jikinta"yana faɗin hakan ya juya tare da shigewa cikin gidan,bango ya kaiwa naushi tare da faɗin "i will kill u Fahad wlh zakai ladamar abinda ka aikata,wlh nizan fara sanin Lili before this is my promise"a zafafe ya juya tare da shiga mota ya bata wuta. Yana shiga cikin parlour yaga mutane sbd baison takura ya gaidasu a taƙaice yay flat ɗin Mama,yana zuwa ya ganta gaban wadrope tana fitu da kaya,a hankali ya ƙarasa wajanta tare da rungometa ya shiga juyi da ita a parlour'n,Mama wacce tsoro ya kamata amma ganin Fahad yasa ta saki ajjiyar zuciya,Tsayawa yay tare da lafewa cikin Mama,wular kansa ta cire ta shafa kansa cikin farin ciki tace "Yaro na wannan farin cikin na mene,tnx God kazu akan kari kafin Uwata ta huce,Lili kullum cikin kuka take ita Yayanta bata da aiki sai kiran sunanka"Lumshe idanu yay tare da taune jajayen laɓɓansa yana jin wani sanyi na ratsa jikinsa,zame jikinsa yay tare da zubewa a ƙasa yay (Sujudur shukkuri)ya daɗe yana wa Allah kirari kafin ya miƙe tsaye fuskarsa fal farin ciki ya shiga zaiyyanawa Mama abinda ya faru,kuka Mama ta fara saida tayi mai isarta yana kallonta bai hanata ba,"Allah sarki ya sadaukar da yaran ƴar cikinsa akan farin cikina,wannan sadaukarwa ba kowane zai iyayinta ba,Allah ubangiji ya jiƙansa yay masa rahama Ubangiji ya ƙyautata ƙarshensa halinsa na gari ya bisa,Rabbil izzatu ya haskaka kabarinsa"da Ameen Fahad yake amsawa a zuciyarsa jin Mama nason tasu masa da miƙin dake Fama dashi yay saurin cewa "Mama na gaji bacci"ya faɗa yana ƙwaɓe fuska,hararar wasa ta watsa masa tace "ok bari nazu na goyaka"dry yay wanda ya bayyanar da fararan jerarrun haƙwaransa masu ƙyau da tsari,murmushi daya haifar da lumawar Beauty points ɗinsa,sajen gemunsa ya shafa tare da jan gemunsa yace "laa bance ba,saidai kijira Ɗana wannan bayan nasa ne"baki ta saki tana mamakin rashin kunyarsa. "Yaran zamani nifa sirikarka ce,yawwa akwai event after magrib"shuru yay kafin yaja numfashi yace "no Mama banson tarin bidi'ar nan,a hqr dayi ayi walima da saukar alkur'ani"jinjina kai tayi domin ta gamsu da bayaninsa,kan bed ɗinta ya faɗa daman Mijinta ba nan yake ƙwana ba,duvet yaja ya rufe jikinsa tare da lumshe idanunsa,daman ya gawa Mama kada ta sanarwa da Lili komai,babu daɗewa bacci yay gaba dashi. Tunda aka sanar masu an ɗaura Auren Lili ta fashe da kuka haddasu birgima a ƙasa,rarrashin duniya su Fannerh sunyi tayi burus dasu,saida tayi mai isarta sannan ta miƙe tare dayin bedroom ɗinsa,cikin nutsuwa take tafiya amma kana ganinta kasan bata hayyacinta tana ƙoƙarin buɗe ƙofa ta shiga cikin bedroom ɗinta taji anyi saurin riƙeta tare da haɗata da jikin bango,tsoro ne ya kamata ganin Sufyan tsaye a gabanta kafin tayi magana ya haɗata da jikinsa tare da matseta ya shiga sauke numfashi,bakinsa ya ɗuran daman kunnanta yace "Lovely bbyna nayi missed naki,finally komai ya ƙare" ya yana tura halshensa cikin kunnanta ya shiga latsa,runtsa idanunta tayi da ƙarfi tana jin wani abu yana yi mata yawu a jiki, sam bata jin daɗin abinda yake mata ji take tamkar wuta ake watsa mata a jiki. Najma pov Ba ƙaramin hauka Najma tayi ba lkcn data tabbatar da Faisal ya mutu tayi kuka kamar ranta zai fita,da ƙyar aka lallaɓata hqr amma har zuwa yanzu bata da burin daya huce taga bayan Lili,wannan shine burinta tashi take ƙwana take tashi,yayinda kuma gefe na zuciyarta yake tunanin tarin kuɗin da mahaifinsu ya mutu ya bari wanda dana da tabbacin kuɗin sunnan kuma ta ɗauki alƙwari mallakar dukiyar gaba ɗayanta,hakan zai bata damar aikata abinda tayi niya ga kuɗin mahifinta gana mijinta daya bari,sosai take farin ciki da samun cikinta wanda take fata ace namiji zata haifa wannan shine zai bata damar yin abinda taga damar yi acikin gidan,a kuma ranar data haihu tana arba'in zata bar gidan ta shiga duniya neman Lubna mustapha Rano babbar maƙiyarta a duniya. *** *** Tsoro da fargaba sune suka cika zuciyarta yayinda take jin wani baƙin ciki ya cikata,tsoransa ya bayyana a ranta tasan abinda yake ba haram bane amma zuciyarta da ganggar jikinta sunƙi aminta da hakan,tana jin kamarta aikata ba dai² ba,jikinta ta shiga ƙoƙarin janyewa amma ta kasa sbd yadda ya ƙara matseta a jikinsa,cikin salo yake ƙoƙarin tura hannunsa cikin rigarta,numfashinta ne ya shiga ɗaukewa cikin fitar hayyaci ta fasa wata uwar ƙara wacce ta karaɗe gidan gaba ɗaya. Yana tsaka da baccinsa mai cike da nutsuwa baccin daya daɗe bai samu irinsa ba,yaji sauƙar ƙara a cikin kunansa,runtsa idanunsa yay tare da dafe kansa daya sara masa a lkcn wata fargaba ta saukar masa a zuciya,yayinda yaji gudun zuciyarsa ya ƙaru ba kamar ɗazu ba,addu'a yay tare da sake lumshe idanunsa yaja duvet ya ƙara lulluɓe jikinta, “Booby” yaji saukar muryarta kamar a mafarki,muryar da har abada bai taɓa manta sautinta ba,a suƙwane ya diro daga kan bed ɗin gaba ɗaya manta ko riga babu ajikinsa,da gudu ya ƙarasa isa parlour'n zuwansa yay dai² da ƙarasuwar Mama,Momma,Fannerh,Afnerh,Yusrah,Uncle Alhaji,Khalid,Fairus.. Sassauta riƙon da yay mata yay tana ganin hakan ta ƙwace jikinta da saurin still idanunta a rufe bata san wake gabanta,a haka ta shiga tafiya da sauri harta faɗa jikinsa ba tare data san waye ba,a tare suka sauƙe ajjiyar zuciya,laɓɓanta ya mannu akan tsinin jajayen nipples ɗinsa,lumshe idanunsa yay a hankali tare da zagaye hannayensa ya rungometa tsam a jikinsa,kuka ne ya ƙwace ba ta shiga dukan ƙirjinsa tare da girgiza kanta tunanin Sufyan ne,ganin abinda take ya tabbatar masa bata cikin hayyacinta,a sanyaye yasa hannu ya tallafu haɓarta tare da tura mata babban ɗanya tsansa a cikin bakinta. ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️ayi comments,ayi comments ko a wanne grp kake kayi comment zan gani kuma a shirye nake dana duba,wlh rashin comments zaija maku nayi sati banyi update ba,wattpad,wasapp,telegram,facebook,ai comments😍😅😅wlh hankali ƙwance zan tafi FADATA nayi ƙwanciyata. Juyayi fans Sarauta place Akafta🤾🏻‍♀️🤾🏻‍♀️🤾🏻‍♀️. *💖JYY💖* *40-41* ```NIMCYLUV🤏🏼``` *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ ```Wattpad``` https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb Ajjiyar zuciya ta saki tare da shigewa jikin Booby still tana dukan ƙirjinsa ba,lumshe idanunsa yay tare da ƙara matseta a cikin jikinsa yana jin yadda gudun zuciyarsa na ƙarauwa fiyeda da,sai yanzu ya tabbatar da bugun zuciyarsa da take bugawa da tunaninta bawai zumunci bane,soyayyace da kuma zallar ƙauna mara algus,ƙaddara babu ta inda bata haɗa mutum sai yanzu yasan ƙarfin ƙaddara yafi gaban haka,yarinyar daya ɗauketa matsayin ƙanwa uwa ɗaya uba ɗaya yau itace ta zama matarsa,matarsa ta sunna ta ina zai fara aƙwai tazarar shekaru masu yawa a tsakaninsu,ƙara lumshe idanunsa yay yana sauraran yadda take tsotsar yatsan sa kamar ta samu sweet,hannunsa yasa ya shiga bubbuga bayanta harya samu ta saurara da kukan sai sauke anjiyar zuciya take har zuwa yanzu taƙi yarda ta buɗe idanunta,sannu a hankali bacci ya shiga fisgarta jinta samu nutsuwa,Sufyan tunda ya kifa kansa a jikin bango bai ɗago ba,sai sauke numfashi yake da sauri idanunsa sun kala Tare da sauya kala,Mamace tace. “Yaro na” Maza ɗauketa zuwa ɗaki naga bacci ya fara ɗaukanta da alama wani abun ya bata tsoro"kasa ce mata komai yay sai cije lips ɗinsa da yay,ɗaukanta yay cak tare mannata da ƙirjinsa yana jin yadda numfashita ke dukan ƙirjinsa,cikin sauri ya nufi ɗakin Mama da ita yana zuwa ya sawa ƙofar key,derect toilte ya nufa da ita yana zuwa ya haɗa ruwan zafi a cikin bathtube yana gamawa ya sakata a ciki. Sauri buɗe idanunta tayi tare da ƙwaɓe fuska tsaye ta ganshi gabanta ya riƙe waist tare zuba mata narkakkun idanunsa wanda suka janye sbd baƙin cikin abinda Sufyan yay mata,da sauri ta miƙe da cikin ruwan sbd mamakin ganinsa a lkcn da matayi tsammanin ganinsa ba,yazu a lkcn da komai ya ƙare yazu a lkcn da zara fara rayuwa da mutumin da bataso bata ƙauna,kasa cewa komai tayi sai kuka data fashe dashi tare da faɗawa jikinsa ta ƙanƙameshi tare da cizonsa,runtsa idanunsa yay yana sauraran yadda take cizonsa haɗi da kuka,sosai kukanta yake taɓa zuciyarsa,ganin abinda bana ƙare bane yasa a hankali yasa haka tattusan hannunsa ya tallafu haɓarta,tsumamman idanunsa ya zubawa innoncet face ɗinta. Lumshe idanunsa yay naji wani abu a ransa wanda bai gama tabbatar da menene shi ba,hawayen fuskarta ya shiga goge mata tare suma rarrashinta ta hanyar bubbuga bayansa,ɗanya tsansa ta tura cikin baki ta shiga tsotsa tare da sauke ajjiyar zuciya ta nayi tana sakar masa cizo,saida ta gaji ta sakeshi tare da sauke manyan idanunta a kansa cikin muryar kuka tace. “Boobyna” Gira ya ɗaga mata ba tare da yay magana ba,sai yanzu ya fahimci zallar ƙuruciya a kan fuskarta,sam bazai iya ba,yana da tausayi yana jin tausayi mata masu ƙanan shekaru irin nata,tayaya zai iya rayuwar aure da ita harya sauke haƙƙinta dake kansa abunda kamar wahala,a hankali ya lalubar kallamar. “My sunshine bby” Turo baki tayi gaba tare da ƙwantar da kanta a jikinsa tana ji kamar zai ƙara guduwa yabar ita ɗaya,a yanzu bata jin zata jure rashinsa,tayaya zatar ruhinta da kuma bugawar numfashi taje ga son ranta? Wannan shine tamvayar da take ranta,cireta yay a jikinsa yace. "oya wanka i will be back soon" kaita jinjina ta suma cire kayanta a gabansa yay saurin fita tare da dafe kansa. Wani ƙyaƙƙyawan mari Alhaji ya kaiwa Sufyan cike da ɓacin rai ya ƙara ɗaga hannu da niya ƙara marinsa Khalid yay saurin riƙe hannunsa tare da faɗin "haba Alhaji wannan ba shine hukunci ba,dani daku kunsan cewa yana cikin hali na ɓacin rai da kuma kishi bai kamata ayi masa hakan ba,kai Sufyan kayi hqr kaje ka rungomi matarka sai Allah ya shiga lamarinka samakaƙon biyayyar da kayiwa iyayyenka"ɓacin rai yasa Alhaji yin shuru tare da girgiza kai,Momma ce ta kada baki tace "Sufyan kaban Mamaki hakan yana nuna zaka iya tarayya da matar wani ko,kasan cewa Lubna yanzu mallakin Fahad ce ba wakai ba,meye duk wannan abunda kake? Ba zaka iya sauya hukuncin ubangiji ba,wlh ka kiyayen na gaya maka"tana faɗin hakan ta shige flat tana jin ranta babu daɗi akan abinda ɗan nata ya aikata domin Uncle ya zayyane masu komai,cike da tashin hankali Afnerh tayi ɗakinsu yayinda Fannerh ta nufi ɗakin baki inda Mijinta ke jiranta,Yusrah ma bayan mahaifiyarta tabi tana jin zuciyarta a sunkushe,Uncle da Alhaji da Fairus sukayi waje,guri ya rage daga Sufyan sai Khalid. Kallon Sufyan Khalid yay kafin yay murmushin gefen baki yace "nasan zuciyarka cike take dason ɗaukan fansa ko baka faɗa ba,ninan zan taimaka maka wajan faruwan ƙudirinka"da saurin Sufyan ya kallesa yana mamakin abinda ya faɗa idan bai manta ba shiɗin ɗan uwane wajan Fahad ko yace Uba gaba ɗaya,amma tayaya zai taimaka masa wajan cikar burinsa,kafaɗarsa ya tafa yace "ka ganni wlh bana da imani babu abinda bazan iya aikatawa ba wajan cikar muradina,kai na taƙaice maka har akan kabari nasha ƙwana sbd wani ƙuduri nawa,dukkan wannan dukiyar da nake samu akwai JUYAYI a cikinta,kawai haɗin kanka nake nema"murmushi Sufyan yay tare da faɗin "tayaya zan mallaketa kafin shi?"shuru Khalid yay kafin yaja kunnan Sufyan ya raɗa masa wani abu,dry suka saka a tare kafin su fice daga cikin gidan. A sanyaye Mama ta tura ƙofar ɗakin da Afnerh take ciki sannan ta tura kanta tare da rufe ƙofar,ta daɗe tana kallon kafin ta ƙarasa inda take ƙwance tana kuka,hannu tasa ta jawota jikinta tare da share mata hawayen idanunta cikin muryar mai daɗi da kuma ƙyaƙƙyawan Lafazi tace "ashe ƴarta ba zata iya ɗaukan ƙaddara ba? Ashe ba zaki tawaƙƙali ki rungumi abinda yazu maki ba,ki sani ko Fahad ya soki ba zaku taɓa kasan cewa abu ɗaya ba,ke dashi jini ɗaya ne jinin dake gudana a jikinsa shine ke gudana a jikinki,Yarinta cikar imanin mutum shine yadda da ƙaddara,damu dake dama kuwa babu wanda ƙaddara bata tare dashi ina roƙanki Allah da Annabi ki rungumi aurenki kada ki bari ki faɗa fushin Ubangiji,Aure kimane daraja ne, kuskure kaɗan zaki ki shiga fushin Allah dana mala'ikunsa,Yarinta kiymin hakan a matsayina na uwa a gareki" kuka Afnerh ta fashe dashi tare da rumgume Mama cikin muryar kuka tace "na yarda Mama wlh na Amince zan zauna da Sufyan har lkcn da Ubangiji zai ɗuramin sonsa,dan Allah Mama ki tayani da addu'a"shafa kanta Mama tayi tace "Ubangijin Rahama yay maki Albarka Allah ya baki ikon riƙe aurenki da gsky da Amana"shuru tayi ta lafe a jikin Mama tana sauke numfashi wai duk wannan soyayyar dake tsakani za'ace ba itace Mahaiciyarta ba,lallai hukuncin Ubangiji yafi gaban komai. “Oyya tashi ki shirya ki amshi mijinki ina jin zasu ɗan ƙwana biyu a nan sbd gyaran gida ake masu,wancan sabbi Flat ɗin guda biyu zan buɗe a bawa Fahad ɗaya Sufyan ɗaya,zuwa jibi kayan da mumai order na furniture ɗinku zasu zo"jinjina kai Afnerh tayi tare da miƙewa ta shiga cikin bathroom,Mama kuma ta miƙe tare da ficewa. _1 week letter_ Ankai Amarya Fannerh gidan gida mai kyau da tsari,tare suke zaune da iyayen mijinta saidai flat ɗinta daban nasu daban,komai yana tafiya cikin farin ciki bata da matsala da kuwa. Wajan Sufyan da Afnerh babu yabu babu fallasa tsakaninta dashi gaisuwa idan ya fita tun safe sai dare zai dawo yayinda kullum suna tare da Khalid suna haɗa muna furcinsu,babu wanda yasan abinda suke aikatawa. Ƙwance take tsakiyar makeƙen royal bed ɗinta ta lumshe idanunta tare da dafe ƙirjinta,yau tun safe ta kejin tsoro da faɗuwar gaba wanda bata san dalilin hakan ba,ƙara curewa take waje ɗaya tunanin yayanta wanda yazu ya zama mijinta a yanzu,tana mamakin yadda har yanzu bai taɓa tunanin yin wani abu da ita ba,me hakan ke nufi kodai bai sonta ne? Shuru tayi jin babu amsa ita kam sosai take jin zuciyarta da gangar jikinta suna muradin wani abu wanda ta kasa sanin menene,tsakinta da Fahad saidai da daddare yaɗan matseta a jikinsa ya shiga cakuɗa mata gashin kanta a haka har bacci ya ɗaukesa,saidai tana lura dashi duk dare saiya haɗa tea mai lemon tsami yasha haka zaita juyi,taita tambayarsa mene saidai yay mata shuru ko kuma ya jawota jikinsa har bacci ya ɗaukesa,numfashi taja tare da ɗauko wayarta tace ta shiga cikin wattpad tayi searching sunan Sarauta (nikam nai dry nace wannan sunan nada banne kamar yadda zai fitu a special book ɗina wanda zuwa yanzu komai ya kammala,salonsa dana banne kamar yadda kuke ganin Juyayi,da Jiddah, wannan za kuyi kuka harku rasa hawaye🤣" Ganin bai bata result ba yasa ta rubuta _Nimcyluv_ murmushi tayi ganin sunan ya fitu littafai ta gani da yawa kawai hannunta ya sauka a kan book ɗin _SAI NA AURETA_ karantawa ta fara tana yi tana dry hartazu indai M.t ke aman jini akan dole saiya auri ƙanwarsa wacce suke uwa ɗaya uba ɗaya,yayinda ita kuma Diya keyin zauce da wani har mgnar aure ya shiga,nan hankali M.T ya tashi ganin da gske aurenta zai dan haka ya yanke wani hukunci a ransa,cikin isa da gadara ya nufi flat ɗin diya yana zuwa ya sameta ƙwance daga ita sai towel cikin sauri ya kashe fitalan ɗakin tare da nufar wajan. Tsaki ta ƙara ja ganin yay ending amma taji dɗi domin taga number marubuciyar sbd paid book ne,cikin sauri ta tura 1k ta accout data gani babu ɓata lkcn aka cillata a _NIMCY VIP GRP_ komai yawan littafan da tayi na kuɗi da wanda zatai nan gaba kana bada 1k za'a cikka ciki posting kullum babu fashi,wanda yake da sha'awa zai iya biyan 1k domin karanta littafanta na kuɗi dama wanda zasu zo nan gaba 0116886423 sulaiman Naima s secreenshot na shaida 08119237616 ga ƴan sarauta place zasu iya biyan 500 sbd zama na amana pls show me some luv yanzu dai covid 19 da sauƙi🤣😍. Bata gama ƙatun ba sai ana kiran isha'i ta miƙe tsaye zuciyarta cike da tsoro abinda ta karanta a book ɗin sai yanzu taji dɗi da Boobynta babu ruwansa,wanka tayi tare da ɗaura alwala,cikin sauri ta shirya fes cikin pech ɗin ƙaramin sket wanda iya karsa laps ɗinta,sai numa milk ɗin riga mai ƙaramin hannu,babban hijab ta zura tare da gabatar da sallah ta daɗe tana addu'a sbd bugun fargabar dake ranta. tana kammalawa ta miƙe tsaye tare da feshe jikinta da turare ta zauna tare da ɗaukan hisilun muslim ta shiga karanta kafin Fahad ya dawo. Misalin 8:30 ya shigo cikin gidan nasa cike da gajiya bai tsawa ko'ina sai bedroom ɗinsa yana zuwa ya ajjiye ledar chocolate data meat ɗin daya siyowa Lili,wanka ya shiga bai daɗe ba ya kammala ya fitu yana gamawa ya shirya cikin sauri tare da saka wando three gauter ya feshe jikinsa da arnar turare,yau tun safe yake jin wani feeling na tasu masa,dalilin hakan bai dawo gida ba sai yanzu,ko riga bai saka ba ya ɗauki kayan ƙwaɗayin daya siyo mata yay waje,a parlour'nsa ya tsaya tare da buɗe ɗan ƙaramin fridge ɗin parlou'r wata ƙaramar gorar ruwa ya ɗauka yana murza murfin ya buɗe babu tunanin komai ya kafa bakin gorar cikin nasa bakin saida ya shanye tas sannan ya rufe tare da ajjiyewa,lumshe idanunsa yay yana jin wata kasala na saukar masa ga wani masifaffan bacci da yazu masa,jiki a mace ya ƙarasa wajan duguwar sofa ya ƙwanta tare da ajjiye ledar hannunsa,nan take wani nauyayyen bacci ya ɗaukesa. Ta daɗe zauna tana chart a I.G kafin ta miƙe da nufin zuwa ɗakinsa sai taji sallamar Afnerh,murmushi tayi mata nan suka zauna a saman sofa suna shira kafin Afnerh ta miƙa mata wani juice tace "nasan wannan shine fovarite juice ɗinki shiyasa na kawu maki"cike dajin daɗi Lubna ta karɓa tare da faɗin "ayya aikam ngd sosai ƴar uwa kamar kinsan tun safe babu abinda na sawa cikina"tana faɗin hakan ta ɓalle murfin rubar tare da kafata a bakinta ta shiga ƙwanƙwaɗa saida tasha fiye da rabi sannan ta miƙawa Afnerh tace "amshi kema kisha ƴar uwa"kaɓa Afnerh tayi tare shanyewa tana mamakin abinda yasa Sufyan yace ta kawowa Lili bayan ita bai bata ba. Can cikin dare da farka da wani matsananciyar sha'awa mai ƙarfin gaske,numfashi ta shiga fitarwa a wahalce tare da mamakin abinda ya rabata da ɗakinta ya kawota nan,tana cikin wannan halin taji an turo ƙofa tare da shiguwa bata damu da ganin ko waye ba,dan tasan babu mai zuwa wajanta a irin wannan lkcn sai mijinta,runtsa idanunta tayi tana jin wata a zaba a ƙasan mararta,hasken ɗakin aka