Showing 12001 words to 15000 words out of 26511 words

Chapter 5 - Darajar Yayana 3 by Halima Abdullahi K Mashi .pdf

bayan nasan tana ranka.Aliyu ya
ce, tsakani da Allah sai ka tuna min.Usman ya ce,
ok, tunda yanxu iya ta yarda dole ka manta.Aliyu
ya ce subuhanalla? Dama wai Sadiya kake
magana?To wacce hira kuma zamuyi tun da na
rigaya an gama magana, sai jiran lokaci.Usman ya
ce, ai duk da haka za aje ayi hira ta san abinda
baka so don a samu zaman lafiya.Aliyu yayi yar
dariya.To ni ba haka tsarina ya ke ba, ina zaton
in har zanje gurin budurwa zan jene don ina
tallata kaina in in samu shiga,tonina riga na
samu shiga babu dalilin da zan matsawa
kaina.Usman ya ja tsaki kai dai bahago ne wlh, to
sai ka sai mata waya ko ta waya kunyi
magana.Aliyu ya ce, to yan zu dai kaine sarkin
yakinta ko?Suka sa dariya.Usman ya ce, da gaske
nikeyi, akwai wata waya da ake saidawa mai kyau
nan kusa daoffice din mu (MTN OFFICE) ya ke
aiki.Aliyu ya ce, ka suyo mata in kazo sai na baka
kudin, sanan kai zaka bata don har karshen satin
nan ban san lokacin dawowata, kafin ita ta tashi
na fita.Usman ya ce shi kenan.Washegari da
daddare ya usman yazo ya kawo mun waya wai
iji yaya Aliyu, inyi hakuriza mu rinka waya aikine
yayi masa yawa.Bani da zabi dole na hakura
tunda ga waya har da layin (MTN) ko da na nuwa
wa iya baki ta tabe sanan ta ce Allah ya sa
alheri.Tun da na karbi wayar ko flashing ba a
taba yi mun ba, ga dai lambarshi a ciki ya usman
ya samun duk da cewa har da kudi a layin nawa
nima cewa nayi ba zan kira shi ba.Sai dai in ta
kiran kawaye da yan uwa wadanda nake da
number su.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Wata rana da dadare naji Iya tana yi masa fada
cewa yana zaton haka za ayi auren ba lefe, biki
saura wata daya da kwanaki, amma ba a ga yana
motsi ba.Ya ce, abin ne ya shige masa, amma
gobe zai je ya sami matar ya sulaiman.Ita da
matar Usman Anty Abida sukai ta zaryar zuwa
kasuwa, saura sati biyu lefe ya kammala da dinki
da komai.Iya ta ce ya Aliyu ya bada kudin mota a
kaisu zariya, ni kuma nan kawaye na sun matsa
da batun anko, lokaci yana tafiya gashi ba zan iya
yi mashi magana ba.Aisha ta ce, kiyi wa iya
magana.Na ce, iya kwana biyu bata sana'a , bata
da kudin anko?Tab! Ba zai yuwu ba.Wayata na
dauka inyi kamar zan kira shi in fasa, Aisha ta
amsa na ce kada ki kira shi dan bai taba kira na
ba, ba wani kiranshi da nima zanyi Allah aisha ni
auren nan tuni ya fitan min daga rai.Ace kai kafi
karfin kazo sai dai abokinka?Aisha ta ce, Allah sai
na rubuta masa tex.Ina kallonta ta rubuta
masa.SALAM.INA FATAN KANA LAFIYA?KAYI
HAKURI KILA YANXU KANA CIKIN AIKI NA TSAIDA
KA, DA MA NAYI MAKA WANAN MESSAGE DIN NE
DON NA TAMBAYEKA A KAN MAGANAR ANKO,
DONKAWAYENA SUN DAMU SABODA LOKACI YANA
KAREWA.NA GODE, KA HUTA LAFIYA.Tana gama
rubutawa ta tura masa, maji amsa-maji amsa
shiru, nace kin gani ko?Ke ayi biki haka bani kara
masa batun anko.Aisha ta ce, niko yanda yake
nashi salon birge ni yake, na ce, au!Wulakancin
da yake min din ne yake burgeki?Tayi dariya, ai
ba wulakanci bane rayuwar sa ce haka.
Lokacin yana office din commissiner ya je a kan
nemansa da yayi tsam ya kame kamar yanda
yake al'adar yan sanda, sanan ya soma magana
cikin natsuwa ranka ya dade an ce kana nema
na.Commissioner ya dube shi cikin natsuwa
sanan ya ce da ma na kira ka ne a kan maganar
barawon shanu din nan da aka ce kaki yarda a
bada belinshi.Aliyu ya sunkuyar da kai don
girmamawa, yace ranka ya dade haka ne, naki
bada belinshine saboda bincike ya nuna shi din
ba karamin mai laifi bane.Daji suke shiga da
motoci suna kora shanayen fulani suna kwashewa