kashe tare da suma takawa zuwa gareta,yana zuwa ya haura saman gadon tare dasa hannu ya jawota cikin jikinsa,yana jin wani daɗi da sanyi na ratsa zuciyarsa yau zai cikar muradin ransa na tsayin wani lkc,gyara mata ƙwanciya Sufyan yay tare da ta ƙoƙarin rabata da kayan jikinta,wata ajjiyar zuciya ta sauke tare da lafewa jikinsa jin tana samun ɗan sauki daga felling pain ɗin da take ji,sosai surar jikinta ta zautar dashi dan baiyi tunanin hakan ba,a haukace ya ƙwantar da ita tare dayi mata runfa,gaba ɗaya jikinta rawa yake sbd jin sabon baƙwan yanayin da ba tayi tunaninsa nan kusa ba,jin abinda yake bata ya ƙara bata tsoro cikin fitar hayyaci tace. “banso” Ta faɗin hakan tana girgiza kanta tare dakai masa duka,ganin abinda take yasa yay saurin sanya bakinsa cikin nata ya shiga bata sumba,cikin zauvewa haɗi da ɗimuwa ya shiga neman hanya,raɗaɗi da azabar data jine yasa ta sakar masa cizo,amma ko ajikinsa,ƙara suka saki a tare yayinda tai ihun zaba shi kuma yay ihun samun nasarar shigewa jikinta,sabbatu ya fara tare da faɗin "wayyo...ni..Sufyanu..gsky lovely bbyna kinyi..da ban sameki ba wlh mutuwa zanyi...gsky Fahad kai lusari ne ka shanye maganin dana baka tass cikin ruwa...yanzu nine winner nina..amshi..virgin ɗin Lubna..saini Sufyan namijin duniya daman na gaya maka saina mallaketa kafin kai..."yana faɗin hakan ya saki kuka tare da ƙara shigewa jikinta. *💖JUYAYI💖* *42-43* ```NIMCYLUV🤏🏼``` ```Wattpad``` https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ Sadaukarwa ga masoyana da kuma masoyan _😍JUYAYI_ ina jin daɗin comments ɗinku da kuma soyayyarku I really appreciate thanks for luv and care _SARAUTA👸🏼_ na maku sahihiyar ƙauna 💋🥰 A ɗan firgice Fahad ya farka daga baccin daya ɗaukesa,yana mamakin yawan baccin da yay ba tare daya duba lafar ƴar mutane ba,miƙewa yay a hankali hannunsa dafe da goshi ya nufi ɗakinsa jin an fara kiran sallah,yana ƙoƙarin shiga bedroom ɗinsa ya fara jiwo saurin kukanta tare da gurnanin mutum,zuciyarsa ce ta bada sauti damm,cikin sauri ya runtsa idanunsa tare da fara kiran sunan Allah,jikinsa gaba ɗaya ya ɗauki rawa ƙirjinsa ya shiga ɗagawa sbd fargaba da kuma tsoro,cikin mutuwar jiki ya ƙarasa shiga ƙaramin parlour'nta a nan ya ƙarajin sautin kukan ya kuma ƙaruwa,da gudu yay hanyar bedroom ɗinta yana zuwa ya tsaya cak sakamakon jin sautin surutan mutum tare da sambatu,a hargize ya biɗe ƙofar da sauri tare da shigewa ɗakin,kasan cewar ɗakin duhu garesa ya shiga lalubar maƙunnin ƙwan,cikin sa'a ya gani tare da kunnawa "innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" shine abinda ya samu nasarar faɗa a fili,wannan abun shine ya dawo da Sufyan daga duniyar daya lulaa,cike da farin ciki da jin daɗi ya zare jikinsa bai damu da duba halin da take ciki ba,yana tashi yay saurin saka jallabiyar jikinsa,zubewa Fahad yay a ƙasa tare da lumshe idanunsa,wasu hawayen baƙin ciki suka shiga zubu masa,wani ɗaci da zafi ya keji a zuciyarsa yayinda ya kasa ɗaga koda hannunsa ne,sunayen Allah kawai yake kira babu ƙaƙƙautawa har saida ya samu nasarar ɗaga jajayen idanunsa tare mannasu a kanta,saurin ɗauke kai yana faɗin "Hasbunallahu wani'imal wakil Astagafirullah" yana faɗin hakan wasu hawayen suka ƙara zubu masa yana ƙara girmama ƙarfin rashin imani irinna Sufyan,wani murmushin baƙin ciki yay yace. “Wait” Sufyan na gafda ficewa a ɗakin yaji saukar muryar Fahad a kunansa,cike da gadara ya tsaya tare da faɗin "nasan baƙin ciki shine zai silar barinka duniya,tabbas yau ina cikin farin ciki wanda ban taɓa shiga irinsa ba,yauna cika muradin raina da kuma zuciyata,na bawa abinda gangar jikina ta daɗe tana muradinsa da kuma farkinsa,nasan abinda ciwo amma yana iya ƙwaɗayina bai tsawa kan kuwa ba sai matar aure matar da abokin gabana,am telling ai nizan fara amsar virgin ɗinta saika ƙarasa da raguwa ko?"takaicine ya cika zuciyar Fahad ya kasa ce masa komai,wajan 3min kafin ya miƙe tsaye cike da jarumta ya taka har gaban Sufyan yace "tabbas kayi nasarar amsar virgin ɗinta amma kasani kayiwa kanka domin ance idan zaka gina ramin mugunta ginashi dai² tsayinka,kafin ka tafi sai kaje ka ɗauki matarka a ficemin daga ɗaki" saurin kallon bed ɗin yay inda ya hangota ƙwance sai sauke numfashi wahala take bacci yay gaba da ita yayinda idanun yay faca² da hawaye,cikin ƙaraji yace. “What Afnnerh how can dat happen no wlh Lili nai rapping ba matana ba”Kafaɗa Fahad ya ɗaga tare da faɗin "banson surutu ka ɗauketa ka ficemin a ɗakin mata,kuma ka ɗauka wannan wasan namu yanzu ya fara wlh ka kiyayi kanka fushina ya kufce a kanka ban iya hauka ba,banza wawa wanda baisan darajar aure ba,kada ka manta komai kayi sai anyi maka wlh wlh dana san haka halinka yake bazan taɓa bari a ɗaura maka aure da ƴar uwata ba,sakalan banza get lost da Allah"wani abu mai ɗaci ya haɗiya kafin ya kalli Fahad yace "bana yafiya ba kuma zan taɓa yi a kanka ba,amma zan baka wata fitila domin ka haskawa kanka idan ka shiga duhu,bani kaɗai ne mai buri a kan Lili saika zage damtse game ɗin yanzu aka fara"yana faɗin hakan ya huce kan bed ɗin babu kunya yasa hannu ya ɗauki Afnerh wacce take baccin wahala"yawwa sai anemi ruwan zafi da gishiri a sakata idan kuma an samu ɗinki muna zauna mu Likitoci a iya nemanmu,munsha tabara munsha yasin tun acikin mahaifa dan haka notin happen with me"yana faɗin hakan ya zabe akan stool tare da dafe kansa take juya masa ga kuma yanayin yadda maƙoshinsa ke zafi sbd yawan maganar da aka sashi a wannan asubar,lallai ya kamata yasan me yake aurensu wajan sati zuwa sati biyu ko kiss bai taɓa yiwa matarsa ba bare wani abu,yana tunanin ba zata iya ɗaukan ɗawainiyarsa ba,amma gashi wani mahaukaci yana son karɓar abinda ba mallakinsa ba,ya tabbatar da Sunshine bbynsa akaiwa haka zuciyarsa bugawa zatai ya mutu sbd baƙin ciki,ya daɗe a zaune yana tunani kala² kafin ya fara tunanin inda take,miƙewa yay tare da nufar toilet yana zuwa yaga nanma bata nan,cikin sauri ya fice daga sashen nata ya nufi nasa sashen hashe ya kunna a ƙaramin parlour'nsa nanma bata nan cikin sauri ya danna kansa cikin bedroom ɗinsa tare da kunna shake,wata ƙatuwar ajjiyar zuciya ya sauke sbd hangota da yay tsakiyar royal bed ɗinsa ta cure waje guda tare da rumgome pillow yadda ta rumgome pillow zai tabbatar maka da bata sama bacci ita ɗaya ba sai dole,yadda take bacci zai nuna maka ayi mata sabu da ƙwana jikin mutum,mutum ɗinma wanda take samun nutsuwa dashi,a nutse ya taka inda take tare da zama a gefen bed ɗin,hannayensa duk biyu yasa tare da jawota cikin,sassayar ajjiyar zuciya ta sauke ta shiga turo bakinta tare mamula ita a dole ayi mata ba dai² ba,lumshe idanunsa yay yana jin wani matsanancin sonta da ƙaunarta na ƙara shigarsa,ji yake kamar ya tsaga zuciyarsa ya turata ciki koya huta,zai iya ɗaukan ko wacce ƙaddara amma banda ta rabuwa da ita,ya tsansa yasa ya shafi cute lips ɗinta data jiƙashi da sliva,gashin kanta ya shiga shafawa a hankali tare da ɗura bakinsa kunnanta cikin wata salon murya yace "wake up my nurulyahat lkcn ibada yayi"gajiyayyun idanunta buɗe tare da saukesu a kansa,saurin rufewa tayi sbd yadda mararta ta ƙarta mata ga wani irin hanayi data tsinci kanta tunda tasha wannan juice,tura baki tayi gaba tace “Boobyna” zuba mata rikitattun idanunsa yay ganin yadda take ta lumshe idanu,ganin lkc naja ya janyeta a jikinsa yace "oya tashi"yana faɗin hakan ya shige toilet ya watsa ruwa tare dayin brush ya ɗaura alwala,yana fituwa itama ta shiga kafin ta fitu ya gama shiryawa cikin wata jallabiya sai zabga ƙamshi yake domin turaren asubarsa nada banne,tana fituwa yay saurin kamata tare da zura mata wata ƙaramar jallabiyarsa,zuruf ta shigeta sai yawo take a ciki,hancinta yaja yace "yarinya tana munna tasa kayan mijinta" washe baki tayi saida ya gama shiryata tare da gyara mata gashin kanta sannan ya jasu sallah dan bayajin zai iya fita ya barta,ya daɗe yana masu addu'a mai ƙyau tare da azkar sannan ya shafa yace ta ƙwanta yana zuwa,yana fita ya sawa ƙofar key,babu inda ya zame sai ɗakin Lili bedsheet ɗin ya cire tare da cillashi injin wanki,cikin ƙaramin lkcn ya gama ƙyara ɗakin sbd baison Lili ta fahimci wani abun yana gamawa ya koma ɗakinsa,zaune ya ganta ta dafe ciki,rigar jikinsa ya cire yana zuwa ya sunkuceta tare da ɗurata akan ruwan cikinsa yay copping face ɗinsu yace "ƴar ƙwailata ya akaine ko kina buƙatar wani abune"tsura masa idanu tai tabbas akwai abinda take buƙata amma Mene? Wazai bata? Ina zata sameshi" kaita girjiza masa cikin rawar murya tace "babu amma meye ƙwaila?"gira ya ɗaga mata babu kunya ce "wacce bata da brest"tura baki tayi tace "to aini inda...!" sai kuma tai shuru tare da kulle idanunta,sbd nauyin abinda tayi niyar faɗe,dry yay kaɗan yace "kina dashi lemme see" ya faɗa yana tura hannunsa cikin jallabiyar jikinsa,sauri riƙe hannunsa tayi jin wani abu nayi mata yawo,girgiza kai kawai daman wasa yake bata,shuru yay tare da lumshe idanun yana tunanin yadda zai bata farin ciki kamar ko wacce mace yana tunanin yadda zai sauke haƙƙin dake kansa dan yasa idan yace zai bata haƙƙinta tabbas zata sha wahala domin yafi kuwa sanin kansa,yana wannan tunanin yaji tana shafa jajayen lips ɗinsa tare da tura ya tsanta ciki,numfashi yaja mai ƙarfi jin yadda tsigar jikisa ta miƙe,buɗe idanunsa yay cikin daƙushasshiyar murya yace "kina sone"kaita ɗaga masa cike da buƙatuwa dan harga Allah bata ɗauki hakan wani abuba,mirginata yay ta koma samansa shi kuma yay mata runfa,hannu ya zura ta ƙasan wuyanta tare da tallafu kanta ya zamana fuskarsu tayi kusancin data juna yadda ta tsura mata idanu ne yasa ya girgiza kansa tare dasa hannu ya rufe mata idanu shima yaja nasa ya rufe,a hankali ya kusanto bakinsa wajan nasa,cikin salo mai ɗaukan hankali ya sanya lips ɗinsa na sama cikin nata bakin yayinda lips ɗinta ya ƙasa ya shige cikin bakinsa,numfashi ta fisga ta sauri jin numfashi ya ɗauke,a hankali ya shiga sucking lips ɗinta tare da zugar yawon bakinta,ƙanƙamesa tayi jin wani abu nayi mata tafiyar tsotsa,littafin IZZAR SO ne ya faɗu mata lkcn da Omehi ke kissing ɗin Mijinta Yarima Sudais ya batare da zato ko tsammani ba,yaji ta cafki lips ɗinsa ta shiga tsotsa. Cikin wannan halin bacci ya ɗaukesu cike da so da ƙunar junansu,masu farka ba sai 11 na safe shine ya fara farkawa bakinsa ɗauke da addu'a,a hankali ya zare bakinsa daga cikin nata peak yay mata a goshi sannan yaja mata pillow tare da rufeta da duvet,bathroom ya shige tare da haɗa ruwan zafi yay wanka sosai tare da brush ya nayi yana lumshe idanunsa sbd wani daɗi dake ratsa sa,duk wani juyi da yay sai yaji gaɗi da zaƙin sliva ɗinta,a haka ya kammala ya goge jikinsa tare da busar da gashin kansa,yana kammalawa ya lemi lotion mai daɗin ƙamshi ya shafa haɗi da fesa body spray,wajan wadrobe ya nufa tare da ɗauko milk ɗin yadi mai ƙyan gske,cikin sauri ya saka kayan masha Allah yay ƙyau sosai musamman yadda milk ɗin yadin ya amshi farar fatar jikinsa,tsarin ɗinkin yay dai² da surar jikinsa ƙaramin hannune da rigar yayinda tsayin rigar ya tsaya masa iya ƙasan waist ɗinsa,bakin toms na zama ya ɗauka ya saka tare manna agogon apple a hannunsa,bluetooth ya manna a kunansa cikin sauri ya fesa turare Ohud a jikinsa,wajan da take ƙwance ya ƙarasa yana zuwa ya sakar mata sumba cikin sauri ya fice daga ɗakin tare dajan ƙofa ya murza key daman ya bar mata wani a gefen bed. Babu inda ya tsaya sai parlou'n Mama yana zuwa ya ƙara wajanta tare da gaisheta kansa ta shafa tace "lafiya lou Yaro na ya katashi Ubangiji ya tsaremin kai da tsarewarsa"murmushin jin daɗi yay tare da jinjina mata kai yace "Mamana tuwon shinkafa nakeso miyar wake pls, sai ƙwadon zagula asa tumatir mai kyau"dry tai masa kafin ta watsa masa harara tace "ina matarka?"shafa kansa yay baice mata komai miƙewa yay tare dayi mata sallama yana ƙoƙarin ficewa tace "kaga na mance ƴar uwarka Afnerh babu lpa ɗazun suka dawo daga asibiti yanzun haka Mommace a wajan ko zaka leƙa?"girgizai yay tare da faɗin "Allah ya bata lafiya"yana faɗin hakan yay waje tare da faɗawa motar cikin sauri ya harbata waje tare da sakin suratul Maryam cikin muryarsa mai daɗi ya shiga bin karatun harya ƙarasa hospital. Afnerh kam sosai tasha jiki dan ƙashinta baiyi ƙawarin da zai ɗauki abinda Sufyan yay mata saida akai mata ɗinki kafin kace me zazzaɓi mai zafi ya rufeta,aikam yasha faɗa wajan Momma daga ƙarshe ta ɗauketa tare da maidata sashinta,cikin iƙon Allah tausayinta ya ɗarsu a zuciyar Sufyan tare da kuma ƙaunarta danta bashi mamaki,amma bazai nuna yana sonta ba sai lkcn daya samu cikar burinsa,da wannan tunanin shima ya fice daga cikin gidan. Lili bata farkaba sai wajan 12 da sauri ta faɗa wanka tana gamawa tayi sashinta ƙwaliyya ta yarfa cikin green less ɗikin riga da sket sosai ɗikin ya amshi jikinta yay mata das,gashin kanta ta gyara sannan ta ɗauki ɗan ƙwali tayi ɗaurin ture kaga tsiya,haka nan ta samu kanta da shafa beby lipstic ya ƙara fitu da cute lips ɗinta,ma dai² cin mayafi ta ɗauka ta yafa a jikinta tana kammalawa ta nufi waje,tana zuwa tayi ɗakin Mama samunta tayi tana sallar azahar saida ta gama sannan ta gaisheta,ɗan waskewa Mama tayi zuma ta ɗauko ta miƙa babu musa ta amsa tare da shanyewa sannan ta bata turare tace saita ƙwanta bacci,nan dai ta zauna wajan Mama har la'asar kafin su shiga kicin gaba ɗayansu a haka suka kammala tuwan shin kafa da miyar wake wacce taji naman gaza,sannan suka haɗa kayan ƙwaɗon zugalar tare da ajjiyeshi saiya dawo a haɗa masa. Bai dawo gidan ba saida yay sallar isha'i sannan ya shigo a gajiye ya zuɓe a parlour'n sbd yunwa,nan Mama ta kawo masa komai gabansa sakkowa yay ƙasan carpet ya miƙe ƙafafunsa,Mama tashi tayi ta nufi ɗakinta,yana ƙoƙari faracin abincin ta fitu daga ɓangarensu sanye cikin ƙaton hijab wanda yay mata ƙyau sai zabga ƙamshi take,sosai yaji daɗin ganinta a haka hannaye ya miƙa mata,cikin kunya ta ƙarasu wajansa tare da zama kusansa tace "ina fatan farin cikin Lubna ya dawo cikin yarda da amincin ubangiji ya hanya"lumshe idanunsa yana jin daɗi kalmanta,gira ya ɗaga mata yace"lafiya lou ƴar ƙwailata" basu rufe baki ba Sufyan ya shigo ganinsu a parlour'n yasa ya zauna tunaninsa zai takurasu,Fahad dryr mugunta yay kana ya saka hannu ya jawota zuwa jikinsa cikin nishaɗi yace "ok tunda ba ƙwaila bace bari naji"sauri riƙe hannunsa tayi kana cikin shagwaɓa tace "no! Pls" ƙansa yay da ƙasa tare da fitu da tongue ɗinsa yace ohya take ur sweet"kamar jira take ta cafke ta shiga tsosa,lumshe idanunsa yay yana jin wani mahaukacin feelings ya tasu masa daurewa kawai yake,bango Sufyan ya kaiwa naushi tare da fitar da wani huci ko cikin gidan bai shiga ba yay waje,yana fita Fahad ya cire bakinsa ana Lili lkcn idanunsa ya gama sauya kala,sauka tayi daga jikinsa tare da zuba masa a bincin plate sai ruwa a ruba hannunsa ya wanke tare suma cin abincin itama hannu tasa sunci abincin sosai sannan Mama ta kawo masa ƙwaɗan zugalan a nan kallo ya komai sama dan har kuka akai tsakanin Fahad da Lili lkcn da zugalan yazu ƙashe da sauri ya ƙashe ya tura bakinsa kuka ta fashe dashi kafinta faɗa kansa ta shiga kukawa,saida ta samu nasarar saka bakinta cikin nasa ta ƙwaso na ciki ta cinye,dry yay mata sosai,miƙewa yay tare sosa kai yace "Mamana saida safe"harara ta watsa masa ba tare data ce masa komai ba,hannun matarsa yaja tare dayin sashinsu,yana zuwa ya saki hannunta ta sameshi zai watsa ruwa,itama wanka ta sauya tare da shafa turaren da Mamata bata,duguwar rigar bacci ta saka wacce tazu cinyarta kana ta saka bby hijab ta rufe ƙofar sannan tayi sashin,a zaune ta samesa yana danna P.c da alama aiki yake mai muhimmanci wajansa ta ƙarasu tare shigewa jikinsa ta ƙasa ta zuba p.c idanu can tace "booby" a hankali yace "what?" kallonsa tayi tace "why kake ƙwashe documents ɗinka zuwa wani accout ɗin" amsa ya bata a taiƙaice yace "just" ok kawo kaga wani abu p.c ya bata ta shiga dannawa cikin ƙwarewa tana ji yana cire hijab ɗin jikinta,ƙwashe komai tayi ta turasu ta email ɗinta sannan ta saka pin tana gamawa ta kashe tare da ajjiyeta cikin hamma tace "bacci" ɗaukanta yay suka nufi bed ɗinsa,hasken ɗakin ya kashe a hankali ya jawota jikinsa yace "Lubna" sauri kallonsa tayi domin bata taɓa jin real name ɗinta a bakinsa ba kasa amsa masa tayi tana jin lkcn daya shammaceta ya cire rigar jikinta,cikin rawar murya yace "i need you..pls don't cry" kaita ɗaga masa tsoron daya fara shigarta ganin yadda yanayinsa ya sauya lkc guda jikinsa ya fara musamman yadda yaga albarkatunta ba ƙaramin girgiza sa yay ba,rumfa yay mata cikin nuna shin jarumin namiji ne ya haɗe bakinsu ya shiga bata lafiyayyar sumba mai tsayawa a ran duk wanda akaiwa,martani ta fara basa hakan ya taimaka wajan rikicewa ya shigayin romance ɗinta gaba ɗaya ya manta dawa yake tare,ɓangarewa tayi jin yadda yake mata tafiyar tsotsa,wasu hawayene suka shiga fita daga idanunta jikinta ya ɗauki rawa,a hankali yake yawo da hannunsa a sassajan jikinta yanayi yana manna mata laifiyyyan kiss,ƙanƙameshi tayi lkcn da taji saukar bakinsa akan...Fahad yi yake like a child wanda mamansa take feeding nasa,yanayi yana shafa ƙasan mararta a hankali wasu hawaye suka fita daga cikin idanunsa suka sauka kan fuskarsa,saurin runtsa idanu tayi kafin tasa hannu ta goge masa hawayen ta shiga girgiza kanta,lumshe idanunsa yay lkcn da yake ware legs ɗinta cikin daƙushasshiyar murya yace "i'm sorry pls for give me" yana faɗin hakan lkcn da yake karatu addu'ar ƙwanciya da iyali "بسم الله الهم جننبنا الشيطان و جنب الشيطان ما رزقتنا " yana faɗin hakan yay saurin haɗe bakinsu tare da shigarta,tashin hankali abinda yaji shine yasa yay saurin sakin bakinta tare da kifa kansa tsakanin ƙirjinta ya fashe da kuka. _book 1 is ending bu haɗe a paid grp domin samun book 2🤣🥰kada ko manta akwai VIP grp ɗina wanda zaku samu littafan kuɗi da nayi,mai makon ko wanne guda a bada 300 saina haɗe a bada 1k da guda biyun da nayi na baya da kuma guda biyun da zanyi na gaba🤏🏼👌🏻300+4 =1200 amma an cire 200 ya koma 1k kawai👌🏻idan guda kuma kakeso 300 shine,ci gaban JUYAYI kuma 500 kawai🙌🏻😍ai nayi kirki kun sanni badai adalci ba, domin shiga VIP grp zaka bada 1k a turo ta accout no 0116886423 Sulaiman Na'ima s, union bank sai shaidar biya 08119237616 sai a tsundu maka NIMCY VIP grp wanda za'a dinga bawa ta prvt kuma zasu bada 1300 my guys nasan zaku iya ina tare da hajiyoyi😍🤣kuma babu corana dan haka saina jiku ku sani JUYAYI yanzu aka fara wasan🤾🏻‍♀️ mene yasa Fahad kuka? Bayan fitar Sufyan maiya aikata? Kuna buƙatar wannan amsar dan haka dole ku kasance dani san so nake maku kuma sahihiyar ƙauna wanda yake da shawara yana iya yimin mgana prvt thanks for the luv💋_ *💖JUYAYI💖* *44-45* ```NIMCYLUV🤏🏼``` ```Wattpad``` https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ 😍😝sorry Fans i knew hantarku ya juya so sorry dana saku a confuse na shirya maku surprise me i luv you all Kuka ne mai nuni da tsantsar soyayya ƙauna da kuma zallar tausayi,sai yanzu ya ƙara girgimama hukuncin Ubangiji,yana iya komai aduk lkcn daya ga dama,babu shakka Allah shine abin gdy da kuma girmamawa,a yau matar daya kewa kallan ƙanwa a wajan ita ta zama a wajansa wacce yake saran zata haifa masa ƴar ƴar masu yawa da kuma tarin albarka,bai dama jin kansa a matsayin mutum mai cikakkiyar lafiya ba sai yau,sau tarin yakan tambayi kansa why baya son wata macen mai yasa baya da feelings da kuwa,ashe bugun zuciyarsa da kuma falkinsa itace rauninsa itace mai bashi barin ciki daga duniyar wanda yake fatan ace har lahira,lumshe idanunsa yay a ƙaru na biyu ya ƙara gwada shiga jikinta amma babu hanya wannan abun ba ƙaramin ɗaga masa hankali yay ba,yakai matakin da bazai iya hqr ba yana jin idan bai shigeta ba zai iya samun matsala da zuciyarsa haɗi da gangar jikinsa,babu yadda ya iya domin rabuwa da ita shine mafita tunda ya riga yasan matsalarta,ajjiyarsa zuciya ya sauke tare da mirginawa gefe ya juya mata baya,lips ɗinsa ya shiga taunewa sbd a zabar da mararsa take masa shikansa yasan yana buƙatar matar amma dole yay hqr zuwa lkcn da zai mata aiki shida kansa _(akwai irin mata da ba'a cire masu bile lkcn suna jarirai,idan har suka girma da ita haka babu yadda za'ai namiji ya raɓesu dole sai an masu aiki wannan matsalar ita ta samu Luban hakan zai tabbatar masu da she still virgin🤙🏼)_ tsoran daya gama ratsa tane yasa tayi saurin jan blanket ta rufe naked body ɗinta,gaba ɗaya jikinta rawa yake yayinda take jinta a cikin wani irin yanayi mara fassaruwa,a hankali ta ƙara shigewa cikin bargun tare da sakin kuka domin abun ya gaza ɗaukan hankalinta gama ɗaya wani abune mara daɗi yake mata yawo a jiki,ga yadda nipples ɗinta yake mata wani zafi da zugi sbd wahalar daya shafa,hannu tasa ta matse mararta wacce ta kumbura hakan ya nuna jikinta ya amshi sabon yanayin daya sameta kuma a shirye suke da ɗaukan abun, _(wannan ma hurumina bane dana faku wata fatawa😍🥱amma ƴan grp ɗin vip ɗina gada ku damu zaku samu maiso a dama dashi come and pay 1k only)_ dashin da taji a ƙasanta shine ya ƙara mata tsoro wanda ya sanya ta ƙara fita hayya cinta kukanta ya tsananta haka ya taimaka numfashinta ya suma shaking tare da suma ɗaukewa,zazzafan zazzaɓine ya rufesa ya shiga haɗa bakinsa jikinsa ya suma rawa sbd yadda ƙofufin jikinsa suka buɗe gargasar jikinsa ta mimmiƙe,hannu ya sanya ya dafe saman forehead ɗinsa dake bara zanar tarwa tsewa gida biyu sbd tsananin zafi da ciwon dake masa,ƙara runtsa idanunsa yay jin yadda take fitar da numfashi ƙirjinta na sama haka ya tabbatar masa da asmarta keson tashin,cikin dauriya da jarumta yaja jikinsa zuwa gareta a hankali yasa hannu ya jawota jikinsa tare da rufe masu jiki da duvet matseta yay sosai a jikinta,a sonsa na dawo mata da numfashinta ya lalubu bakinta ya sanya cikin nasa ya shiga wura mata iskar bakinsa tare da ɗan danna mata ƙirjinta sama²,wajan 5min ta saki wani wahalallan numfashi ta buɗe baki zata saki kuka yay saurin sakar mata wata haɗaɗɗiyar sumba a tsakiyar bakinta,sanyin daɗin abinda taji duk bata cikin hayyacinta yasa ta lafe jikinsa ta shiga sauke numfashi sun ɗan jima a haka yaji saukar numfashinta a ƙirjinsa hakan ya bashi damar zare bakinsa daga ɗata,ƙwanciya ya gyara mata lumshe idanunsa yay wannan lkcn shine ya dace daya fara fahimtar wani abu wannan lkcn ne ya dace ya ɗauki fansar ran iyayensa ta hanyar gano wanda suka aikata hakan,da wannan tunanin bacci mara daɗi ya ƙwashesa. Lkc guda suka farka da asuba mai tsaya jiran komai ba ya ɗauketa tare da nufar toilet da ita ruwan zafi a bathtube ya sakata kuka ta saka masa akan ruwan yay mata zafi bai kulata ba saima ƙoƙarin zare ɗan boxer dake jikinsa yay da sauri da kulle idanunta dan bata jin zata ita ganin surar jikinsa gefe guda kuma tana girmama rashin kunyarsa,tana jinsa ya gama wanka tare dayin alwala ta ɗaura towel a jikinsa,murmushi yay mata cikin murya mai sanyi yace "nikam na banu bayan kin kasance ƙwaila ashe hadda ƙauyanci mijin naki kike kunya" yana faɗin hakan ya fice a toilet,ajjiyar zuciyata sauke sbd tsoran daya gama ratsa,ƙirjinta ta kalla taga irin baiwar da Ubangiji yay mata amma a haka yake kiranta da ƙwaila,cije lips tayi lkcn data tuno moment ɗinsu na jiya,saurin haɗe jikinta waje guda tayi jin tsigar jikinta na tashi wani feelings ya ratsa jikinta,tunanine kala² a ranta ita dai yadda take jin labarin aure da kuma abinda yake faruwa tasan ba haka bane ya shiga tsakaninta dashi,bata kai yay hakan da ita bane komai? Sonta ne ba yayi komai haka nan taji ranta ya ɓaci a kasalance tayi wanka ta fitu lkcn ya daɗe da fita masallaci,a nan ya samu lbrn Alhajinsu Sufyan ya koma nigeria domin gabatar da wani compny,Uncle kuma ya koma wajan aikinsa,yayinda Khalid da Fairuz suka huce gida,ya daɗe cikin masallacin saida rana ta fitu sannan ya miƙe tare da shigewa gida,dicret kichen ya nufa yana zuwa ya haɗa coffee yasha daga nan ya gaida Mama sannan ya huce sashinsa,ganin bata ɗakin yasa ya huce sashinsa ya watsa ruwa cikin sauri ya gama shirya cinin wata dakakkiyar shadda amy colour sai baza ƙamshi yake,da sassarfa ya shiga ɓangarenta ƙwance ya sameta tana bacci hakan yasa bata light kiss a lips ɗinta sannan ya fice a gidan. Buɗe manyan idanunta tayi tare dasa hannu ta shafi laɓɓanta wajan da yay mata kiss pillow'n kusa da ita taja tana jin wata ƙaunarsa na ratsata amma wani gefe na zuciyarta taƙi aminta da abinda yay mata a matsayin wani babban dalili,shiyasa tayi pretending kamar bacci take,miƙewa tayi tare da zura ƙaton hijab ɗinta ta nufi ɓangaren Afnerh,a ƙaramin parlour ta sameta tana shan ice cream gefe ɗaya kuma Sufyan ne zaune yana latsa waya,da farin ciki Afnerh ta amsheta tare da faɗin "kaga mata a wajan Dr,nasan tunda kika fitu to baya nan"murmushi tayi mata tare da faɗin "nikam karki cika gani da surutu...yaya Sufyan ina ƙwana"kallonta yay sai kuma yay saurin ɗauke kai da murmushi a fuskarsa yace "yace lpa lou matar Dr fatan kina lpa dai?" a taƙaice tace "Allhdllah..nazu duba matan kane naji Mama tace ƙwana biyu zazzaɓi take nace ko an samu bbyne?"hararar wasa Afnerh ta watsa mata tace "ke ai saiki zauna kallo kina zauna zan haifawa my luv yara"da sauri Sufyan ya amshe mgnar ta hanyar faɗin "aa kada kiga laifinta kika sani ko mijinne baya da lafiya"saurin kallonsa Lili tayi tare suma kimantar maganarsa, rashin lpa kamar kodai da gske baya da lafiya shine ya ƙasa gayamin? Amma idan hakane aida ya faɗa mata shuru tayi na wani lkcn sa kuma ta kawar da zancan daga ranta dan bata son saka zargi a zaman aurensu. "ayya nikam idan na samu beby dangi zata bi ina faɗa masu akace maku? Kuma dani daku ai duk ɗaya ƴar ƴanku nawa ne right? Than mijina lafiyar lou dan bana bacci saina tabbatar da lafiyarsa" ta ƙare tana amsar ice cream ɗin hannun Afnerh tare da kaiwa bakinta,wani yawon baƙin ciki Sufyan ya haɗiya yaushe ta zama haka ashe har zata iya gaya masa magana akan mijinta hakan ya nuna masa tun a baya ba sonsa take ba,shuru yay tare da jijjiga yana tunanin ta inda zai ɗauki fansar abinda Fahad yay masa,a zahiri kuma yace "kema kince wani abu to Allah ya ƙara ƙauna" ...ameen tace nan ya miƙe yay waje suka dasa shira a nan Lubna ke ƙara warwarewa Afnerh zaman aure da kuma abubuwan dake cikinsa,ta ƙara fata wasu fa'idodi wanda idan ta riƙe za taji daɗin zaman auren lkc kaɗan kuma zata samu nasarar amshe zuciyar Sufyan wanda har yanzu basu gama zama nrml,haka sukai ta hira inda Lili ta ɓoye damuwar dake ranta a nan ta tallatawa Afnerh Nimcy vip grp aikam tayi farin ciki sosai bata bar gidan ba saida aka biya 1k aka saka Afnerh a grp ɗin,misalin 2:30 tabar gidan sannan ta nufi ɓangaren Mama ta sameta tana cin ƙwaɗon rama a nan wajanta ta zauna sukaci tare a taƙaice dai har isha'i suna tare da Mama saida Fahad ya dawo sannan ya jata suka huce sashinsu bata wani nuna masa ɓacin rai ba,a haka suka ƙwana babu wani abu daya kuma shiga tsakaninsu. *** *** Komai nada lkcnsa haka lukuta suka dinga hucewa ranaku suka dinga tafiya yau cikin Najma ya shiga watan haihuwa,farin ciki wajanta ba'a magana tana murna zata zama jagora a gidan haihuwarta shine zai bata amsar dukkan wata dukiya da Faisal ya mutu ya bari bayan tumunin ta kaba da za'a bata,ƙwance take tana faman juyi akan gado duk iyakarta da daure zafin ciwon amma abun yaci tura a haka Ammi tazu ta sameta cikin tashin hankali suka nufi hospital Papi da kansa yake dreving suna zuwa aka amsheta tare da shigewa da ita labour room,tasha wahala sosai kafin ta haifi bebynta namiji mai kama da ita cikin sauri likitoci suka ɗaukesa tare da kaisa wani ɗaki sbd yasha ruwan mahaifa,farin ciki wajan Najma ba'a magana ganin burinta ya kusa cika,ranta fess take amsa sannun da Ammi take mata cikin muryar yaudara tace "Ammi kinga hukunci Ubangiji ko,Faisal ya tafi Faisal ya dawo insha wannan shine zai gaji dukiyar daya matu ya bari kuma inda ina numfashi babu wanda ya isa yaymin iko da Ɗana da kuma abinda ya mallaka na wajan mahaifinsa"ta faɗi hakan tana kuka,Papi ne yace "ayya wake maganar wata dukiya yanzu burinmu muga girman Lil Faisal,kinga na manta an samu address ɗin da Lubna ke zauna Allah mai hukunci ashe Fahad shine mijinta kinji rabo ajali ko?daman ance matar mutum kabarinsa nan ya basu labarin komai har inda suke zaune" wata ashariya Najma tayi tare da faɗin "ashema agula ce wlh inayin arba'in na amshi tumunin taka bata da kuma gadon ɗaya zanje gareta i will kill you Lili ki shirya ganina soon,wlh....," bata ƙarasa maganar ba wata nurse ta shigo da sauri tare da faɗin "am sorry he ardy left munyi missing bebynsa Ubangiji ya amshi abinsa"wani ihu Najma tayi sai gata sumamniya daƙyar aka samu ta dawo hayyacinta,tasha kuka kamar ranta zai fita ƙwanansu biyu aka sallameta. Bayan arba'in Washe garin da zatai arba'in ta gama neman ticket ɗin tafiya pakistan nan kuma tasa gaba sai ambata dukiyar da Faisal ya mutu ya bari,Papi ya kira malami akai mata bayanin komai inda aka mata gadon ɗanta sannan aka bata tumunin ta kaba,gari na waye tayi airport bata jima ba jirginsu ya ɗaga. Sosai Mama tayi farin cikin ganinta daman an shaida mata zuwanta tunda tayi waya gyara zama tayi tace "Mama ina ƴar uwarta Lubna da kuma yaya Fahad" jin Mama tayi tace "ayya matarsa yaywa aiki yauma ta samu sauƙi zasu dawo gida ai"cikin ranta tace "good" a zahiri kuma tayi kalan tausayi tace "Allah sarki rabin rai nayi missed nata sosai ƴan uwa masu daɗi inda na huta na leƙa wajan jinina Afnerh da kuma ƴar uwa Fannerh"sunyi shira kaɗan inda Sufyan yazu ya samesu faɗin daɗin da yaji na ganin Najma ba'a magana daman sun gama tsara komai ardy tasan daman Lili bata gida. Tsaye yake ba'a iya ganin fuskarsa a hankali Khalid yace "hope kun gama shirya komai dan yanzu aikinmu zai fara"shuru yay yana sauraran abinda akece masa jijjiga kai yay alamar gamsuwa kafin ya kashe wayar,yana ajjiyewa wayarsa tayi ƙara saurin dubawa yay ganin Sunan Fairus yasa ya taɓe tare da picking call yace "ɗan uwa yakake?" daɗan sauri yace "kai haba yaushe ka shigo pakistan"sun jima suna waya kafinsu kashe can Khalid ya fesar da iskar bakinsa yace "Fairus kada ka ɓatan tsari"yana faɗin hakan ya faɗa mota tare da janta da gudu yabar wajan. Ɓangaren Fahad tun safe yake cikin farin ciki domin yana saran yau zai zama najimi kamar ku wanne namiji,ba ƙaramin hqr yay kusan wata 5 da aure zuwa shida haryau baisan matarsa ba,yasan cewa itama ba ƙaramin hqr tayi masa duk da bata san dalilin ba sai yanzu, tura ƙofar room ɗan ya sameta ta gama shiryawa yana ƙarasawa ya jawota zuwa jikinsa ya sakar mata murmushi yace "sunshine bbyna yau zan sauke duk wani abu na haƙƙin aure da ubangiji ya ɗuramin,zai maidaki cikakkiyar mace kamar kuwa zan baki farin ciki mai ɗura wannan daren zai zama dare mafi muhimmanci a rayuwar aurenmu,zan nuna maki niɗin ƙwarzone a shiri nake yau danna amshi virgin nami wify na"kunya ce ta kamata ta sunne kanta a ƙirjinsa,hannun ya zura ya shafi mararta zuwa cibiyarta tayi saurin maƙalesa,cikin shauƙin so da ƙaunarta da kuma wani mahaukacin feelings ɗinta daya tasu masa yasa hannu ya shafi nipples ɗinta tare da murzawa,ƴar ƙara ta saki tare da cizonsa a ƙirji,hannunsa ya zare tare da ƴar ƙaramar dry yace "no banyi baki komai a nan ai wannan daren specail ne,samun kanta tayi ta shafa ƙirjinsa cikin sanyin murya tace "ina maka sahihiyar ƙauna wanda baki bazai taɓa faɗin irinta ba,kaiɗin haske ne a rayuwata kaine farin cikina da kuma jin daɗina,ina kallonka matsayin wata katanga mai kare lafiyata, a duk lkcn dana tunaka naji daɗi da farin ciki ya ziyarci raina tabbas nayi dace da samun gwarzon namiji kuma adali ma'abocin addini da kuma ƙyautatawa ina sonka sosai fiye da sosai bazai daina sonka ba har sai sanda numfashina ya tsaya"ta faɗa lkcn da wasu hawayen daɗi suka zubu mata,shima hawayenne ya zubu masa bai taɓa jin zafin so da kuma daɗinsa ba sai akanta,copping face ɗinsu sukai tare da sakin dry lkc ɗaya bakinsu ya haɗe ya shiga bata lafiyayyen kiss,kiss ne wanda duk yay katarin samunsa dole ya ƙara muradin samun a gobe kiss ne mai tafiya da tunanin wanda akaiwa kiss ne mai tsayawa a rai,sun daɗe haka kafin ya samu daƙar ya cire bakinsa,hancinta yaja ciki daƙushasshiyar murya yace "muje"hannunsu cikin na juna suka ƙara gaban sabuwar motarsa mai kalan blue black dafe kai yay yace "i forgot my phone pls ƙalbi 2mins"kaita ɗaga masa tare dayi masa bye,yana zuwa ya ɗakko wayar cikin sauri ya dawo ganin bata wajan yasa ya leƙa motar yaga babu kuwa,wajan getman yaje yace "Baba ba kaga matana ba?"..."ayya Yaro yanzu nadawo daga zaga banɗaki amma dai naga wata baƙa ta fita da gudu sai kuma wani talmi daya faɗi kagansa can"da sauri ya ƙarasa wajan takalmi da mamaki yake juya takalmi dan yasa na Lili ne wanda ta ɗauka a shopping da sukai,da gudu yay waje yana zuwa yaga motar na shillawa kan titi wata ƙara ya fasa tare da faɗin "Lubna" Tofa waya ɗauke Lubna Sufyan da Najma ko Khalid ko kuma Fairus? _you guys kuna da abin mamaki mai yasa kuke tunanin zan maida JUYAYI na kuɗi? Yana nan free kamar yadda nai alƙwari addu'arku nake nema da kuma buƙata a koda yaushe👏🏻, masu buƙatar grp ɗina na Vip ƙofa a buɗe take ga dukkan maiso, zaka iya biyan kuɗinta ta wannan accout no 0116886423🤏🏼 Sulaima Na'ima s😍sai shaidar biya ta wasapp no 08119237616 kada ka bari a shiga Vip grp babu kai wannan damar zata fara daga yau 28/1/2021 zuwa 30/2/2020 idan ya huce haka ya tashi daga 1k zuwa 1500 domin specail qrp ne karatu cikin sauƙi posting kullum topic masu ma'ana bada shawarwari ga ƴan uwa matan aure da kuma ƴan mata,ina nan ina zaman jiranku da kuma nuna soyayyarku🥰💋nasan ina tare da hajiyoyi🤾🏻‍♀️ ina maku sanso_ The Writer up Ƙaddarar mace=free Ashe ƴar babata ce=free Lamrat=free Izzar so=300 Raino ne sila=free Jiddah=free Sai na aureta=300 Juyayi=free Masu zuwa Uncle Ne The New Emir Zarafi Cutar So Zurfin Ciki E.t.c idan kana Vip baka da matsala🤙🏼 *💖JYY💖* *46-47* ```NIMCYLUV🤏🏼``` ```Wattpad``` https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ _______ _______ Durƙushewa yay a wajan yayinda zuciyarsa ta shiga ta farfasa jikinsa ya ɗauki rawa idanunsa suka sauya kala daga farin zuwa jaa,wasu hawayene masu zafi suka shiga fita daga cikin idanunsa,ya rasa mai yasa yake da rauni a kanta,mai yasa ƙwalla bata fita daga idanunsa saita dalilinta,itace mutum na farko daya sashi zubda hawaye gashi still bai daina ba,shin wanne irin mijine shi da har yay sake aka ɗauke masa mata a lkcn da yafi buƙatar kasan cewa da ita a koda yaushe,hannusa yasa ya dafe kansa a hankali ya shiga furta "Hasbunallahu wani'iemal wakil,Ubangiji kayimin maganin abinda yake shirin tun karuni,ya Allah kayimin maganin waɗannan mutanan danka fini saninsu,ya wahabu kayimin tsakani dasu,ya ganiyu ka karemin matana daga kaidinsu,ya laɗifu ka haskamin inda zan ganta na samuta,ya hakamu ka sassautamin daga ciwo da raɗaɗin da suka saka zuciyna,Ya Allah nasan baka goyan bayan azzalumi Allah nayi tawassali da ƙyawawan sunayenka guda ɗari babu ɗaya,Allah nayi imanin da Annabi Muhammad S.a.w,Ya samadu nayi imani da ƙaddara wlh nayi imani da ita Allah ka shigemin gaba ka zama jagorana mai bani kariya My sunshine bby stop cry i knew kina cikin tashin hankali da yardar Ubangiji saina samuki" Da sauri ya miƙe ya nufi inda motarsa take yana zuwa ya faɗa ya jata da gudu babu inda ya tsaya police station da Agent vizer sai kuma tashoshin mota haka ya dinga bulayi a gari babu Lili babu labarinta,lkcn guda ya fita a hayyacinsa baya gane komai sbd tsananin tashin hankali,bai dawo gida ba sai wajan 11 na dare,yana zuwa ya samu Mama da Najma sai Kuma Sufyan Fairus da Khalid,yana shiga bai tsaya takan kuwa ba duk da irin kiran da Mama take masa amma bai kulata ba bare tasa ran zai tankata,cike da tashin hankali Mama tabi bayan Fahad da kallo haka kawai jikinta ya gaya mata ba lafiya musamman da bata ganshi da Lubna ba. "Mama lafiyansa lou kuwa banga rabin rai ba?"cewar Najma ta faɗa cikin damuwa kafin Mama tai magana Fairus yace "gsky dai banjin lafiya domin yanayinsa kawai zai nuna ba lafiya ba"shuru Mama tayi abin duniya duk ya dameta sosai