su kai kudu su saida, wanan kamawar ita ce ta
goma sha uku amma ba a taba mikashi kotu ba,
azzalumine na gaske,Commisioner yayi dan
murmushi sannan yazo ya dafa kafadar Aliyu ya
bubbuga alamun jinjina, san nan ya ce, Dan
Sanda mai kishi, lallai kasan aikin ka da ka tsaya
binciko wannan files din, ka tattarosu ka miko
min nan, ni nasan yanda zan kawo karshen
lamarinsa.Zan shigo gurinku anjima kaje.Aliyu ya
sara masa, sanan ya fito.Gaskiya in son samu ne
case din nan ya tsaya a hannunsa dan kam zaiyi
gogaiya da zalunci.Shigarshi office din sa kenan
sako ya shigo wayarsa, sai da ya zauna sanan ya
duba.Murmushi yayi bayan ya karanta, a fili
kumaya ce, ko me nene anko?(hahaha,kunjifa
dan rainin hankali inji,shin kuna ganin zai yuwu
ace baisan Ankoba,ai dai kayan yansanama
Ankone,kuma kala biyu, wasu su sa baki
kawai,wasu kuma baki da light blue ko? Cewar
ANaM Dorayi)
Ya kira layin Usman bayan sun gaisa ya tambaye
shi ko menene Anko? Usman yayi murmushi wato
kai dai in kaje ka shige caji ofis dinku shi ke nan
baka tuna meye a cikin garin.Aliyu ya ce, aboki
mu kuwa dake wanan ofishin mu muke da
labarin abunda ke cikin garin, amma ba wanda
ya shafi biki ba.Usman ya ce zaka bata kudi ne
kurum ta shiga kasuwa da kawayenta su zabo,
haka su ke yi.Aliyu ya ce, gashi ni kuma bana son
yawo bare kuma xuwa kasuwa, in dai zani ne in
zan je gidan zan tsaya nan wani super market in
sayan masu, guda nawa ake siya?Usman ya ce,
da ka basu kudin.Aliyu ya ce, ba zata kasuwa ba,
wanan shine ra'ayi na, zan siyo musu zani.Usman
ya ce shi kenan, sai ka suyo musu mai kyau.Aliyu
ya ce ina ruwa na da zabe, ni dai kawai in dau
zani.Don haushi Usman ko sallama babu ya
kashe wayar.Aliyu ko da wuri ya bar office din ya
bi ta kasuwa ya sai zaunnuwa kala uku ko
wanneguda bibbiyu ya nufi gida.Iya tana zaune
tana yankan kubewa ni kuma ina daga kicin ina
kwashe tuwo ina mulmulawa a leda ina sakawa a
kula ya Aliyu ya shigo da sallama.