zuciyarsata tayi sanyi jiki babu ƙwari ta miƙe tare da nufar ɗakinsa Najma ce fa rufa mata baya a tare suka shiga a nan tsakiyar bed suka samesa ƙwance idanunsa a rufe ruf,yana jin shiguwarsu amma ko mutsi baiyi ba,Najma ce tace "Yaya hope komai nrml"idanunsa da sukai masa nauyi ya buɗe tare da watsasu kan Najma hantar cikinta ce ta kaɗan musamman kallon da taga nayayi mata mai kama da tuhuma yasa tayi saurin ficewa a ɗakin,zama Mama tayi tare da shafa kansa tace "Yarona ina fatan ba wani abun bane na ganka a hargitse?"idanu ya zuba mata kafin wasu hawaye su shiga zuba daga idanunsa,a ɗan rikice Mama tace "ya salam kuka a idanun gwarzon namiji lallai ko mene wannan ya taɓa ranka"rungometa yay tare da fashewa da kuka bubbuga bayansa ta shigayi tare da shafa kansa sosai yake kuka da ƙyar Mama ta samu ya lafa ya shiga sauke ajjiyar zuciya "mene?" shine tambayar da Mama ta cilla masa,hannunta ya riƙe cikin muryar kuka yace "Mama sun ɗauken mata,sun ɗauken farin cikina zuciyata ciwo bazan juri rashinta ba dan Allah ki nemomin ita"salati Mama ta shigayi tare dayin shuru ta ɓoye damuwar dake ranta tace "Ka ƙwantar da hankalinka inaji a jikina babu abinda zai sameta duk inda take,kuma duk mai ƙoƙarin cutar da mutum Allah baya bashi iko,tabbas sun cika azzalumai mai suke so?mai suke nema da zasu ɗauki matar aure?"shuru yay yana tunani kala² a ransa yama rasa gane kan abun duk inda yake tunanin ganin ya duba babu ita,cikinsa ta shafa tace "Yarona ba dai bakaci abinci ba?"fuska ya ƙwaɓe ba tare daya ce komai ba,miƙewa tayi ta nufi haɗu masa coffee tana fita ya miƙe ya sawa ƙofar key dan baijin zai iyacin wani abu a halin da yake ciki. Mama na fita suka haɗu da Najma gaba tayi ta barta a wajan tana tunanin tsaiwar mai takeyi haka,babu daɗewa ta haɗa masa coffee cikin sauri ta ƙarasa sashinsa tayi bugun duniya amma yaƙi buɗewa haka ta hqr ta juya zuciyarta babu daɗi,tana shiga ta kira Unlce Mijinta a waya ta shaida masa komai nan ya shaida mata gobe yana hanya insha Allah. Hankali ƙwance Sufyan yay sashinsa yana jin zuciyarsa tass farin cikinsa da muradin zuciyarsa ya kusa cika,haka nan yau yaji yana son kasan cewa da matarsa yana zuwa ya nufi bedroom ɗinta can ya hangeta tana sharara bacci,kayan jikinsa ya rage yay shirin ƙwanciya,yana zuwa ya jawota jikinsa ya shiga rabata da kayan jikinta,cikin bacci taji abinda yake mata nanta shiga ƙwaɓe baki zatai kuka yay saurin jan tsaki yace "wlh koki tsaya konai maki ta ƙarfi banza raguwa komai kuka wlh za kija na ɗaureki"haka ta haɗiye kuka badan tasu ba amma haryau ta kasa sabawa da abun musamman yadda yake mata babu tausayi bare imani yayta durzarta kamar kayan wanki,haka ya ƙwashe lkc yana abu ɗaya idan yay kamar zai barta saiya ƙara ƙaimi wajan abinda yake mata,haka yabarta badan ransa yasu saidan kukan da take masa a haka saida yace tunda ta hanasa tayi sauri ta sama masa nutsuwa cikin komai take masa komai sbd yadda ƙasanta keyi mata wani raɗaɗin zaba,sai wajan 1 ta samu yabarta,cikin dauriya ta miƙe tarw da nufar toilet tai wankan tsarki tana kallonsa yay bacci dana jasa a jiki babu bakin magana,zaɓawa gefensa tayi ta ƙwanta nan itama bacci ya ɗauketa. Lili's pov Bayan tafiyar Fahad zuwa ɗauko wayarsa ko minti guda ba'ai ba ta wani mutum ya faka a motarsa yana fituwa ya nufata tayi saurin jaa baya tana ƙoƙarin kurma ihu yay saurin danna mata abu a hancinta da bakinta,kafin wani lkcn jikinta ya saki numfashinta ya ɗauke nan ya turata a mota suka bar harabar asibitin. Can cikin dare ta farka cikin nauyayyen baccin daya ɗauketa ganinta a wani ɗaki kuma an ɗaureta yasa ta saki wani ihu tare da rushewa da kuka tana kiran sunan Booby,kukan take sosai tare da ƙoƙarin kunce kanta babban burinta bai huce ta ganta wajan boobynta ba,tana tsaka da wannan halin taji an banko ƙofar cokin ɗan ɗakin da aka sakata,cikin kuka tace "dan Allah ka kaini wajan boobyna tsoro na keji"dryar mugunta yay mata saida yay son ransa sannan ya haɗe fuskarka tamkar bai taɓa drya ba, ƙarasawa wajanta yay tare da faɗin "Ah lallai baki da hankali idan har zan maidaki to mai yasa na ɗaukoki eyee,yarinyar kima daina coz babu mai jinki bare yay ƙoƙarin taimaka maki booby kuma kine kika sanshi bani ba"cikin kuka ta tofa masa yawon bakinta tare da faɗin "ƙarya kake wlh idan ka manta da Ubangijin daya haliccemu toni ban manta ba sakare,kuma booby da kake mgn na rantsa da wanda ya busa numfashi shi zai kawo ƙarshenka" hannu ya ɗaga ya daki bakinta kafin ya shiga zabga mata wasu ta gwayen maruka ya shiga nunata da yatsa yace "what are u mad hanni zaki tofawa yawo lallai kinyi kuskure"zafi da raɗaɗin marin da yay mata yasa ta saki wani ihu tare da ƙanƙame jikinta tunda take zata iya cewa bata taɓa sanin zafin mari irin haka ba sai yanzu,kuka ta shigayi sosai yawan kuka da take ne yasa numfashinta ya samu ɗaukewa cikin ƙaramin lkc ta fita hayyacinta sbd ƙaramin abune yake sawa ta fita hayyacinta to hakanne yanzu lkcn kaɗan numfashinta ya ɗauke abunka damw asma,nan ta langwaɓar dakai jikin kujerar babu numfashi,tsaki yaja yay hanyar waje yana ƙoƙarin fita wani na ƙoƙarin shiguwa,baya yay tare da bawa mutum waje yace "Oga barka da zuwa ga yarinyar nan"jinjina kai mutumin yay kafin yace "why aka ɗaureta har haka?" sosa kai Baffade yay cikin rashin gsky yace Oga raini zata kawomin shine na kuya mata hankali"cikin ɓacin rai Oga yace "what duka fa? kada ka kuskura ka ƙara ina buƙatar lafiyanta da komai nata domin sai dasu zan samu cikar muradina"cikin girmamawa baffade yace "afuwa Oga zan kiyaye"jinjina kai mutumin yay alamar gamsuwa kana yay hanyar fita shima baffade bin bayansa yay suka fice ba tare da duba halin da take ciki ba,Oga na fita ya faɗa mota yace "yawwa ka kiyaye muna gamawa zan nema maka ticket kabar garin domin an baza ko'ina ana nemanta da kuma wanda ya ɗauketa,kasan sun fimu kuɗi ka yarda aka kamaka babu abinda zan iya akai"yana gama faɗin hakan yaja motar ya fice daga mamakeken kangwan,baffade zama yay a harabar ƙangwan tare da ɗaunko sigari ya fara bata wuta. Misalin 7 na safe ya gama shirinsa cikin blue wata dakakkiyar shadda faɗin ƙyan da yay ɓata baki ne,sai zabga ƙamshi yake,zaune yake saman sofar parlour'nsa tym to tym yakan shafa sajen fuskarsa tana ƙirjinsa ya saki murmushi hakan yana tuna masa ita dan tafi shafa nan a jikinsa,wani lkcn har mataji zata ɗauka da varsiline tace zatai masa kitso taita ja masa saje da gemunsa,lumshe idanu yay yana sauraran yadda zuciyarsa ke ɗagawa da sauri wata wutar sonta na ƙara cimmasa,shi kaɗai yasan halinda yake ciki,ƙwana yay bai runtsa ba sbd addu'ar da lafilfili daya dungayi,gani yake kamar ubangiji zai kamashi da sakaki da yay da Amanarsa dan ita ɗin amanane a wajansa,makekiyar wayarsa ya ɗauka tare da zubawa ƙyaƙƙyawan picture ɗinta idanu wanda ya ɗauka bayan anyi masu aure,tana sanye da wando na bacci pink colour iya cinyarta sai ƙaramar riga gashin kanta yasha ƙyara ta turo bakinta gama tare da juya manyan idanunta,a haka ya ɗauketa pic ɗinsa lips ɗinta ya shafa yace "Amanata kina raina dan Allah ki bayyana gareni zuciyana ciwo babu daɗi inajin kamar zan rasa rai sbd ke,mai yasa kikeson yin nisa dani a lkcn da nafi buƙatarki,rashin babbar illah ne a gareni,dan Allah Amanata idan wasa kike ki daina banso"ya faɗi hakan yana ƙwaɓe fuska tamƙar tana gabansa sai kuma wasu lafiyayyun hawaye suka shiga zuba daga cikin idanunsa,yana cikin wannan halin yaji an tsaya a ƙansa sharewa yay tare dacin magani ya waske tamƙar bashi keyin kuka ba, "kuka kam aiya zama dole kayishi sbd samu sauƙi a zuciya,amma kuma yin masa baya da wani amfashi da kuka na yana maganin damuwa da tuni yay maka tunda kai shidane akan halin daka shiga na baya"cewar Fauwaz ƙara haɗe fuska yay yace "ke bar gurin nan"cikin sauri Fannerh ta juya tana guge hawayen idanunta, "aa malam kada ka firgitamin matana" miƙewa Fahad yay ya zubawa Fuwaz idanu sai kawai ya faɗa jikinsa yana maida numfashi ya kasa ɓuye rauninsa a kan dukkan abinda ya shafeta,bai san mai yasa baya iya ɓuye damuwa a ransa ba indai tata ce,bayansa ya shiga bubbugawa alamar numfashi sun jima a haka kafin ya zare jikinsa yace "boddy nayi wasa da Amanata a dalilina ta shiga wannan halin banajin zan iya riƙe wannan amanar domin ban cancanta ba"kallan tausayi Fauwaz yay masa yace "aa babu wani wanda ya cancanci ya riƙe wannan amanar saikai,kaine dai² ita kaine farin cikinta kuma muradin zuciyarta kunawa kanku so irin wanda bakinku bazai iya faɗinsa ba,so u have to think wannan damuwar is to much dole a nemi mafita,tun jiya ban runtsa ba nida matana itama haka ta ƙwana tana kuka mu gaba ɗayanmu muna cikin tashin hankali,domin Lubna haske ce a cikinmu kuma maganin damuwarmu"shuru kawai Fahad yay yana sauraran abinda abokin nasa cikin sauri ya ƙwashi wayansa da key ɗin motarsa yay waje ganin hakan yasa Fauwaz ya mara masa baya,a nan parlour suka sami Mama da Momma sa Uncle da zuwansa kenan,gefe guda kuma Fannerh da Afnerh da Yusrah sai Kuma Najma a gefe idanunsa yay jaa sbd kukan da tayi,cikin saurin Mama ta share hawayen fuskarta dan bata son yaga damuwarta bare ya ƙara girman tasa,da kallo ta bishi ganin ya faɗa idanunsa sunyi zuru²,amma idan ka ganshi ba zaka ɗauka yana da damuwa ba sbd haɗe fuska da yay tamau ya zura hannayesa a cikin aljihun rigarsa yana tafe cikin izza da kuma nagarta yana tafiyarnan tasa wacce take nuna shiɗin namijine mai ta ƙama da kuɗi izza haiba da cikar zati,idanunsa rufe yay waje yana cije laɓɓa domin sarai yaga kukan Mama hakan ya ƙara narkar masa da zuciya,yana jin Mama da Uncle na kiransa yay banza dan indai ya tsaya zuciyarsa zata iya karyewa,kuma baiso raini ga yara sun cika waje sai raba idanu suke,yana fita ya shiga side ɗin mai zaman banza ya cillawa Fauwaz key ɗin,mazaunin drever ya shiga cikin sauri ya tada motar da gudu suka bar cikin gidan. Sanyin ruwan da taji ne yasa ta farfaɗuwa ta shi sauke ajjiyar zuciya mutumin ɗazun ta gani still a kanta hannunsa ɗauke da take away da ruwa,miƙa mata yay yace "ga abinci"kanta da kawai gefe tare da sakin sabon kuka tace "boobyna dan Allah ka kaini wajansa"kallon baki da hankali yay mata yace "kwananki biyu kenan a halin suma ama ba zakibar hauka bako dallah amshi abincin" abincin ta ƙarɓa ta watsa masa a jiki tace "banza mara imanin da izinin ubangiji sa Allah ya sakawa zuciyoyin da kuka raba"hannu ya ɗaga zai daketa mai ya tuna kuma sai kawai yay waje ya barta a nan tana kuka. Tu abufa kamar wasa duk inda suke tunanin ganin babu yau wajan ƙwana uku kenan Booby ya fita hayyacinsa hakan shiga ɗaki ya kulle yayta kuka amma idan yana cikin mutane ba zaka taɓa ganin kukansa ba,ha yaɗa sosai ko abinci sai Mama ta sashi gaba haka zaice "Mama ban iyaci idan banga amanata ba"haka zatai ta bashi hqr gida ya zama babu dɗi duk farin cikin gidan yanzu babu kuwa yana cikin halin damuwa,a wannan lkcn Afnerh tayi ɓarin ƙaramin cikin dake manne a mararta sbd yawan takurar da Sufyan keyi mata shikenan abu ɗaya saidai idan basa tare,Yaci faɗa wajan Momma haryay ladamar abinda ya aikata domin Allah ya ɗura masa son cikin. Yana ƙwance jikin Mama sai faman tura masa coffee take a baki yana ƙaucewa,da ƙyar ta samu yasha rabi kansa ta shafa tace "komai yay zafi maganinsa Allah muci gaba da addu'a ubangiji na tare damu bazai taɓa kunyatamu domin yana ganin ƙyaƙƙyawar zuciyanmu"kai ya ɗaga mata ana haka yaji wayarsa tayi ƙara alamar shiguwar saƙo buɗewa yay yaga an rubuta. _Dr Fahad Mustapha Rano ashe iya nan ƙaunar ta tsaya lallai ka tabbatarmin kai lusari ne kuma sakarar zaka iya amsar fansar matarka idan kasu nan da zuwa gobe amma rashin hakan kamar ka bata damar da wani zai amshi virgin ɗinta_ Da sauri ya miƙe daga jikin Mama gaba ɗaya jikinsa rawa yake cikin sauri ya tura masa. _ka ajjiye wani shirmanka a gefe ka gayamin abinda kakeso_ Mamace ta miƙe tace "Yarona lafiya dai"wayar ya miƙa mata nanta shiga zabga salati tare da zubewa saman sofa ta zabga tagumi saurin duba wayarta jin ƙarar notification zaburar tayi tare da waro idanun tace "what"da sauri ya kalleta tarar da amsar wayar innalillhi wa'inna ilaihir raji'un kawai ya faɗa abinda ya gani ba ƙaramin tayar masa da hankali yay jikin Mama ya faɗa yace "shikenan Mama yanzu komai ya ƙare. Comment Share Vote _The secret issues_ *JYY* *48-49* ```NIMCYLUV🤏🏼``` ```Wattpad``` https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ Not edited😎 Kai Mama ta girgiza masa tare da ƙoƙarin danne damuwan dake ranta sosai abinda suke buƙata ya tada hankalinta,a ɗan rikice Mama ta kallesa tace "wannan mutanan basa tsoran Allah rayuwarka sukeson ruguzawa da kuma farin cikinka,kuma nasan sun sanka tunda suka buƙaci abinda ba kuwa yasan dashi a wajanka ba ya rabbi ka kawu mana ɗauki"lafewa jikin Mama yay yana fitar da numfashi hannu yasa ya dafe kansa dake juyawa masa tare da halmasa cikin juriya da nuna shiɗin namiji ne ta fesar da iskar dake bakinsa yace "Mama zan basu abinda suke buƙata koda zanyi yawo tsirara,rayuwar Amanata ita nafiso fiye da komai,bazan iya rayuwa cikin farin ciki babu ita ba"girgiza kai Mama tayi tare da shafa kansa face "Wannan lapton ɗin da suke nema itace rayuwarka gaba ɗaya kada ka manta duk wasu bayan files na companys ɗinka da kuma dukiyuyinka,ka sani wannan dukiyar bakai kaɗai bane aƙwai ƴan uwanka idan ka ɗauka ka basu,su kuma fa haƙƙin sune domin dukiyar mahaifin kuce gaba ɗaya"miƙewa yay daga jikin Mama yaja numfashi mai ƙarfi sbd yadda zuciyansa ke masa zafi da raɗaɗi ga yawon maganar da yake sam bai saba da ita ba,ya ɗauki lkc kafin ya kalli Mama da rinannun idanunsa yace "Mene kuɗin dana tara? Zan ɗauki lapton na basu su kuma zan basu dukkan kadarar dana tara,nida Amanata zamu rayuwa cikin inuwa ɗaya da kuma farin ciki da ƙaunar juna hakan ya wadatar dani ban damu da ajjiyar wani kuɗi ba indai baza suyimin maganin damuwata ba"kai Mama ta jinjina alamar gamsuwa kafin tace "Shikenan rabbi ya shige mana gaba saika shirya yadda zaka basu" gemunsa yaja tare da miƙewa manne da waya a kunnansa yana magana ƙasa² a haka ya fice daga cikin gidan ya nufi wajan motarsa,still waya ce manne a kunnansa a hankali ya lumshe idanunsa tare da shafa tunbinsa jin yadda yake ihun yunwa "ka nemi ticket saiku taho gaba ɗaya"yana faɗin hakan ya kashe wayar tare da cillata saman kujerar mai zaman banza,side ɗin drever ya zauna yana shiga ya tada motar tare dayin bisimillah ya fara murza kan motar,yana fita daga gidan ya saka suratul Ankabut ya shiga binta cikin nutsuwa harya harba motar kan titi. Yana fita Mama ta mike tare da nufar ɗakinta ranta a jagule ta rasa gane kan wannan lukutar masifa abu daga wannan sai wannan,sai yanzu tasan cewa tabbas jininta ke guna a jikin ɗiyarsa tana sonta tana son ganin farin cikinta fiye da komai,tana son kasan cewa da ita taji ɗumin jikinta amma ƙaddarori sun hana faruwar hakan,tun tana ƙarama mugwayen abu kebin rayuwarta,tana shiga ɗaki ta nemi waje saman gado ta zauna tare da zabga tagumi ta shiga rera kuka kamar ƙaramar yarinya,tun shiguwarsa yake tsaye kanta harya gaji dajin kukan nata yaja jiki zuwa gareta zama yay kusanta tare da jawota zuwa jikinsa,jinta jikin mijin nata yasa ta ƙara fashewa da wani saɓon kuka shi har mamakinta yake wani lkcn,tabbas tana da hqr da kawaici haɗi da ɗauke da kuma rashin damuwa da abu,abune mai wahala kaga ta tayar da hankalinta har hawaye ya fita a idanunta indai kaga hakan tabbas ta shiga halin tsaka mai wahala idan kuma harta fara kuka mai rarrashin aikine kumawa take kamar yarinya taita kuka tare da tunani kala²,bata taɓa samun sukuni saita samu abinda take so,a hankali ya shiga bubbuga bayanta tare da jijjigata alamar rarrashi,numfashi ta shiga saukewa can kuma tayi saurin janye jikinta cikinki kuka tace "ina son ganin ƴarta banso rayuwarta ta salwanta pls do something abban yara"hannu ya kama tare da faɗin "ashe faɗimatu ba zaki iya hqr da hukuncin ubangiji ba,kinsan cewa kuka bazai maki magani ba,wannan addu'ar dai da kike ita zakici gaba bi'izinillahi albarkacin annabi addu'armu baza ta faɗi a banza ba,insha Allah babu abinda zai faruwa da rayuwarsa daga ita har ɗannamu kuma sirikinmu"kanta ta ɗaga alamar gamsuwa sauke numfashi tayi tace "amma Abba yaran wannan lapton ɗin da suke nema aƙwai lauje cikin ɗani ina tunanin yadda suka san da ita a wajan yarona"kansa ya ɗaga kafin yace "tabbas nayi wannan tunanin daman ance ɗan adam 9 yake bai cika 10 duk yadda kake dashi kada ka bashi yarda,amma zato zunubi ne kada musa wani zargi a ranmu bare ubangiji ya kamamu da laifin hakan,ni yanzu bari naje na ƙara sawa ayi addu'a insha ubangiji na tare damu da kariyarsa"hawayen fuskarta ta goge sannan tai hugging nasa tare dayi masa fatan samun nasara dry yay mata yace "Maman yara uwar rigima baki girma sam"gemunsa taja kafin ta kamshi suyi waje tace "koda zan girma a idanun kuwa ai banda idon jiguna right?"hannunta ya ɗan masa yace "u're right my unique" har compund ta rakashi ya shiga mota sannan ta dawo gida,a babban parlour ta tarar da Najma ita da Yusrah suna shira sama² ganin Mama yasa Najma zama kusa da ita tace "Mama daman inaso idan big bro ya dawo ki tambayarmin haƙƙina na wajan Daddy ina son fara business ne"tunda ta fara magana Mama ta zuba mata idanu tana mamaki abinda take cewa cikin dauriya Mama tace "Amma Najma kinsan komai no need nai waiting tym ɗina wajan yi maki explation"girgiza kai Najma tayi tace "Mama naga ɓatan Lili bashi da halaƙa da kuɗin dana tambaya ko?"jinjina kai Mama tayi tare da kauda kai tace "halan baki da labarin wanda sukai kidnap ɗin Lubna ƙadarar da mahaifin naki suke buƙata a basu kinga mganar a baki kuɗi babu shi"saurin kallonta Najma tayi tare da zaro idanu waje tace "eh Mama za'a iya basu amma a tabbatar an cire nawa haƙƙin before ayi hakan"tana faɗin hakan tayi ɗakinta zuciyar cike da baƙin ciki tana ji tana gani za'a mata sakiyar da babu ruwa haƙƙin tane ya zama dole a bata,da kallo Mama da Yusrah suka bita Yusrah na mamakin hali irinna Najma tana abu kamar ɓatan ƴar uwarta bai damunta,numfashi Mama taja daman tasa za'a rina kuma ta ƙuduriniyar bata abinda take buƙata,miƙewa tayi tare da kallon Yusrah tace "Yaya jikin ƴan matana,yau Momma shuru hope dai lpa?"murmushi Yusrah tayi tace "la Anty Afnerh sun fita da ya Sufyan kina bacci Momma kuma shiri take nanda 1week zanu huce zuwa gida"baki Mama ta riƙe tace "ni Faɗimatu amma shine babu sanarwa bari na kammala girki saina ƙarasa wajanta ko"miƙewa Yusrah tayi tace "Mama muje na tayaki yau gidan babu daɗi sam"jerawa sukai a tare suka nufi cikin kichin,wajan 1hour suka ɗauka suna shirya abinci kafinsu kammala lkcn anata kiran sallan magrib suna gamawa suka nufi yin alwama Mama tai sashinta Yusrah ta nufi ɓangaren Momma,a lkcn ne Sufyan da Afnerh suka shigo daga shopping ɗinda suka tafi. Fahad bai shigo cikin gidan ba sai wajan 10 na dare yana zuwa ya faɗa toilet cikin sauri yay taken shower daga shi sai troser hannunsa ɗauke da towel yana goge jikinsa tun yadda kakai da kallon ƙurilla baka isa ka ganu abinda yake zuciyarsa bare face ɗinsa yay showing ainahin abinda ke ransa,iskar bakinsa ya fesar yana ciwo ziyansa nayin wata tafasa musamman da Mama ta shaida masa abinda Najma tayi ta waya bai dawo gida ba saida yaje ya saita komai na abinda zai bawa Najma'n daman ardy an masa bayanin abinda kuwa zai samu na gadon nasu,ƙarasa goge jikinsa yay kana ya nemi versilen mara ƙamshi sosai ya shafa² saman fresh skin ɗinsa,gaba ɗaya baya cikin nutsuwarsa komai yake cikin dauriya yake hakanma ba ƙaramin ƙoƙari yayma sbd ƙarfin addu'ar da yake shiyasa zuciyarsa ta an lafa,wando three gauter ya saka sai t.shirt mara nauyi kana ya taje kansa bai wani tsaya fesa wani turare ba,ya ɗauki wayarsa yay waje,yana shiga babban parlour'n gidan wayansa nayin ƙara cije lipa yay dan zuwa yanzu bai son magana ko takuri,makeken screen ɗin yaja nan take lafiyayyan pic ɗinta ya bayyana wani tsadaddan murmushi ya saki ganinta cikin farin ciki a pic ɗin yaji kasu 50 na damuwarsa ya kau,saman wayar yaja ya shiga notification ɗin daya gani saƙwannine guda biyu na farka anyi haiding number saƙon ya shiga karantawa kamar haka. _Idan ka shirya gobe kazu ka da lapton ɗin sannan ka amshi matarka,ko 5minutes ka ƙara ina mai tabbatar maka zaka rasa lapton kuma zaka rasa ƙimar matarka i promise you_ Runtsa idanunsa yay da ƙarfi wata iriyar muryar yace "wlh ƙarya kuke duk sai naga bayanku na rantse da sariki dake busamin numfashi,ƙaramin ƴan iska matsoranta banza da iska"yana faɗin hakan yaka dugun fasali sbd yadda maganar tayi masa tsayin gske dafe kansa dake sara masa yaya cikin jarumtar daya aruwa kansa ya shiga saƙo na biyu ya suma karantawa kamar haka. _na samu ticket kamar yadda kace amma dole sai zuwa gobe zamu samu damar ƙarasuwa,thank you once again frnd_ Cikin sauri yaywa kowannansu replay kana ya jefa wayar a pocket ɗinsa ya ƙarasa parlour,Sufyan da Mama ns wannan karan hadda Momma gefe guda Afnerh ƙwance tans ɓacci can ɓarin Najma da Yusrah ne kuwa na danna waya,tsakiyar sukansa kuma iyayensa ya zauna tare dayi masu sannu da gida sannan ya gaida Mama,takaddun da suke cikin aljihunsa haɗi da trailer ta kuɗi ya damƙawa Mama cikin ƙasa da murya kamar mai raɗa yace "Mamana kason tane da take buƙata,ga files na company ninta sai kuma takaddun filayensa guda 3 ga kuma kuɗinta nan 10.m"yana faɗi hakan idanun a lumshe,Mama ta kalli Najma tace "ga abinda kika buƙata nan"cikin sauri ta miƙe tare dare amsar files farin ciki fal fuskarta,tana amsa tayi ɗakinta,Yusrah kam mutuwar zaune tayi sbd wani muvun ƙwarjini da Fahad yay mata komai nasa cikin tsari yake sam baya da hayaniya uwa uba rashin magana,ta fahimci yana da ƙyautatawa da kuma tausayi da wannan ake samun nasarar ganin bayansa,abu mai birgewa a tare dashi ƙyawawan halinsa wanda sai kana tare dashi zaka fahimta hakan,amma miskiline shi na ajin ƙarshe bai damuwa da kuwa kamar yadda bai damu da adamu dashi ba,kafin kaga dryarsa zaka wahalan gske,saidai ka yaya ya gyara fuskarsa hakan yana taimakawa beauty points ɗinsa damar lutsawa dalilin hakan za kaga kamar yay murmushi,numfashi tare da saurin ɗauke kai sbd hararan daya banka mata sosai taji kunyar kamata da yay tana kallonsa,5minutes bai ƙara ba ya miƙe tare da shigews sashinsa,parlour'n ya ɗauki shuru kuwa da abinda yake saƙawa a ransa,kafin lkc yaja kuwa ya nufi ɓangarensa,yana shiga ya zare rigar cikinsa tare da fesa turare ya ɓalli tables ya shafa saman makeken bed ɗinsa ya faɗa tare da kunna suratuƙ baƙara ya shiga bi har bacci yay gaba dashi. Sufyan na shiga sashinsa ya faɗa toilet bai daɗe ba ya fitu,cikin sauri ya shirya cikin kayan bacci tunani kala² a ransa yana mamakin yadda abubuwan suke tafiya haka,idan har bashine ya ɗake Lili ba to waye? Meye amfanin karɓar lapton ɗin hannun Fahad? Bayan shida Najma da suka sakawa rayuwarsu idanu ya tabbarwa kansa cewa akwai wani ko wasu,da wananin ya gama shirya ya fice daga ɗakinsa zuwa ɗakin Afnerh ƙwance ya sameta saman bed harta fara bacci,kansa kawai ya girgiza yana jin sonta na shigarsa yanzu daya ta ɓata yaji raki,murmushi yay dan yasan shiɗin ba kuwa wacce mace bace tsararsa,da wannan ya refe mata ƙofa kai tsaye ɗakin Najma ya ƙarasa yana shiga ya sameta ɗaure da towel,da ɗan Mamaki ta kallesa tace "lapia dai a wannan lkcn?"dry yay mata kana ya ƙarasu ciki ya zauna daf da ita yace "wata shawara nazu baki idan kin shirya to lallai kina gaf da zama the richer young lady"waro idanunta cike da murna tace "harkar kuɗi waya baya sonta a shirye nake tsaf"gyara yay yace "na gano inda Lapton ɗin Daddynku take idan kika bani haɗin kai zan amsota na baki ita,kiga daga nan zan samu farin cikina Lubna ke kuma zaki samu kuɗi"jinjina kai tayi domin harta hango yawan kuɗin da zata samu kallonsa tayi tace "wanne haɗin kai kake nema a wajena?"matsuwa yay tare da shafa mazauninsa yace "ina buƙatarki a wannan inaso na baki the best sexy"a ɗan tsorace tace "gsky ban iyawa saɓo ai sai yaymin yawa haba sake tunani dai"miƙewa yay ya nufi hanyar fita yace "ok shikenan saiki daina mafarkin ganinki a paris kamar yadda kike muradi"shuru tayi na wani lkcn ganin yana shirin fita tayi saurin cewa "na amince"wani shu'umin murnushi yay mata tare dasa hannu ya kashe hasken ɗakin da saurin ya nufi inda take zaune yana zuwa ya jawota jikinsa ya shiga ware towel ɗin jikinta a haukace ya hankaɗata saman bed ɗin cikin sauri yay naked bai tsawa jire komai ba ya shiga mata wani romance mai lafiya,cikin ƙaramin lkc ya tasu mata da ƙwantaccen tsumin dake jikinta,cikin sauri ya ta shiga bashi martanin abinda yake mata kafin wani lkc sun haukata junansu baka jin komai sai sautin fitar numfashinsu,lkcn da kuwa ya keso ya jisa a babban fakene yasa suka gyara ƙwanciya babu kunya bare tsoran Allah ya shiga ƙoƙarin cilla jikinsa cikin nata wani ihu suka saki a tare suka ƙanƙame juna summa manta cikin gidan mutane suke. Cikin baccinta taji wata a zababbiyar yunwa da salati a bakinta ta miƙewa tare da nufar toilet ta wanke fuskarta a zuciyanta tana mamakin rashin ganinsa a ɗakin,dan tasan ko baizu ba shisai yazu,dicret babban parlour ta nufa tana zuwa ta shiga kichin gas ta kunna tare da ɗura ƙamar tukunya ta shiga dafa indomie da ƙwai wajan 30minutes ta ɗauka tana gamawa ta zauna a nan taji abincinta kana ta kura da ruwa,ɗakinta ta koma harta ƙwanta taji yau tana buƙatar mijinta miƙewa tayi ta nufi wajan dressing mirrow ta fesa turare tare da goga lipstic,ɗakinsa ta nufa tana zuwa taga baya ciki bata yarda ba ta shiga duba toilet da saurin ta nufi waje tana mamakin inda yaje a wannan daren,fituwa tayi a ɗakin ta nufi hanyar sashin Momma tana ƙoƙarin giftawa taji surutai a ɗakin najma haɗi da nishi sama² tun tayi kodai bata da lapia ne har zata huce sai kuma tayo baya domin duba lapanta,tana ƙoƙarin ƙarasawa ƙofar ɗakin taji anyi saurin riƙe hannu tare dayin baya da ita baki ta buɗe zata saki ihu akai saurin saka hannu aka rufe mata baki. *1/feb/2021* 3:34 *💖JYY💖* *50-51* ```NIMCYLUV🤏🏼``` ```Wattpad``` https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb ```pls Aunty idan kina telegram kiyi join wannan link ɗin coz 2days zanyi busy bazan samu damar posting a grps masu yawa ba,but kina grp ɗina na telegram zaki ga new update as soon as nayi sabon typing thank you guys i hrt u all😍``` *_@Telegram 🤙🏼_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ Tsoro da firgici ne ya hana Afnerh magana runtsa idanunta tayi dan bata son ganin abinda zai ɗaga mata hankali,gefe guda kuma na zuciyarta tunanin Najma take da kuma ihu haɗi da sumbatun da take jiyowa a ɗakin,sosai gabanta ke faɗuwa tana jin yadda ake janta kamar kayan wanki,a haka har suka ƙarasu wani ƙaramin parlour tana jin yadda aka rufe ƙofar da key,a hankali ta buɗe idanunta ta saukesu a kansa,yana tsaye ya juya mata baya sanye yake cikin kayan baccinsa daga shi sai three gauter sai farar singlet hannunsa ya ɗura akan waist ɗinsa tare da sunkuyar da kansa ƙasa alamar tunani,yadda bai kulata haka itama bata kulashi ba kuwa aƙwai tunanin da yake a ransa tare da nemawa junansu mafita,yayinda take tunanin mijinta Sufyan da kuma tunanin inda ya tafi a wannan daren ita dai haka kawai taji ranta bai ƙwanta da ɗakin Najma ba tai daiyi shuru ne coz bata wani kuzari ko kuma dalilinta na neman son jin ba'asin kukan da ake a ɗakin,yayinda Fahad zuciyar keyi masa lugude haɗi da tafarfasa kallo ɗaya zakai masa kasan cewa ransa ya gama ɓaci ,bai san haka yake ba,da babu abinda zaisa ya amince a bashi ƙanwarsa a matsayin mata,wani huci ya ƙara fitarwa domin wani ɓangaren zai iya cewa thank God da hakan ya faru domin a wannan daren ya fahimci abubuwa da yawa wanda yazu masa a JUYAYI, lumshe manyan dara daran idanunsa yaya tare da cije lips ɗinsa kana ya fesar da wata zazzafan iska daga cikin bakinsa,a hankali ya juyawa zuwa gareta cikin nutsuwa ya zauna kujerar da take kusa da ita hannunsa yasa ya shafi sajan fuskarsa kana ya zuba mata idanunsa cikin ƙwantacciyar muryar mai cike da nutsuwa yace "fituwa cikin dare why" kanta ta sunkuyar ƙasa ba tare da tace komai ba,a fusace yace "kee!!! ni zaki maida mahaukaci?" kuka ne ya ƙwace bata saita tasu da gudu ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka,runtsa idanunsa yay yana jin kukanta har ransa,sai yanzu ya kejin ƙanwar tasa cikin zuciyarsa dan yanzu duk duniya babu wani wanda ya fita a wajansa domin ita ɗin jinin sace,hannunsa yasa ya shiga bubbuga bayanta alamar rarrashi cikin kuka tace "am sorry Yaya ban fitu da wani abun bane na fitu neman Sufyan naga baya ɗakinsa ne"kallonta yay tare da cireta daga jikinsa kana yaja numfashi yace "alright maza koma bedroom naki,kada ki kuskura ki shiga ɗakin Najma"kaita jinjina masa kafin ta kallesa cikin sigar shagwaɓa tace "but Sufyan fa?" haɗa fuskar yay tamau kamar bai taɓa dry yaba yace "halan shiɗin ba yaro bane?" kaita jinjina masa tare da goge hawayen dake fita daga cikin idanunta,kanta ya shafa kana ya miƙe tsaye yay cikin bedroom ɗinsa zuciyarsa nata fasa,cikin mutuwar jiki tayi hanyar fita daga flat ɗin nasa,a babban parlour ta tsaya tare da shigewa duniyar tunani. Sufyan da Najma kam sun daɗe da fita daga hayyacinsu babu abinda ke fita a cikin ɗakin sai sautin numfashinsu tare da surutai marasa amfani,sun ɗauki tsayin lkc suna aikata saɓon Ubangini saƙo mafi muni,domin daka aikata zina gwamma ace fyaɗe kayi ko akai maka,yin zini babban ɓata ne ɓata kuma mai munin gske wanda duk wanda ya aikata hakan bazai taɓa samun nutsuwa ba sai ancire haƙƙin Allah a kansa wato an jefesa kamar yadda yazu a hadisi,sun riga da sun mantan hakan shiyasa suke sheƙe ayarsu hankali ƙwance tunaninsu babu mai ganinsu tunaninsu wannan itace hanyar daza subi su samu muradin zuciyarsu,amma saƙwan Ubangiji da sukai sai ya hanasu ƙwanciyar hankali bare ma har suyi tunanin samun ƙudirunsu,haka suka dinga abu guda idan yay kamar zai barta saita ƙara tun zurashi,idan tai kamar zata kamsu saiya fita a jikinta yaci gama da romance ɗinta harta fara yi masa sunbatu sannan ya ƙara shigewa jikinta haka suka dingayi har aka fara kiran sallar farko na asuba sannan suka hqr da junansu,cikin sauri ya miƙe tare da shigewa bedroom ɗinta ya sakarwa kansa shower tare dayin wankan sarki a haka ya kammala ya fitu ya zura kayansa duk a kan idanunsa dry tai masa tare da faɗin "ka iya aiki"gira ya ɗaga mata yace "nima zam na jiki ƴan mata kamar sabuwa saidai ba ita ɗin bace"kanta ta girgiza tace "kusan hakan namiji ɗaya ya sanni a lkcn ya haɗu da ajalinsa,bayan haka kaine na biyu" (kaji sakalya ubanwa yake faɗin sirrin zaman aurensa🤔). Baice bata komai ba ya kammala saka kayansa yay waje,itama miƙewa tayi tare da shigewa toilet tayi wankan sarƙi,sai a lkcn ta kejin kamarta aikata babban kuskure na amincewa da Sufyan da tayi,wata zuciyar kuma tace "a'a Najma kinye dai² wannan hanyar itace zata baki damar samun burinki da kuma ɗaukan fansa a kan Lili domin itane sanadin mutuwar mijinki" da wannan zancen tayi amfani a gurguje ta sanya kayanta tare da faɗawa saman gado sai bacci ta naji ana sallar asuba amma ko a jikinta. Sufyan na fita yay hanyar sashinsa da murmushi fal fuskarsa,tun daga nesa zuciyanta ya buga kanta ya shiga juyawa da sauri ya tasa hannu ta shiga murza idanunta still shi ɗin dai take gani yana fituwa daga ɗakin Najma,jikinsa tabi da kallo ganin yadda ruwa ke ɗiga ga yadda gashin kansa daya jiƙe, jikinta ne ya fara rawa da ƙyar bakinta ya samu damar faɗin "innalillahi wa'inna ilaihir raji'un". Tsayawa yay turus sbd baiyi tunanin ganinta at this tym ba,kansa ya sunkuyar alamar rashin gsky,kallonsa kawai take lkcn wasu hawaye suka shiga fita a idanunta,cikin sauri ya ƙarasu wajanta ya shiga ƙoƙarin jawota zuwa jikinsa tayi saurin yin baya kallonta yay yace "Baby na..."sauri ɗaga masa hannu tayi wanda ya hanashi ƙarasa zancen da yay niya,da sauri ta juya ta nufi ɓangarenta tana zuwa ta faɗa kan bed tare da sakin wani kuka mai ciwo,wato surutai da sumbatun data jiwo shine kenan,wata kan wannan dalilin yasa Fahad ɗauketa gudun kada taga abinda zaisa zuciyarta bugawa,hakan yana nufin Fahad yaji abinda suke kuma ya fahimta,how long suka kasance a haka?daman shi ɗin a haka yake ko yanzu ya fara? Hakan yana nufin yana tarayya da wasu matan ko kuwa? Kodai laifin tane da take masa raki har yaji haushin hakan ya faɗa wannan halakan? “No!!” ta faɗa cikin ƙaraji domin tasan halinsa duk kukanta idan har yay niya baya fasawa saidai idan ya gama ya bata hqr,kuka tayi sosai har bacci ya ɗauketa a wajan inda Allah ya taimaketa tana fashin sallah. Sufyan kam ji yay babu daɗi yayinda kunyar matansa ya dirar masa a zuciya idan kuma ya tuna cewa yayi hakanne domin ya mallaki muradin ransa da kuma farin cikinsa sai yaji wannan ba komai bane,ƙafarsa yaja zuwa sashinsa yana zuwa ya faɗa toilet yay alwala sannan ya sauya kaya ya fita zuwa maallaci, a can masallacin ya haɗu da Fahad da Uncle suna tattaunawa a kan yadda zaije ya amso matansa,ya tafi da ƴan sanda cewar uncle yayinda shi kuma yace shi kaɗai zai tafi haka Uncle ya rabu dashi badan yasu ba, cikin sauri Sufyan yabar masjid ɗin yayo gida babu inda ya tsaya sai sashin Fahad ya shiga neman lapton duk inda yake tunanin ganinta ya bincike babu ita babu dalinta,ganin idan ya tsaya zai iya cin masa yasa yay saurin barin ɗakin ya nufi ɗakin Afnerh ƙofar ya shiga bugawa amma taƙi buɗewa dolensa ya juya tare da shigewa ɗakinsa a ransa yana tunanin inda Fahad ya ajjiye lapton ɗin da wannan tunanin bacci yay gaba dashi,Fahad kamar yasan za'ai hakan lkcn da zai fita masjid ya fita da ita tare sa sanyata a mota hakan yasa Sufyan ya gama bincikensa bai ganta ba. Misalin baƙwai na safe ya gama shirinsa cikin wata dakakkiyar shadda lemon green yay ƙyau sai zabga ƙamshi yake yana gamawa ya buɗe wata box ɗinsa wacce yake ajjiye muhimman abunsa a ciki,da sauri ya saka pin cikin harufan "SUNSHINE BABY" yana gama rubutawa ta buɗe wasu ƙanan abu ya ɗauka wanda baka iya tantance menene,yana gamawa ya rufe box ɗin tare da watsa abun a cikin aljihunsa,wayoyinsa ya ɗauka tare da key ɗin motarsa yay waje,ganin babu kuwa a parlour yasa ya huce sashin Mama nan ya sameta tana haɗawa Uncle tea gaishesu yay yace "Mamana Uncle zan huce amsu matana a sanyamin albarka"ya faɗa yana lumshe idanunsa kansa suka shafa a tare sannan suka sanya masa albarka tare dayi masa fatan alkairi,Mama tace "Yarona mai zai hana ku tafi sa Sufyan?"runtsa idanunsa yay saukar sunan Sufyan a kunansa dai² yake da a ɗauki mashi a caka masa baijin a ƙwai wani abu daya tsana sama da Sufyan kasa amsa mata yay sai miƙewa da yay tare da ficewa a ɗakin,bayansa suka bi da kallo suna Mamakin yadda yake nuna rashin damuwa a kansa,gaba ɗaya sabga idan ba tasa ba bata fiya damunsa ba,babban abinda yake bata mamaki yadda sometimes mgn take masa wahala ga kafiya da kuma naci,dan yana yaro idan aka fiya yi masa surutu fashewa yake da kuka ko kuma ya shiga jifa da dukkan abinda yaga dama,wannan dalilin yasa ba'a fiya ta kurasa ba,Fahad na fita ya faɗa motarsa ya jata da gudu yabar gidan,a hanya ya tsaya ya ciro kuɗi masu yawan gske a cikin motarsa ya rabawa almajirar nan suka dinga yi masa gdy da kuma saka masa albarka haɗi da addu'a, yana tafe cikin mota suna yi masa ƙwatancen inda zaizo ya amshi matarsa,a wani gefen titi ya tsaya,ya daɗe a tsaye kafin yaga wani ƙaton mutum mara fasali ya nufusa fuskarsa ɓoye cikin wani baƙin yadi,fituwa Fahad yay daga cikin motar tare da nufar mutumin yana zuwa gaf dashi yay tuntuɓe ya faɗa jikin mutum a rashin sani,wajan 2minutes ya dafa kan mutumin tare da janye jikinsa,Lapton ɗin ya basa mutumin na amsa yay masa ƙwatancen gidan da suka ajjiye masa Lilinsa,da sauri ya faɗa mota tare da janta da gudu cikin ƙaramin lkcn ya ƙarasa wajan,cikin isa da gadara ya shiga takawa inda yake da tabbacin ta nan,yana shiga yay saurin ɗauko wayarsa ya kunna sbd duhun ɗakin nan ya shiga haskawa,tsayawa yay cak tare da sakin wayar hannunsa. (kasa ai fushi da Sarauta na shiga sabgar biki💃🏻😂so typing ɗinma sai a hankali,kuyimin afuwa yau babu long typing but ina son long comments ohhhya kun gane ai😉) ```NIMCYLUV🤏🏼``` *52-53* Sorry guys vry busy wlh✋🏼🤙🏼 ______ ______ Wayar na faɗuwa ta tarwatse abinka da glass, cikin saurin ya ƙarasa inda yaga vail ɗinta yashe a ƙasa yana zuwa ya ɗauka,hankalinsa ba ƙaramin tashi yay ba da yaga babu ita a ɗakin da sukace tana ciki,vail ɗin ya ɗauka cike da fargaba haɗi da zullumi,ina take? Me sukai mata? Wannan shine tambayar da yake zuciyansa amma babu amsa,durƙushewa yay a wajan tare dasa hannu ya dafe kansa take juya masa,lkc kaɗan jiniyoyin kansa suka firfitu yayinda gargasan jininsa suka shiga miƙewa sbd tashin hankalin daya shiya,wani zazzafan huci ya fitar daga cikin hancinsa,cikin mutuwar jiki yasa hannu ya safe tsakiyar forehead ɗinsa, ƙara runtsa idanunsa yay sbd lugudan da zuciyarsa keyi masa,da ƙyar ya samu ya ware jajayen laɓɓansa ya shiga faɗin “YA HALILU, YA NURU,YA ZUL'ARSHID MAJID,YA FA'ALILLUMA YURID”. Ya ɗauki tsayin wani lkc a wajan kafin ya miƙe tare da fice a wajan cike da kuzari,sosai Booby yay ƙoƙarin danne damuwa da kuma raunin dake son fallasa a sirin zuciyarsa,hannayensa duk biyun ya zura jikin aljihun wandonsa,amma dwon hrt ɗinsa sosai take a zabantuwa sa rashin ganin Amanarsa kuma sanyin idaniyarsa,babban tashin hankalinsa ya kasance an taɓa lafiyarta,zai iya jure komai amma bazai jure zubar hawaye daga cikin idanunsata ba,yana cikin tafiya zuwa motarsa wayansa ya shiga ƙara alamar kira ya shigo,ɗan tsaki yaja kaɗan kamar bazai ɗauki wayar ba,sai kuma ya ɗauka a nan yaga irin fashewar da wayan tayi ko 2weeks bata rufa da siya ba amma ji yadda ta fashe,yana ƙoƙarin bai data aljihu wani kiran ya ƙara shiguwa,rikitattun idanunsa ya zubawa wayan ganin number ba suna,lumshe idanunsa yay tare da picking call ɗin ya manna wayan a kunnansa,daga can ɓangaren a kace. _Hello Dr Fahad Mustapha Rano,to me kace? What the you think? You're very stopid if you think zamu baka matanka cikin ruwa sanyi, no!! Ka maidamu wasu cat or dog something lyk dat dai,ur is with me kayimin rubushi yanzu na mai data a kuyana hhhh_ Wani huci Fahad ya shiga fitarwa jikinsa duka tsuma yake yayinda ya kawai motar wani wawan naushi kamar itane yay masa laifi, cikin muryar gargaɗi mai kamata kashe di yace. _Hey!! Emty head i will kill u kada ka sake nayi gaba da kai i will give u yanyash on ur body salakan banza, meye wifyna ta maku ni zaku kama ba ita ba,than tell what the you need na baku,i need my wify frist_ Wata dry akai ta cikin wayar sai da yay mai isarshi sannan yay shuru tare da faɗin. _calm down my friend matanka yana lafiya fiye da kai,zan baka itane for one condition,just tell me ur password da kai using dashi a lapton ɗinka and ur emal adress_ "Allahumma ajirni min musibti wa'aklifni khairan minha" shine kawai abinda Fahad ya samu damar faɗa,domin basu wannan abun dai² yake da rasa komai na rayuwarsa,dukkan kuɗin da yake ta ƙama yana dashi sai yaza mana ruwan sha ya gagareshi,amma Lubna'nsa ta fiye masa komai na rayuwa ko da kuɗin idan babu ita to babu jiɓ daɗi da ƙwanciyar hankali tattare dashi,hannu yasa ya hargitsa ƙyaƙƙyawar sumar ƙansa,runsa idanun yay da ƙarfi tare da taune laɓɓansa har saida jini ya fitu,cikin sanyi murya mai kama da yankewar jin daɗi yace. _Password HADNERH,and email is 21lilinbooby@gmail.com_ Wata shu'umar tare dry akai daga cikin wayar kana akace. _Dr Fahad lallai mahaifinka yabarka da dukiya mai yawa,good boy kazu titi zaka samu matanka a nan_ Yana faɗin hakan ya kashe kiran,bai jira wani lkcn ba ya faɗa motarsa tare dayi mata key ya jata da wani irin spend yabar cikin kangwan,yana hawa kan ititi ya fara rage gudun mota ya shiga wulga fararen idanunsa zuwa gefen hanya. Lili's pov Duk inda kuke tunanin wahala Lubna ta shigeta bata da wani aiki sai kiran sunan booby,duk abinda zasu bata da zummar abinci bata iya ci ruwa kawai take iya sha shima dan ya zama dole ne,tasha suma tana farfaɗuwa sbd kukan da take yana taimakawa asma ɗinta tashi hakan yasa take rasa numfashinta. Yanzu ma tana ƙauce cikin ɗaukewar numfashi ɗaya ta fita hayyacinta,duk irin gyaran da Fahad yaywa gashin amma abanza gashinta ya barbazu ƙasan wajan da take ƙwance,turo ƙofar ɗan ƙaramin ɗakin sukai tare da shiguwa ciki,kallonta sukai tare da sakin dry,ruwa mai sanyi suka ɗauka tare da sheƙa mata ruwan,wata ajjiyar zuciya ta saki tare da ƙanƙame jikinta ta saki kuka,ɗaya daga cikin sune ya taka zuwa inda take tare da fisgota,tirjewa ta fara ganin zata ɓata masa lkcn yasa hannu ya ɗauketa cak ya dannata cikin mota,a guje suka bar cikin waje saida suka nemi gefen titi sannan suka tsaya tare dayiwa Fahad waya su nayi suna danna lapton ɗin,saida suka gama buɗe komai sannan suka buɗe motar tare da fitu da ita daga cikin motar sukai sa'a babu kuwa a ciki hakan tasa sukaja motar a guje suka bar tsakiyan titi,yanayin sanyi da iskar dake kaɗawa yasa ta suma karkarwa tare da tunanin inda zata ɓuye taji daɗi sbd ba wani abin arziƙine a jikinta ba,jan jikinta tayi zuwa gefen titi tare da ƙanƙame jikinta waje guda,yadda ta cure waje ɗaya zai wahala ka gane mutum ne a wajan. Tunda ya hau kan titi yake juya fararen ƙwayar idanunsa saman titin da gefensa amma babu ita babu dalilinta,wajan 20 minutes yake nemanta amma shuru haka yake murza kan motar cike da tashin hankalin da yaƙi ɓoyuwa a fuskarsa,har kifta ta wani waje sai kuma ya dawo da baya a hankali yay ƙasa da glass ɗin motar tare da zura kansa kaɗan ta window motar,hangota yay ta zure waje guda sai rawar sanyi take,da sauri ya kashe motar ya fitu yana zuwa bai tsaya ɓata wani lkc ba yay sama da ita,baki ta buɗe zatai kurma ihu sbd tsoran da yake ranta yay saurin sanya bakinsa cikinta,lumshe idanunta tayi ta shiga sauke ajjiyar zuciya wani sanyi da nutsuwa suka dirar mata a zuciya,ƙwantar da kanta tayi saman ƙirjinsa tasan ko wanne bazai taɓa cutar da ita ba,haka nan taji ta samu nutsuwa dashi cike da izza da ta ƙama yake da tafiya da ita a jikinsa zuwa cikin mota, ya haɗe fuska sosai sbd kallon da mutane suke masa,yana zuwa ya buɗe side ɗin drever ya zauna da ita a saman kujera,dake baƙin glass garesa ya shiga yin sama da glass ɗin motar harya gama zugewa,jin gina bayansa yay jikin motar ya shiga hamdala a jikin zuciyarsa,jin yay shuru kuma still bakinsa yana cikin nata yasa a sanyaye ta zare bakinta tare da buɗe nauyayyun idanunta da sukai mata nauyi,ɗan ƙara ware idanunta tayi ganin mutumin da ba tayi tunanin gani dan zuwa yanzu ta hanke ƙauna da samun farin ciki balle harta kasance tare dashi,jikinsa ta faɗa ta shiga dukan ƙirjinsa tare da sakin wani sabon kukan mai cin rai,a hankali ya ware gajiyayyun mayan idanunsa a kanta,jin dukan yay yawa hadda cizo daya ƙushi kamar shine yay mata laifi yasa shi zagaye hannayensa tare da matseta a jikinsa tsam nan ya fahimci ƙaramin zazzaɓi dake jikinta,a hankali ya shiga zare rigan jikinta tana karewa,wani murmushin gefen baki ya sake sbd shi ɗin ba ma'abocin dry bane,dryarsa ya ɓuye dan yana fituwa da ita zai ƙara haddasa wata rigimar,a haka ya samu nasarar zare rigan jikinta,rigar shaddan jikinsa ya zare kana ya zura mata a jikinta,kallonsa tayi kana da saki murmushi wanda ya fitu da hawaye cikin sanyin muryar tace. “boobyna” Gira ya ɗaga mata alamar tambaya dan baijin zai iya amsata hawayen ta guge tare da kama hannunsa ta ɗura bisa ƙirjinta tace "zuciya ciwo babu abinda yake min daɗi bana jin zan iya rayuwa babu kai,pls kada ka bari wani abu ya ƙara samuna pls boobyna ban hqr da rashinka"ta faɗi hakan tana ɗura cute pech lips ɗinta saman nipples ɗinsa,lumshe idanunsa yay tare da matseta a jikinsa yana ji kamar ya tsaƙa ƙirjinsa ya maidata ciki,kanta kawai yake shafawa tare da buga bayanta alamar rarrashi,babban ya tsansa ta tura cikin bakinta ta shiga sauke ajjiyar zuciya,lkc kaɗan bacci yay gaba da ita,tausayin kansu ne ya dirar masa a zuciya ƙaddarori da yawa sunna kunnuwa cikin rayuwarsu,kanta ya ƙara shafawa tare da bata wata lafiyayyiyar sumba,kana ya murza kan motar tare da bisimillah suka bar wajan. _ƙauyen yola_ Yau tunda Baba habu ya tashi yake zabga gudawa abu kamar wasa yaƙi ci yaƙi sha,a haka suka ƙwana tun yana iya zuwa ban ɗaki harya kai da saidai yay a ƙwance hankali Uwande ya tashi cikin firgici tasa aka nemo mata Musty lkcn har Baba habu ya fara fita hayyacinaa ko yay bayan gida sai yanzu baƙiƙƙirin ga wani shegen wari daga ƙarshe saiya fara amai shima baƙi,da sauri suka ɗaukesa suwa babban asibitin dake cikin garin yola ƙwanansu biyu amma abu yaci tura,nan Dr yake shaida masu taifut ce dashi kuma taci ƙarfinsa,dam harta fara taɓa hanjinsa sai anyi masa aiki,cikin tashin hankali Musty yace "yanzu Dr meye mafita?"gyara zama Dr yay tare da zare glass ɗin fuskarsa kana ya kalli Musty yace "a gksy wannan abin yafi ƙarfinmu domin hanjinsa ne ya taɓo kuma dole sai anyi masa aiki,idan ba haka ba zai iya fashewa at any time" dafe kai Musty yay yama rasa mai zaice wannan wacce irin lukutar masifa ce ta kunnu masu,kallon Dr yay yace "inaga wannan ba abin damuwa bane a shirya yadda za'ai masa aikin" girgiza kai Dr yay cike da tausayawa yace "a halin da muke ciki babu halin yi masa wannan aikin"da mamaki Musty yace "but why?numfashi yaja yace "bamu da babban likita a yanzu kuma aikin na buƙatar kuɗi masu yawan gske,babban tashin hankalin shine indai aka huce ƙwana 2 ba'ai aikin ba aƙwai matsala so dole a fitar dashi"salatin kawai Musty yake gdy yaywa Dr kana ya miƙe ya nufi ɗakin da Baba habu yake,yana ƙwance sanye da drip numfashinsa na fita da sauri gaba ɗaya ya fita hayyacinsa,nan ya ƙwashe komai ya faɗawa Uwande,kuka ta saki sosai tare da faɗin "shikekan zan rasa mijina kamar yadda na rasa ƴarta wayyo Allah"rarrashinta ya shigayi sosai kana ya fice daga cikin room ɗin ya nufi compound na asibitin,rasa mai yake masa daɗi yay wata zuciyarta bashi shawara a kan ya kira Fahad yaji tunda likita ne,bai tsaya wani nazari ba ya danna masa kira,sun daɗe suna mgana kafin ya kashe kiran,yana gamawa ya shiga motar yabar asibitin bai dawo gida ba saida ya gama sama masu ticket gaba ɗayansu. Washe gari tun da safe suka gama shirinsu domin jirgin ƙarfe 8 zasu bi,suna isa airport 7:30 nayi suna zaune suka gama cike ciken komai Musty ya bada motarsa wajan security saida suka kammala kana suka shige jikin jirgin Musty waje guda suka zauna da Baba habu sai kuma Uwande a bayan kujerarsu, 8:5 dai jirginsu ya ɗaga zuwa paskitan. Cikin nutsuwa yake dreving motarsa tym to tym yana sakin murmushi tare da shafa ƙwantaccen gashin kanta,saida ya biya wani waje ya amshi saƙo cikin sauri kana ya ɗauki hanyar zuwa gida,tun daga nesa yake danna wani lafiyayyen horn da gudu mai gadi yazu ya buɗe masa get,da sauri ya cino hancin motar zuwa cikin farfajiyar gidan a rumfar ajjiye motoci yay parking kana ya fitu ɗauke da ita a jikinsa,yana tafe yana ƙara matseta cikin jikinsa wani daɗi ya keji haɗi da farin ciki yayinda wani sanyi yake ratsa sassan jikinsa,cike da izza haɗi ta kuzari yaci gaba da tafiya harya ƙarasa ƙofar babban parlour,cikin daddaɗan muryarsa yay sallama,cikin sauri Sufyan ya miƙe wanda ke zaune duk abu ya damesa duk inda yake tunanin ganin lapton ɗin abun yaci tura har bai san abinda zaice da Najma ba,domin yana son ya samu lapton dan ya ƙara zuwar mata da buƙatarsa,zuba masu idanu yay sai kuma yay saurin janye idanunsa sbd wani ƙwarjini da Fahad ɗin yay masa,ko mawa yay ya zauna yana wasi wasi a ransa,kai tsaye Fahad ya nufi sashinta da ita yana zuwa ya shimfiɗeta saman lafiyayyen royal bed ɗinsa tare da gyara mata ƙwanciya,da sauri ya ƙarasa wani ƙaramin ɗaki ya haɗu kayin drip tare da dawowa kusanta ya zauna,cikin sauri ya gama kammala saka mata drip ɗin kana ya haɗa injection wacce zata ƙara taimakawa jikin nata ya zuba cikin drip ɗin,kanta ya shafa tare da sauke mata kiss a gefen lips ɗinta cikin zazzaƙar muryarsa yace "luv u my baby girl, you're the rest of my life.. Mu'ahh 💋"ya ƙara sakar mata kiss tare daja mata duvet ya rufe mata jikinta,cikin nutsuwa ya juya tare da ficewa daga sashinsa ya nufi ɓangaren Lili domin zaɓu mata kayan sawa,nan yaga ikon Allah anyi kaca² da ɗakin kome ake nema ohhhu girgiza kai kawai yay kana ya nufi wadrube ɗinta ya zaɓu wata wasu ƙananun kaya masu ƙyan gske,dan yana ji ajikinsa yau shima zai angwance,ƙwasu kayan yay tare da komawa flat ɗinsa ya sakarwa kansa shower wanka yay sosai wanda ya manta rabon da yay kamarsa,cikin ya shafa wanda ya keji kamar zai haɗe da bayansa sbd yunwa,sai yanzu ya kejin yunwar dan rabon daya samu yaci wani abu a cikinsa ya manta,a gurguje ya kammala komai ya sanya wani haɗaɗɗan boyal mai ƙyan gske sosai kalan boyal ɗin yaywa fatansa ƙyau,orange ne wanda akai masa aiki da baƙin zare,sumar kansa ya gyara kana ya murza hula zanna bukar,wani lafiyayyen turare ya ɗauka mai daɗin ƙamshi ya fesa,yana gama komai ya juya ya zuba mata rikitattun idanunsa wanda suke cike da so da ƙaunarta haɗi da wutar sha'awarta yana jin yau ɗinnan maza tsallake tarƙwansa ba,a yau ɗin nan zai maidata cikakkiyar mace kamar kuwa, a yau ɗinan zai bada jindaɗi da farin ciki wanda ya fata ya kasance har ƙarshen rayuwarta, a yau ɗinan zai tune duk wani Juyayin da ɓoyayyen sirrin dake ƙwance cikin zuciyarsa,a yau ɗinan zai sata kuka,kukan farin ciki wanda zaiyi farin ciki da jinsa,ma dai² cin gemunsa ya shafa tare da lumshe idanunsa,cikin wani saɓon shauƙi daya samu kansa ya shiga takawa zuwa gareta. ```NIMCYLUV🤏🏼``` JUYAYI *54-55* Our TAURARUWA kiji daɗinki ina yinki irin sosai ɗinan😍😍 QUEEN NASMERT yabonki yaymin Sarauta taji daɗi har zuciyanta yay fess ina sonko har ƙasan zuci irin can can ɗinan ehhh kun gane ai,wannan page ɗin na kune halak malak rabbin rahama yay maku albarka👏🏻😘. Cikin tafiyarsa mai cike da izza haɗi da nutsuwa wacce take nuni da shiɗin naminmji ne ya ƙarasa gareta,zama kusanta tare da zuba mata narkakkun idanunsa wanda suke always sleepyn,cikin wata fitinannan shauƙi ya sunkuyar daf da fuskarta ya sakar mata wani lafiyayyen kiss mai tsayawa a zuciya,kanta ya shafa tare da sauke ajjiyar zuciya cikin wata narkakkiyar murya yace "kin zama jini da tsoka na jikina,keɗin garkuwa ce gareni ina sonki fiye da komai na rayuwarta,kin zama wani jigo na rayuwata i can't life without"ya kai ƙarshen maganar yana shafa cute pech lips ɗinta masu ɗan tudu,ya daɗe yana kallonta kafin ya miƙe ya nufi waje. A can parlour ya samu Mama da Momma sai Afnerh da Yusrah suna kallon wani Indian series film mai suna The Vow,gaba ɗaya hankalinsu naga film ɗin sbd sonda da suke masa,tafiya yake cike da kamala yana tafe yana sakin wani tattusan murmushi yaɗe da shafa sajensa zuwa gemonsa,bakinsa ɗauke da sallama ya shiga babban parlour waje ya samu ɗan nesa dasu tare da ɗauko wayarsa ya zubawa photon idanun yana ji kamar ya haɗiyeta ya huta,a yanzu ya rasata dai² yake da bugawar zuciyarsa da kuma taiwar numfashinsa wanda hakan zai tabbatar daya zama gawa,sam ya manta dasu Mama a ɗakin sai saukar muryarta da yaji tana faɗin "Yarona naji dadi Ubangiji rahama ya ƙara kareku da kariyarsa,ya rabaku da sharrin maƙiya da kuma mahassada Allah ya baka ikon kula da matarka"lumshe idanunsa yay sbd yaji dɗin addu'arta ɗan ware laɓɓansa yay cikin muryarsa mai daɗi yace ا مين يا رب العرش الكريم thank you soo much Mamana we really luv u"jinjina kai tayi zuciyarta fal farin cikin ƴarta ta dawo lafiya,Momma itama ta tayashi murna haka Yusrah da Afnerh,dake yana cikin farin ciki na abu biyu yau matansa ya dawo kusansa,yau yana tabbacin cikin yardar Allah shima zai angwan ce,wannan dalilin yasa ya kejin zuciyarsa fal farin ciki,saurin miƙewa yay yana ƙara gyara zaman bluetooth ɗin kunnansa,wayarsa ya ɗauka cikin sauri ya shiga kiran wata number ringing biyu tayi aka ɗauka cikin wata murya yace "ohhya maza kuje airport zasu bar gari"yana faɗin hakan ƙitt ya kashe wayar,yana ƙoƙarin fita Najma na shiguwa parlour da sassarfa ta ƙarasa wajansa tace "Brona nayi farin cikin dawowar rabin rai,daman wannan kuɗaɗan daka banine da kuma files shine nace bari na dawo maka dasu nayi tunani naga zamansu wajena baya da amfani"taɓe baki yay irin bai damu ɗinan ba,kamar bazai magana ba sai kuma yace "bawa Mamana" yana faɗin hakan yasa kai ya fice daga cikin gidan,Najama ta miƙawa Mama kamar yadda yace kuma tayi hakanne sbd dogaro da lapton ɗin da Sufyan zai ɗauko mata da tayi,Mama na amsa tayi cikin ɗakinta itama Najma ta juya zuwa ɓangarenta,tsaki Afnerh taja tana jin ranta duk a jagule wata tsanar Najman ta sauka cikin ranta tun ranar da wannan abin ya faru,ji tayi ba zata iya ƙarasa kallon ba ta miƙe tare da nufar sashinta. *** *** Gudu suke sosai a mota zuciyarsa fal farin ciki he get what he want ta cikin ruwan sanyi,daman yace saiya ɗauki fansar abinda Mamansu tayi masa naƙin aurensa da tayi,Baffade na ajjiye Lili daga mota ya ɗauki hanyar wani babban hotel dake garin bai wani daɗe ba ya ƙarasa ɗakin da oga ke cikinsa,yana shiga ya sameta a tsaye ya gama shirinsa na barin garin kafin a fara wani tunanin nemansa,jinjina kai Baffade yay tare da faɗin "oga ga lapton ɗin"wata dry wanda aka kira da Oga yay kafin ya fara jiyowa a hankali,ya salam nikaina saida na ware ido ganin mutumin da baiyi tunanin gani ba, FAIRUS ne cousin ɗin Mamy tsaye yana sheƙa dryar mugunta,cikin farin ciki yace "good Baffade ka shirya zuwa airport yanzu zamu bar gari"farin ciki ne ya bayyana fuskar Baffade yace "aini a shirye nake Oga muje kawai"yana faɗin hakan yay gaba shima Fairus ya taka masa baya,suna zuwa harabar hotel ɗin suka faɗa mota tare da janta da gudu suka nufi airport,basu daɗe ba suka ƙarasa suna zuwa wani jirgin na sauka,cikin sauri suka gama cike komai suka faɗa cikin jirgin suna jiran lkc yaya su tashi zuwa Cameroon,baifi 5minutes aka fara sanarwar kuwa ya ɗaura blet ɗinsa,jirgi na shirin tashi akai saurin dakatar dashi,wasu manyan jami'an S.V.I suka shigo passingers suka fara dubawa,hankalin Fairus ba ƙaramin tashi yay ba,ya shiga sadda kansa zuwa ƙasa,amma duk da hakan bai hana suƙi ganeshi ba,suna zuwa ƙansa suka ce "Fairus Haruna you are under arest" haka suka kamashi tare da mai take masa baya Baffade suka nufi cikin motarsu dashi suna zuwa suka cillashi tare da jan motar a guje. Wani shu'umin murmushi Fahad yay wanda ke gefe yana jiransu Musty su ƙarasu yakai Baba Habu hospital, lumshe idanunsa yay kana ya zare wani ƙaramin voice recoding daya maƙala cikin kunnansa,cikin muryar da take nuni da farin ciki yace "you are a loser malam Fairus Haruna"yana faɗin hakan ya cilla na'ourar da yay conecting da ita a jikin Baffade, (kada ku manta lkcn da Fahad yaje bawa Baffade lapton haryay tuntuɓe ya faɗa jikin baffade to yana sane yay hakan dan ya samu nasarar saka masa na'ourar ɗaukan magana da kuma wannan damar ya samu ya kamasu coz duk maganar da suke yana jinsu kuma yay recoding nata as evidence). Yana wannan tunananin yaji maganar Musty kusansa,da farin ciki ya rungome Musty kana ya amshi keken da ake tura Baba habu ya nufi wajan sabuwar motarsa cikin saurin suka sanyashi a mota kana Musty ya amshi dreving ɗin shi kuma ya koma side ɗin mai zaman banza,Uwande ta zauna kusan Baba habu a side ɗin baya,suka nufi wani sabun asibiti wanda Fahad ya buɗe ko ma'aikata bai zuba ba sbd wannan matsalar daya shiga. Kasan cewar gudu suke yasa basu jima ba suka ƙarasa *Hadnerh teaching hospital* a wani specail room aka saka Baba habu cikin sauri ya maƙala masu wasu manyan na'ourori a jikinsa tare da sanya masa Oxygen yana gamawa yace Uwande ta zauna a nan zuwa anjima Musty zai kawo mata abinci da kuma kayan sawa zuwa gobe za'ai masa Aiki,yana gama faɗin hakan ya juya suka bar ɗakin dake asibiti ne babba kuma ga tsaro yasa baiji fargabar ajjiyesu a cikinsa ba,suna zuwa harabar asibitin suka faɗa mota tare da hucewa zuwa gida. Jama'an C.v.i ɗin babu inda suka tsaya sai babban station ɗinsu dake pakistan,suna zuwa aka cillasu cikin dugun ɗaki mai duhun gske babu ɓata lkc aka cire kayan jikinsu kana aka ɗauresu a jikin wani ƙarfe suna kammalawa suka fice daga cikin duhun ɗakin,wani ne wanda shima yake a ɗauren ya ƙyalƙyale da dry kafin ya tsuke fuska yace "san zuciya ya kawoku kabarinku"zare ido Baffade yay alamar tsoro yace "kamarya?"shuru mutumin yay dan yawanci idan yay mgn ɗaya bai ƙarawa,wajanne ya ɗauki shuru kuwa da abinda yake tunani can wani yace "Ni mahaifina na kashe a kan na gaji sarauta kufa?"wata harara Fairus ya watsa masa yace "is not ur business"dry mutumin yay yace "ok nga gwamma musan juna kuma mu saba,idan kana tunanin fita a nan kayi ƙaryya saida gawarka ta fita daga nan badai kai ba"kuka Baffade yasa tare da faɗin "nidai ka cuceni wlh ko haƙƙin rayukan dana kashe bazasu barni ba,ni baƙin cikina ba bansan dalili da yasa kace na kashesu ba"shikansa Fairus ya shiga tashin hankali da fargaba hakan tasa yaja bakinsa yay shuru. Najma na shiga ɗaki taja wayarta tare da kiran number Sufyan cikin sa'a taji ya ɗauka kafin yay mgna tace "Sufyan u keep me waiting kasan ina cikin Juyayi ka ƙwamusheni kasa kullum kai nake tunani,sannan mgnar lapton naji shuru wlh...,"ƙitt ya kashe wayar ba tare data kammala ba,baki ta saki tana mamakin dalilinsa nayin hakan,sai kuma wata zuciyan tace kodai yana cikin mutane? Haka taita tunani a ranta har bacci ya ɗauketa. Misalin shida na yamma ta shiga buɗe idanunta wanda yay mata nauyin gske bakinta ɗauke da addu,ar tasgi daga bacci,drip ɗin hannunta tabi da idanu tana mamakin lkcn aka sanya mata,ganin ya ƙare yasa ta runtsa idanunta tarr da zare allurar daga jikinta,miƙewa tayi jiki a sanyaye ta nufi cikin bathroom ɗinsa ta haɗa ruwan zafi mai kana ta shiga cikin bathtub ɗin,lumshe ido tayi sbd ruwan yay mata daɗi ta daɗe cikin ruwan zafin kafin ta sauya wani tai wanka,sai lkcn taji ƙarfi a jikinta rabonta da wanka harta manta,a ɗan gaggauce tayi brush tare da ɗaura tana astagafirullah a ranta,cikin sauri ta shafa lotion mai daɗin ƙamshi kana ta sanya wata duhuwar abaya ta fesa turare samun kanta tayi da zizara ƙwalli da bby pink lipstic,sosai ta kalli kanta a madubi ganin tai wani ƙyau haɗe dayin wani fresh kamar ba ita ga,lallai babu abinda yafi zama da masoyi daɗi,hijab ta sanya kana ta shinfiɗa paryer mat ta tada sallah,ta daɗe tana addu'a kana ta shafa,wayarta ta ɗauka tare da kunna data ta shiga wattpad nan taga new posting na Nimcyluv wanda zata fara sabon book ɗinta na *The New Emir* sosai taji daɗi dan tasan book ɗin zai bada ma'ana how wanda baya ƙasar na kimanin shekara goma zai dawo gidan sarautar a lkcn da *kuyanga zarina* ta bayyana s matsayin baiwa, tayaya wanda yake matsayin *soja* zai zama *Emir* ? Small bro ɗinsa na sonta,yayinda *Sarki* maici a yanzu yake kiwata ta domin cimma buƙatarsa,shin zaibar hakan ta faru ko yaya? Cikin sauri ta shiga tai comment da _Sarauta pls ki fara posting ɗinsa wlh ko nawane zan baki_ tana gama yin send ta miƙa jin ana kiran sallar magrib,sallah ta gabatar kana ta ɗauki wayarta dan wata yunwa ta keji kamar me,direct waje ta nufa domin zuwa wajan Mama,tana hanya taji karar D.M cikin sauri ta duba ganin Nimcy ce. _Ga mata wajan Dr Fahad ardy kina cikin Vip so kada ki damu,wannan book ɗin koda ace na kuɗi ne to wlh Allah saida rabonka,na tura abu cikin Vip nasan zai maki amfani musamman yanzu da kike tare da mijinki😝_ Dry tayi kana tayi replay sannan tayi offline,dagu ta ƙarasa parloun tana kiran “Mamana” Mama dake zaune ta saki dry tace "aa kaga uwata kuma Mamana ur wlcm"dry Lili ta saki tana faɗawa jikin Mama,ganin babu kuwa a parlour'n yasa Mama rungome ƴarta tana sauke numfashi, "Mamana nayi missed naki sosai"ta faɗa lkcn da idanunta yake fitar da ƙwalla,goge mata hawayen tayi kana ta sumbaci forehead ɗinta tace "Uwata nima nayi missed naki sosai,komai ya ƙare tunda gaki ga Mamanki ko?"gyaɗa kai Lili tayi tare da shigewa jikin mahaifiyarta ta,tana jin wata nutsuwa na saukar mata,kama hannunta tayi tace "ohhya muje ki sama cikinki wani abu"jerawa sukai suka nufi flat ɗin Mama. Bayansu Fahad sunbar asibitin ya shiga bincike domin tabbatar da abinda yake zargi,saida suka ɗauki lkcn suna yawo kafin ya samu cikakken bayanin daga bakinda bazai masa ƙarya ba,kana suka huce wani botic suka ƙwashi kaya kamar hauka, suna fituwa suka nufi wani haɗaɗɗan wajan cin abinci yay masu take way masu yawa kana ya bada umarnin a zuba masa mayan gasassun kaji buda biyi a leda😂dai kuma ɓanƙararran kifi irin gashin larabawan nan shima guda biyu,kana a zuba masa juice masu daɗi da kuma tsada shima guda biyu,ana gamawa aka kai masa cikin mota ya biya kuɗin sannan suka koma cikin asibitin ya sauke Musty domin shine zai zauna dasu a cikin asibitin,kana ya juya zuwa gida zuciyarwa wasai sai sauke lafiyayyen murmushi danshi kaɗai yasan abinda ya shirya,saida ya tsaya ya gabatar da sallah magrib da isha'i sannan ya nufi gida. Yana zuwa ya shige cikin sashinsa tare da faɗawa toilet yay wanka versiline ya ɗauka mara zafi ya shiga shafawa naked body ɗinsa,yana gamawa ya sanya trouser a jikinsa tare da feshe jikinsa da wani lafiyayyen turare mai daɗin ƙamshi ga wani sanyi dake sanya zuciya nutsuwa,saman bed ya ƙwanta rigingine wayarsa ya ɗauka ya kira Mama tana ɗauka yace "ardy night a bani matana" yana faɗin hakan ya kashe wayan. Daman tasan za'a rina shiyasa ta sanya Lubna yin wanka ta shafeta da wata hadaɗɗiyar humura,kallon Lili tayi cikin tausayawa tace "Mamana mijinki na kira maza tashi"haka ta miƙe badan ranta yasu ba tayi sashinta,a babban parlour taga Sufyan hannunsa ɗauke da wata katuwar ƙwalba da alama,giya ce cikin sauri ta shige sashinsu,tana zuwa ta nufi sashin Fahad,bakinta ɗauke da sallama ta shiga tare da zama kusansa,kasa amsata yay sai kafeta yay da jajayen tsumammun idanunsa,hannu yasa ya fisgota zuwa jikinsa kana ya mirginata ƙasa tare da zare hijab ɗin jikinta,tsoro ne ya kamata ganin yadda gaba ɗaya jikinsa ke rawa,jikinta ta cure waje guda ganin harya rabata da kayan jikinta,hannu tasa ta shiga turesa cikin rawar murya ya ɗura bakinsa saman kunnanta yace"pls wify ban cutar dake"ya faɗi hakan lkcn da yake tura halshansa cikin kunnanta. _JUYAYI_ _Wattpad: *Nimcyluv*_ *56-57* Wannan page ɗin gaba ɗayansa sadaukarwa ne ga *M.K PLACE* ngd sosai da addu'oinku gareni ubangiji ya ƙaremu da lpa baki ɗayanmu,Allah yabar ƙauna da zumuchi ina maku sahihiyar ƙauna har zuci😘wlh ina sonku da gske mg special writers Allah ya ƙara mana basira da ɗaukaka baki ɗaya. Saukar numfashinsa cikin kunnanta yai² da ɗaukewar nafa numfashin sbd sabon yanayin daya saukar mata a yanzu,tsigar jikinta ne ya fara tashi ga wani abu mara daɗi daya shiga yi mata yawo a jiki,tsoro da fargaba gaba ɗaya sun gama cika mata zuciya,gaba ɗaya ta shiga ruɗu da juyayi domin ba tayi tunanin wannan abun a dai² wannan lkcn ba,kukawa ta shigayi da numfashinta dake ƙoƙarin ɗaukewa da gske,nayayin yadda naked body ɗinsa ya haɗu da fresh skin ɗinsa ya ƙara zautar dashi tare da ƙara tura tongue ɗinsa cikin kunnanta ya shiga guga mata sajen fuskarsa,a hankali ya janye jajayen laɓɓansa dagq cikin ears ɗinsa ya shiga manna mata kiss a naked body ɗinta,cikin salo ya ɗura tafin hannunsa a saman lafaffan cikinta ya shiga shafawa tare dayin sama dashi,wni ajjiyar zuciya ta sauke lkcn da taji saukar hannunsa saman albarkatunta,cikin fitar hayyaci ta shiga girgiza kanta sbd tsoran da yagama ratsa zuciyarta,jajayen narkakkun idanun ya zuba mata yana jin wani irin tausayinta na ratsa zuciyarsa,da ace zai iya rabuwa da ita da yay hakan amma shi kansa abin a tausaya masa ne,wani irin masifaffen feelings ne yake barazanar tarwatsa masa mara,a hankali yar copping face ɗinsu cikin daƙushasshiyar murya mai nuni da zallar abinda mutum keso yace "pls wify ki tausaya boobynki"ya faɗi hakan yana ƙara shigewa jikinta tare da ware laps ɗinta jikinsa na rawa da ɓari ya shiga neman hanya,zafi da raɗaɗin da taji ya fara tsata yasa ta buɗe baki zatai kuka yay saurin sanya bakinsa cikin nata ya shiga bata wani lafiyayyiyar sumba mai tsaya a zuciyar dukkan wanda akaiwa,runtsa idanunsa sbd jin yadda kansa ke tsarawa tare da juya masa,ganin idan baiyi da gske ba bazai taɓa samun hanya cikin wani guzari daya zo masa ya shiga karatu addu'ar dasuwa da iyali kana ya shiga jikinta da ƙarfi,ihu da ƙara suka saki lkcn guda yayinda tayi ihun a zaba data shige wacce bata taɓa tunanin aƙwai irinta lkcn kaɗan ta fita hayyacinta banda girgiza kai haɗe da taune bakinss dake cikin nata babu abinda take,nutsuwa farin ciki sune suka sauka a zuciyarsa da kuma gangar jikinsa,wasu hawayen farin ciki ne ya shiga fita daga cikin idanunsa yama rasa mai zaiyi gaurantakar zai sauke mata ko kuma tuzuruntakar jinsa yake a sama gaba ɗaya kansa ya juye cikin fitar hayyaci ya suma shige jikinta ya suma raya sunnar ma'aiki kamar yadda yazu a addini,banda surutai da sanya mata albarka babu abinda yake sosai yake raya daren cikin nutsuwa da kuma ƙwarewa kafin wani lkc baiwar Lili ta fita hayyacinta ko hannu bata iya ɗagawa sai hawaye dake ambaliya cikin idanunta,gaba ɗaya fuskarta ya haɗe majina hawaye ta haɗu tayi jajir,bai samu nutsuwa ba sai daf da kiran sallar asuba,kana ya saki wata ƙara tare da faɗa jikinta ya rungometa tsam a faffaɗan jikinsa ya suma fidda wani numfashi,lkc kaɗan wani zazzafan zazzaɓi ya rufesa su duka biyun,yayinda Fahad fever ɗinsa ke nuni daya samu kuma ya zama cikakken namiji kamar yadda yake fata,ya fitar da dukkan wani sifam ɗinsa wanda a koda yaushe yake takurasa gefe guda kuma ya juye dukkan wani sha'awarsa gareta dalilin hakan zazzaɓi ya rufesa,zafi da wahalar data sha ga kuma yanayin jikinta da ba lpa gareta hakan ya haifar mata da zazzaɓi cikin ƙashi haɗi dana fata,yadda take fitar da numfashi da ƙyar ne yasa shi dawowa hayyacinsa,a hankali ya zare jikinsa daga cikin jikinta tare da mirginawa gefe ya zuba mata gajiyayyun idanunsa yana jin wani sonta da ƙaunarta na ratsa sassan jikinsa,jawota yay jikinsa ya matseta ya shiga sanya mata albarka lafewa tayi jikinsa tana sauke numfashi murmushi yay tare da shafa mararta yace "ƙwailata kin sanyamin farin ciki wanda ban taɓa shigarsa ba,nayi imani da Allah yau ƙwaina zaikai ga raga nan da 9mouth zan sami beby Allah yay maki albarka"kanta ta cusa cikin ƙirjinsa ta sakar masa ciwo tare da ƙwaɓe baki ta shiga kukan shagwaɓa,dry yay mata cikin ɗauriya ya miƙe da ita a jikinsa suka nufi toilet,da kansa yay mata wanka kana tayi na tsarki kafin ta gama ya gyara ɗakin tare da sauya bedsheet, paryer mat ya shimfiɗa masu sannan ya tada sallah itama tayi a zaune tana sallah tana kuka har suka idar,ɗaukanta yay cak ya azata bisa bed kana ya cire jallabiyar jikinsa itama ya cire mata,sosai yay hugging ɗinta yana ɗan bubbuga bayanta,ƙoƙarin ƙwace kanta take amma ta kasa gane haka yasa a hankali ya sanya bakinsa cikin nata kana ya rufesu da duvet. Bayan Lubna tabar Sufyan a babban parlour yana shan giya,sai abun ya ƙara ta'azzara haka ya dinga ƙwanƙwaɗar giyar har saida ya shanye tas,cikin maye ya miƙe yana tangaɗi ya nufi ɗakin Afnerh,tana ƙwance taji an faɗo kanta ana shirin rabata da kaya jikinta,da sauri ta hankaɗesa yay baya sbd tun dga wannan ranar bata ƙra yadda dashi ba, ƙara kusanto ta yay ta ƙara ja baya da hannu ya shiga nunata yana lumshe idanu cikin sarƙewar murya yace "sai naga bayansa,Fahad ya shiga tarkuna yau shine zai ƙwanta da matar da nake sha'awa nake burin kasan cewa da ita,yay kaɗan saina kashe i will kill him ehhh na faɗa"nan ya dinga surutai marasa kan gado,ƙara nufuta yay tare da cillata kan gado ya faɗa samanta ta saki wata ƙara sbd wahala,ganin da gske so yake ya ƙwanta da ita ta sakar masa cizo a hannu babu shiri ya fara dawowa hayya cinsa ya zuba masa idanunta cike da takaici yace "kije ba'aso ma,ke bana sonki ma na sakeki saki biyu"yana fɗin hakan ya zari key ɗin mota yay waje,kuka ta saki tare dayin hamdala haka nan taji tayi farin ciki da sakin da yay mata,wajan 2 minutes ya dawo ya cillo mata takaddar saki tare da ficewa da sauri yana tan gaɗi,kuka ta shiga rerawa wanda bata san dalilin yinsa ba,a haka har bacci ya ɗauketa a wajan,Sufyan na fita ya faɗa cikin mota tare da janta a guje har wani tashi sama ta keyi kamar zata faɗi haka yayta yawo a wajan harya tsaya a wani haɗaɗdan club parking yay tare da shigewa ciki yana shiga idanunsa suka fada kan wata haɗaɗdiyar yarinya ƴar zamani wani yawo ya haɗiye nan take mararsa ta karta,yana cikin maye yaje yaja yarinyar suka nufi wani ɗaki cikin son ransa da kuma rashin tsoran Allah suka shiga aikata alfasha _(Ubangiji ya tsaremu da tsarewarsa ka rabu sa son zuciya irin wannan Allah kasa mana tawakkali)_ haka suka dinga lalata har kiran sallar asuba. Ango da Amarya basu tashi ba sai wajan 12😝soyayya daɗi,a tare suka buɗe idanu tare da saukesu a cikin idanun junansu,ko wanne na wassafa irin son da yakewa ɗan uwansa,murmushin ƙarfin hali ta saki dan bata son nuna masa gazawarta,hannu tasa ta shafi sajensa cikin daddaɗar muryarta tace "mrng my happiness"sumar kanta ya shafa kana ya murza lips ɗinta yace "mrng too my ƙwailata"turo baki tayi ta shafi lallausan gashin ƙirjinsa cikin shagwaɓa tce "uhm uhm a'a"gira ya ɗaga mata cikin do da ƙauna ya sunkuceta sama ya nufi bathroom da ita. Sai wajan 1 suka gama shiryawa ya mata magani tasha kana ya rufeta da bargo,hancinta yaja yace "u're my life my happiness kice komai nawa"ya faɗi hakan yana sakar mata kiss a gefen lips ɗinta,kana yay waje tare da rufe mata ƙofar,gana ganinsa zaka san yana cikin farin ciki da ƙwanciyar hankali. Rayuwa kenan anyiwa baba Habu aiki kuma an samu nasara,yayinda a ƙwana biyun nan Amarya kuma Uwar gida take fama da ciwon kai bata cin komai sai chocolate ƙwaɗon zugala,gwajin farko a tabbatar da shigar ciki na sati biyu,farin ciki wajan Fahad ba'a mgn haka ya dinga rabon kuɗi wa almajirai da kuma masallatai,a wannan ranar kuma lili ta nuna masa ƙadarorinsa wanda ta maida cikin email ɗinta saida yay sujudul shukkuri yaywa ubangiji gdy. Najma uwar biyu itama ta kamu da samun ciki na tsawon sati uku,wanda ta tabbatar cikin Sufyanne sosai ta shiga tashin hankali ta fara ladamar haɗin kan data basa taci kuka ta gode Allah. Yau aka sallami Baba habu daga asibiti a hankali Fahad yay parking a compund na gidan ya fitu,yana gama Uwande na bayansa sai Musty daya riƙe baba habu a haka suka ƙarasu cikin,Da farin ciki Mama ta amshesu Fahad wajan matarsa ya nufa ya zauna kusanta,idan mutane ya faka ya sakar mata kisa kana ya aza ƙafartaa saman cinyarta ya shiga matsa mata,hakan yay mata ta lafe cikinsa babu jimawa bacci yay gaba da ita,Haba habu da Musty suka nufi ɗakin da aka basu kana uwande ta zauna suna hira da Mama,Najma ce tai sallama tare da shigowa cikin parlour,Uwande ce ta ɗago kai cikin sauri ta miƙe tare da nuna Najma da hannu cikin ɗaga murya tace "Hansai!!!! *_sorry guys kunjini shuru wlh bana da lpa 2days ina ƙwace a hospital🙁ku sani a addu'arku dan Allah dan Annabi kuyi share,kada ku manta ina buƙatar comments ɗinku 😍😘dan Allah ai comments_* _JUYAYI_ _Wattpad *Nimcyluv*_ *58-59* *_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ "Hansai!" shine abinda Uwande ta ƙara faɗe lkcn da take tun karar Najam,gaba ɗaya mutanan wajan suka zubawa Uwande idanu hatta Fahad dake ɗan matsawa Lili ƙafa kallonta yay na wani lkcn kafin ya ɗauke kansa ya maida ga matarsa yaci gaba da abida yake hankali ƙwance,ganin matar tana kusantu ta kuma gaba ɗaya ta birgice sai Hansai take faɗi yasa Najma ƙwasa da gudu tayi bayan Mama😂 _(Uwande taga Hansai chajiii)_ ,Mama ce tayi juriya da kuma ƙarfin halin kallon matar tace "Ƴar wacce Hansai kuma?"cikin rawar murya Uwande tace "ɗiyata Hansai wlh ita ne,Allahu akbar daman nasa tana raye tunda har yau ban daina mafalkinta ba"kafin Mama tayi mgn Afnerh ta gyara zama tace "ayya Umma kila kamace kawai amma wannan sister tane her name is Najma how zata zama Hansai bayan bata taɓa saninki ba as her mother🤔"ta faɗa riƙe haɓa alamar mamaki,jinjina kai Mama tayi kana tace "gsky ne Dota amma bri naji ko tana da wata hujja halan..."bata da wata hujja kawai da kama ce"cewar Musty dake shiguwa bayan ya ƙwantar da Baba habu daga ɗaki"Fahad wanda tunda suka fara mgn baice komai ba ta matarsa yake wacce yake jinta a cikin zuciyarsa ta zama komai nasa ya kalli Musty tare da haɗe fuska yace "meye naka kai? Koka fita sanin yar cikinta ne so let her talk abeg"shuru Musty yay ya zubawa Afnerh idanu wacce itama shi take kallo,murmushi ya sakar mata kana ya nemi wajan zama yana jiran jin lukutar mgnar da Kakar tasa zata sake faɗe,Afnerh ɗauke kai tayi nan taji zaman ya fara damunta coz duk wani juyi nata tana jin idanunsa na yawo a kanta, majinar dake fituwa a hancinta ta sharce cikin kuka tace "tabbas aƙwai shaida a jikin ƴarta idan har aka duba babu ita na sallama na amince ɗiyata bata raye"dry Musty yay yana jin maganar nata kamar ta wanda ya samu tamun brain yace "to Uwar gidana faɗi muji"guge hawayen fuskarta tayi tace "tun Hansai na jaririya nayi mata shaida a gefen cikinta ta hanyar zana mata farko sunanta da reza"Najma najin hakan tayi saurin ƙanƙame jikinta tare da sakin wani kuka mai ciwo sbd alrdy tasan aƙwai abinda yake ɓoye a jikinta wanda ita ta san da zamansa,jawota Mama tayi cikin muryar rarrashi tace "meye na kuka Dota bari na duba wannan labarin babbane fa"ƙara dunƙule jikinta tayi cikin kuka tace "no Mama i nver be her daugter dan Allah let go of me "tsawar da Fahad ya daka mata itane tasa ta dawo cikin nutsuwarta cikin nutsuwa da kamala yace "wanne irin shirme ne wannan kina abu kmar ƴar local area dan malama ki tsaya"ya faɗi hakan yana bubbuga bayan Lili wacce take shirin farkawa daga baccin daya ɗauketa jikin booby,a hankali Mama ta shiga ɗaga rigar dake jikin Najma,yayinda Najma jikinta duka rawa yake dan ba tayi expecting wannan abun nada a laƙa da rayuwanta ba,da saurin Mama ta saki rigar tare da zabga salati sosai idanunta suka sauka a gefen cikin Najma wanda zannan harafin “H” ya fitu ɓaro²,Uwande kam zubewa tayi kan ƙafatunta tare dayiwa Allah gdy daya bayyana mata ɗiyarta wacce ta mallaka,Fahad kasa mgn yay sbd wani tsoro daya kamashi tayaya zata zama ƴarta tsahun wannan lkcn ba tare sunga wata shaida ba,Musty da Afnerh baki suka saki sunma kasa cewa komai sbd tsoro a lkcnne Sufyan ya shigo cikin parlour tare da zama ya zubawa afnerh ido wacce a yanzu yake jin wani mugun sonta na ratsa zuciyarsa,gaba ɗaya wajan ya ɗauki shuru cikin dakiya Mama tace "Yarona kayi shuru,shin Yaya Mustapha ya taɓa gaya maka zancd makamanci wannan kam?"girgiza kansa yay kafin kuma yace "Wait Mamana bani 2min"yana faɗin hakan ya sunkuci matarsa cikin tafiyarsa mai cike da taƙama ya nufi sashinta da ita. Yana zuwa ya shimfiɗeta saman royal bed ɗinsa tare da zare mata hijab ɗin jikinta ya shafi kanta yace rest of my life, Luv u wify na, muu'ahh💋" ya sakar mata kiss tsakiyar forehead ɗinta kana ya buɗe inda yake ajjiye muhimman abunsa,yana zuwa wajan ƴar ƙaramar box ɗin ya danna pin ɗin jiki mai haraɗin. “H A D N E R H” Yana gama rubutawa box ɗin ta wangane cikin sauri ya ɗauki wasiyar da Daddy ya bashi yace karya buɗe saiya rasa mafita,yana ɗauka ya rufe box ɗin yay waje,yana zuwa ya miƙawa Mama taƙaddar dan bai yarda ya buɗe ba,kallon mutanan wajan tayi kana ta mayar da hankalinta kan taƙaddar ta shiga karanta kamar haka. _Banson na ɓoye wannan sirrin ba,domin ya kasa the big secret issues kuma ya kasance abunda zaisa zuciyoyinku *JUYAYI* amma banyi hakan da wata manufa ba saidai nuna cewa kuɗin gaba ɗaya matsayin ƴar yar na ɗaukeku,amma a zahiri bana da wani ɗa daya huce FAHAD shine ya ratsa jini da tsokata yazu duniya,LUBNA kusan wacece ita kamar yadda na faɗa a baya yanzu kuma ina magana a kan NAJMA ne,a zahiri sunanta HAFSAT na tsinceta ne a kan hanya ta dawowa gida daga Yola zuwa kano,na tsinceta ne cikin zanin goyanta haɗe da wata taƙadda wacce ta ɗauke da rubutu kamar haka *Sunanta Hafsatu dukkan wanda ya tsinceta anbar masa halak malak* a ranar dana ɗauketa lkcn Fahad yay shekara guda da tafiya karatu Mama kuma bata gari sunje ƙasa mai tsarki ita da mijinta,tun daga wannan ranar na ɗauketa na sauya mata suna kuma na maidata kamar ƴar dana haifa a cikina domin in ganta rayuwarta,dan haka ko bayan babu raina na bata gidana guda ɗaya da kuma company na dake nan kano domin bata da gado na,wannan shine abinda zance game da rayuwar Najma wacce a yanzu take matsayin Hafsatu_ _Alhj Mustapha Rano_ _Sun/dec/2021_ ~MSRN~ Tana gama karantawa da yaga taƙaddar tare dajan Numshi,Najma kam nan take wani ƙunci ya gama ziyarta zuciyarta na dama da dana sani ta gama sauka cikin zuciyarta da kuma gangar jikinta,Fahad kam shuru yay yana girmama hukunci ubangiji domin wannan abun ba ƙaramin tsaya masa rai yay ba,dan wannan ƙaddarar zata iya faɗawa kan kowa shiyasa a koda yaushe akeso ka zama na gari mai tsoron Allah da kuma ƙyautatawa mutane amma ita gashi san zuciya yana shirin kaita ga halaka,a kullum idan ya tuna cikin jikinta dake manne a jikinta baya iya bacci,gashi cikin ikon Allah ya tsarkake zuri'arsu daman duk wani ɗa nagari bazai so tuzarta ahalinsa ba, koda wannan ubangiji ya barta aita gama jin kunyar duniya haka yayta zancen zucinsa ba tare daya ce ƙala ba,Momma da zuwanta kenan ta shiga bawa Najma hqr haɗe da nusar da ita yarda da ƙaddara,miƙewa tayi ba tare data kula kuwa ba tayi cikin ɗakinta,Uwande ta nufi ɗakin da aka ƙwantar da Baba habu wanda a yanzu ya zama _(Uban Hansai😂)_ zuciyarta fal farin ciki,Musty da Fahad kuma sukayi waje Sufyan kuma ya nufi ɗakinsa Yayinda Mama kuma ta nufi kichen domin haɗawa Lili ƙwaɗon zugala. *** **** Ina labarin Dr Laylerh tun lkcn data sami labarin mutuwar Dr Fahad Mustapha Rano shine iyayensa da kuma ƙanwarsa Lili wacce yanzu take matsayin mata garesa,ta shiga tashin hankali tayi kuka kamar ranta zai fita da ƙyar iyyensa suka rarrasheta harta amince da auren cousin ɗinta Saydeek zuwa yanzu tana tana da yaro guda ɗaya wanda yaci sunan Fahad,sai ƙaramin ciki kimanin watanni uku kenan data ɗauke dashi,haka take zaune da mijinta cikin soda ƙauna basu taɓa samun matsala ba sai lkcn da tace tana son a sama ɗanta sunan Fahad yace bai yarda ba,nan fa tace saida ya bata saki dan ba zata zauna ba,haka ya hqr aka saka sunan dake yana sonta daga wannan basu ƙara samun matsala ba. _Mai duguri road_ Ammi Papa sosai sukaji baƙin cikin abinda Najma tayi masu a nan kuma suka fahimci kuskuren da suka tafka na amincewa da aurenta sa sukai,Ammi tayi kuka harta gaji domin gani take itane silan mutuwar ɗanta Faisal,kullum cikin nema masa Rahama ubangiji suke har suka hqr,cikin ikon Allah kuma raguwar kadarorinsa da suka rage suka ƙaramun samun albarka kullum buɗi ake samu ta ɓangarensu,Anty Khausar da ƙara haihuwar ɗa namiji yaci sunan Faisal inda ake kiransa da little. *** *** Bayan wata taƙwas Sosai cikin Lili da Najma ya girma kuma ya shiga cikin watannin haihuwa,sosai Lubna ke samun kulawa wajan mijinta abin alfaharinta,bata da wata matsala saita girman cikinta wanda ya sauya mata kama ta zama ƙatuwa ga wani uban haske da ƙiba da tayi,kullum cikin kuka take ita ta gaji a cire cikin ta huta kawai,haka zai lalace wajan bata hqr da kalamai masu daɗi da kuma sanya nutsuwa a zuciya. Soyayya tsakanin Afnerh da Musty ta ɓalle sosai suke nunawa junansu ƙauna,yayinsa Sufyan aka yanke shawarar haɗashi aure da Najma bayan ta haihu. Yauta kama ranar da aka ɗaurawa Afnerh da Musty aure a kuma ranar ne Najma ta sauka cikin rashin sa'a ta samu yayyun fitsarin sbd hawalar data sha kafin haihuwar,duk yadda Fahad yasu gujewar faruwar hakan amma abin ya gagaresa haka aka maƙala mata rubar fitsari abun tausayi,a wannan ranar kuma aka ɗaura auren Sufyan da Najma dan Alhajin Sufyan yace aure babu fashi sbd dukkan abinda ya sameta ai dalilinsa ne tunda cikin sane ba,dan haka aka ɗaura aure gaban shaidun kowa. Nan abu yaywa Sufyan yawa gani a karo na biyu ya ƙara rasa wacce ya keso sbd son zuciyarsa ga kuma baƙin cikin abinda ya samu Najman,ga ɗan shege daya samu da ƙuruciyarsa cikin tashin hankali ya ɗauki key ɗin mota yay waje,yana zuwa ya faɗa motar ya jata da gudu kamar za'a tashi sama,sosai yake gudu cikin fitar hayyaci ba tare daya san inda zashi ba,cikin rashin sa'a motar ta ƙwace masa ta daki wata bishiya take gefen titi,na motar tai wata katantanwa ta kifa lkc kaɗan ta fara hayaƙi kafin kace me mutane harsun rufe majan da ƙyar aka fitu da Sufyan daga cikin motar,kamar jira ake motar ta kama da wuta, ambulance ce ta ɗaukesa suka nufi asibutin *Hadnerh teaching hospital* nan Dr Fahad da wasu likitoci suka rufu a kansa da ƙyar aka tsaida jinin dake zuba a ƙasansa sbd wani ƙarfe daya cakesa,sun ɗauki lkcn mai ɗan tsahu kafin su shawo kan matsalar,gumi Fahad ya goge tare da fesar da wata iska cikin bakinsa a hankali ya furta 'Innalillahi wa'inna ilaihur raji'un" wani Dr dake gefensa yace "lafiya?" girgiza kai Fahad yay tare da faɗin "Mazantakarsa ta daina aiki😱. _Daga gobe ne fa🤾🏻‍♀️🤾🏻‍♀️🤾🏻‍♀️kawai kuci gaba da bina kamar yadda kuka saba kada ku kaji,farin cikina ku kasance dani kuma kuso littafaina wanda nake kawowa,jin daɗi na kuma kuyi share ɗinsu zuwa wani wajan idan kukai hakan kun faranta raina 😍🥰 *THE NEW EMIR* is loading kada ayi babu ke kada kice baki san da zamansa,shi naso farayi na fasa na fara Juyayi sbd ban gama bincike a kansa ba,so dan Allah dan Annabi ba danni ba dukkan inda ki kaga *THE NEW EMIR* kiyi share ɗinsa zuwa grps ɗin da kike ciki wannan shi nake buƙata ku riƙe comments abunku na yafe🤣_ _JUYAYI_ _Wattpad: *Nimcyluv*_ *60-61* _*@Telegram*_ https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ *_FINALLY🤾🏻‍♀️✋🏼_* Masha Allah,yau Mon/Feb/15 Ubangiji ya bani ikon kammala JUYAYI so a tayani da addu'a. Ƙawayen amana😅 My Heroine kuma jaruma jagora a book ɗina na THE NEW EMIR. Hajajju Haseenatu autar manya banda ni😟taƙi bani ƙyautar page halan sai taje yin ZARAFI. Fatima bintu mss flower kina zuciyata😍, Fauziya s madaki dole na sakaki,My Star bazan mance dake ba, Queen Nasmert kema kina side ɗina😘 Antyna Hassana Ɗan larabawa har yau bani da bakin gode maki, Ummu Najma babar gayya kenan,Zee kumurya dole nace maki weldone,my sister Nanatou ina yinki thank you😍kai ysin kuna da yawa ga jama'ar *M.K Place*. Ƴan uwa nagari kuma ina gdy sosai Allah yabar zumunci. Muhammad ibrahim ango Bro Mu'az N.Yareema Fast class Abbakar Ak saraki 80k Muhammad Kareem Al'ameen Its saydeek Hassan tanko Hassan basiru Gaba ɗaya book ɗinnan sadaukar wane ga mahaifina *ALHJI SULAIMAN SHU'AIBU DAGACIN JA'OJI* Zaro idanu Dr yay tare da faɗin "what ta daina aiki ya subuhanallah" girgiza kai kawai Fahad yay tare da ficewa da cikin room ɗin,shima Dr rufa masa baya yay suka fice daga cikin ɗakin yana mai jin tausayin Sufyan a zuciyarsa domin wannan ba ƙaramar lalura bace,da wannan tunanin ya koma office ɗinsa ya fara duba marasa lpa,Fahad ma Office ɗinsa ya shige yana zuwa Momma da Alhaji tare dasu Mama suka shiga tambayarsa abinda yake faruwa,zare glass ɗin idanunsa yay tare da fesar da wani huci mai zafi cikin sanyin murya mai tattare da nutsuwa yace"Alhaji saidai aiwa Sufyan addu'a kawai"cikin firgici da tashin hankali Unlce yace "kamarya?"kasa bashi amsa yay sai sadda kansa ƙasa da yay,Momma fashewa tayi da kuka cikin ɓacin rai Uncle yace"wai Fahad mu zaka saka cikin zullumi ko me?"cike da kunya Fahad ya shigayi masu bayanin abinda ya samu Sufyan ɗin,shuru wajan ya ɗauka kowa da abinda yake tunani a ransa,kukan da Momma ta ƙara fashewa da shine yaja hankalinsu cikin muryar ladama mai cike da tausayi tace" wannan ranar nake guje maka Sufyan,ranar da maka isa ka tseratar da kanka a kan abinda kai ka jawa kanka,duk yadda nasu na nusar dakai abinda kake ma dai² bane amma ka gagara fahimta sam,ka maida hulda da mata tamkar ruwan shanka kaƙi aure kaƙi fahimtar abinda kake ba dai² bane,gashi tun ba'aje ko inaba Ubangiji ya nuna maka kai ba komai bane,ka cuci kanka Sufyan ka cucemu amma bazan maka baki ba abinda ubangiji ya ɗura maka kaɗai ya isheka"takai ƙarshen maganar lkcn da take ficewa daga office ɗin. Unlce ne ya jinjina girman abin kafin yace "Ubangihin rahama ya yaye masa wannan lukutin iftila'i"Ameen Fahad Alhaji suka faɗa kana suka miƙe gaba ɗaya sukai waje,Direct room ɗin da aka ƙwantar da Sufyan suka shiga lkcn ya farka sai kuka yake Mama da Momma da Yusrah na gefensa suna bashi hqr banda sunan Fahad da Lili babu abinda yake kira,ana haka suka shigo baki ɗayansu,yana ganin Fahad yay saurin ɗauke kai sbd wata kunyarsa data kamashi,cikin muryar kuka wacce take nuni da zallar ladama yace"haƙiƙa nasu cutar da bayin Allah'n da basu jiba basu gani ba,idan nace zan faɗi abinda nayi tabbas nai ƙarya ina roƙanka daka yafemin kaji da tausayina,wlh nasan haƙƙinku bazai barni ba haƙiƙa bazai barni inji daɗi wannan duniyar ba,inajin zafi da ciwo a raina kuma ina mai cike da ladamar abinda na aikata maka dan Allah ka yafeni pls" Murmushi Fahad yay danku guda mai riƙi Sufyan a ransa domin yana sane da dukkan abinda ya aikata masa,cikin kuzari da nagartarsa yace "babu komai ubangiji ya yafemu baki ɗaya"Ameen aka amsa gaba ɗaya sannan suka nufi ɗakin da aka ƙwantar da Najma,da sauri suka rufe hanci sbd wani zarni daya daki hancinsu,shikam Fahad ko ajikinsa,nan ma kuka ta shigayi tare da neman gafararsu,nan Fahad yace babu komai Allah ya bata lpa ya kuma raya abinda ta samu,ana haka aka kirasa Lili babu lpa da guda ya ƙwasa tare da ɗaukan dukkan abinda yake buƙata na karɓar haihuwa,cikin sauri ya isa gidan lkcn tazu daf da haihuwar da bata sha wata wahala ba sosai,Uwande da Afnerh ce wajanta sai kuma Fannerh da zuwanta kenan,yana zuwa ya sunkuci matarsa ya nufi sashinsa sa ita,cikin ƙwarewarsa ta likitoci ya shiga bata taimaƙon gaggawa,yana jin wani irin tausayinta na ratsa jikinsa da zuciyarsa,cikin hukuncin ubangiji da kuma taimakonsa ta samu nasarar haifu ƙyaƙƙyawar yarinyarta fara tas mai kama da mahaifinta,cikin sauri ya ɗauki ya yanke mata cibi tare da mannata a ƙirjin mahaifiyarta wacce bata cikin nutsuwarta,cikin farin ciki yakai goshinsa ƙasa yaywa Ubangiji gdy tare dayi masa kirari,cikin sauri ya goge jikin ƴar tas da man zaitun ya shiryata cikin kayansa masu ƙyau da taushi kana ya ɗauki showel ya goyeta😂ya dawo kan uwar,kafin wani lkc ya gyara uwa da ƴarta tsaf ya shimfiɗesu saman makaken gandonsa sai bacci suke gwanin sha'awa,sashinsa ya gyara tas ba zaka taɓa cewa anyi haihuwa ba sai zabga ƙamshi gidan yake,shima yay wanka tare da gyara jikinsa farin ciki dake ƙwance saman fuskarsa sam yaƙi ɓoyowa,yana jin wani on top wanda yafi kuwa dace da samu mace ƙamila kuma nagartacciya mai tsayawa akan al'amurar mijinta da gidanta baki ɗaya. Ranar suna yarinya taci sunan *Khadija* mahaifiyar Fahad sai suka bata nick name mai daɗi ana kiranta da *Hibbat* sunan yarinya ta shiga ran kowa sbd farin jini gareta,ƙyaƙƙyawa ce ajin farko komai na fahimta babu inda ta barsa hakan yaywa Lili daɗi sbd kamar da tayo ta farin cikinta kuma mahaɗin rayuwarta,sun samu gift wajan mutane da yawa inda Mama ta bawa jaririya ƙyautar gida Uncle kuma ya bata ƙyautar mota,Fauwaz kan abubuwan da yay ba'a magana hakama Musty,Uba kuma jagora viza tafiya ƙasa mai tsarki yay masu dashi da iyalansa. *** **** Bayan wata 8 abubuwa da yawa sun faru daga ciki har hukucin da aka yankewa Fairus da Baffade,wata kam hukuncin KISA ta hanyar rataya,sosai sukai kuka kuma suka amshi hukuncin da akai masu domin shine jin daɗinsu an fidda haƙƙin Allah jikinsu. Najma kuma ta samu lpa sbd kulawar da Fahad ke bata,kuma taje ta roƙi gafarar Iyayen Faisal,abu ɗaya ke damunsu rashin lpar Sufyan wanda kuma samuwarta sai wani hukunci na Ubangiji. Yusra amarya ita tayi aure harta cikinsa samun shiga saidai muce ubangiji ya bada zama lpa,Allah ya sauki Afnerh ta samu ɗa namiji inda aka saka masa sunan Daddy ana kiransa da *Muhib*. Arziƙi sosai ya bunƙasu wajan Fahad sbd taimako da yake abin sai san barka,sosai suke kulawa da Junansu,yayinda Lubna ta zama uwar bata ta zama babbar mace ajin farko,yarinyarta tai wayo sosai amma ba tayo iyayenta ba sbd shegen surutu gareta,sunje Nigeria a nan suka haɗu da Dr Lalyerh sosai yaji daɗin ganin lil Fahad taƙwaransa,haka yay mata alheri domin daman sallama yazu masu a gobe jirginsu zai ɗaga zuwa ƙasa mai tsarki. Suna zaune jikin jirgi manne da juna,hannunsa ya cusa cikin mararta da mamaki da kallesa kuma ta kalli mutane wajan,gira ta ɗaga masa alamar tambaya🤨,murmushi ya sakar mata yace "vry soon zan saki ajjiyar ƙwaina kuma jinina"lafewa jikinsa tayi tare da shafar sajen fuskarsa tace"zanso hakan nima domin na tara maka iyali masu albarka gwarzon mijina abin alfaharina"kiss ya mannata yace "dat's good idea ƙwailata"ya faɗa yana shafa ramin cibiyarta,baki ta tura ceke da shagwaɓa yana shirin haɗe bakinsu *Hibbat* ta shige tsakiyarsa tare da faɗin "Papi mima" ta faɗa cike da gwaranci,dry sukai gaba ɗaya kana suka sun baci kuncinta a tare,cike da soyayya Dr Fahad Mustapha Rano ya rungume iyalinsa,a dai² nan kuma jirginsu ya fara harbawa sararin samaniya,cikin daddaɗar Murya Lubna tace _"Allahamdulillah"_ Allahamdulillah Nima na ƙara faɗe lkcn da nake sauke hannuna a kan wayata ta rubuta labarin *JUYAYI* bazance komai sai gdy,nasan dole aƙwai kuskure amma dai² yafi kuskuren yawa,abin na faɗa dai² Ubangiji yaban ladansa Wanda nai kuskure Allah ka yafewa baiwarka Ni'eemerh,Ina gdy da dukkan wanda suka kance dani a lkcn da nke rubuta wannan labarin ƴan manata kuma fans ɗina, *Sarauta place ina gdy*🥰 *Juyayi fans ina gdy* 😚 *Nimcyluv place on telegram ina gdy* 😍 *my fans my happiness kai gsky na yaba maku my readers on WATTPAD thank you soo much* sai kuma sauran grps kuyi hqr kuna raina sosai. Dan Allah ina jiran comments ɗinku mai ma'ana kada a bani kunya wannan shine last a juyayi,and don't forget wlh it gonna be damn yes kada ayi babu ke ko kai,dan zaka ciji yatsa😅😅😅😂amma da sauƙi idan banawa za'a ciza ba ahha *The New Emir* ya kusa. Mai ƙorafi ko gdy gareni 08119237616 *_Tammat bi hamdillah_*