Kusan kwana hudu ban sashi a ido na ba , da ya
zauna yana gaisheta.Ta amsa ya ce, ga zaunnuwa
anko ne suka ce ko menene ma?Ta dauki ledar
tana cirowa ta re da fadin kaine ka siyo ankon
gadanda da kanka?Ya ce, to duk ba zani bane,
shi nan sai su zaba.Ina kallo daga ciki kuma ina
jin su, tun kafin in fito zaunuwan suka tafi
dani.Ya ce, naki ne da nata.Iya ta ce, to mun
gode, da ma ina so inyi maka zancen gidan ne, a
ina kasamu?Ya ce, to ni dai nafi so a can kasan
layinku, gefen makabarta din nan, to ba a samu
ba sai na dawo neman na siyarwa, kudina
dakekasa yanxu za su iya semin gida, amma
albashin wanan watan da na wancan watan hada
mana za ayi.To ganin kurewar lokacin sai kurum
na barshi yanxun anjima zamuje mu ga wani gida
da yaya Sani da Usman wai ciki da falo sai kichin
da ban daki dubu dari da hamsin.Iya tayi shiru
tana nazari, can ta ce ina nufin kasan gidan su
babba ne?Ya ce ciki uku ne da kicin da ban daki
sanan ga filin da mutum zai iya fakin din mota
har biyu.Iya ta ce kuma nawa?Da sauri ya ce wai
miliyan daya da dari takwas.Ta ce, ina ganin zaifi
ka siya gidan in yaso sai a daga bikin.Ya dubi iya,
ai saboda bana son dagawar shiyasa na hakura
da siyan gidan.Iya ta ce siyan xai fi maka sauki
ka huta da biyan haya, auran kurum za a daga
ba.Ya ce ba dagawa za'ayi ba, abinda ya sa in an
daga za ayi asara da yawa.Abokaina sun kashe
kudi gurin kati mai tsada tare da wasu abubuwan
abokan aikina suma sun kashe kudi gurin shirya
bukin.Iya ta ce to, kana ji ko, yanda za ayi kawai
a daura auren da buki, sai ta zauna gida kafin a
gama gyara tunda dai nan a gida ne ba a dawa
ba, bana so ka rasa gidan nan ne muhalli a bariki
ba karamin rufin asari bane
Aliyu ya ce, shi ke nan sai ayi haka din bari zan
kira yaya Sani sai muje dake ki ga gidan sai a
biya.Lumshe ido nayi cikin jin dadin an fasa daga
bikin, kai naso in tare a gida na ranar amma baji,
buri na dai a daura auren, amma da iya ta so
kwafsawa wai a daga.Ya mike ya juya da nufin
fita ida nunsa sukasauka a kichin a inda nake, da

sauri na ce ina yini?Sai da ya dauke kai sanan ya
ce, lafiya.Har ya fita ina kallonshi.Iya ta katse ni
da cewa, wata rana sai kin gaji da kallon shi.Na
sunkuyar da kai kunya ta rufe ni, ban santana
kallona ba sa karya, in dai gadanga ne gaki ga shi
nan.
Pink din muka zaba ni da Aisha, sai dai muna
zuwa kasuwa aka ce dubu uku ce gashi kudin
aisha bai kai ba.Sai muka dawo gida da kyar
mamanta ta cika mata muka koma muka
siyo.Muka roki mai shagon ya ajiye mana da mu
siya da yawa.Yamma tai mana a kasuwa gashi
ana wahalar mota.Muna tsaye a kan titin kano
Road, na ce bana son magariba tayi mana tun
daya muka fito gashi iya ba ta san mun koma
unguwar mu'azu mun dawo kasuwa ba.Aisha ta
ce, sai dai muje mushiga dambancen ko za mu
samu, na ce zamuje.Ta kan legas street wani
lokacin ba a wahalar mota.Muna tafe wai wani
mai mota ya tsaya, 'yan mata kuzo mana.Na ja
tsaki tare da kara sauri, Aisha ta ce, lafiya?Ya ce
rage muku hanya zanyi.Na ce Aisha, kema kika
tsaya tambayarshi.Haka mutumin nan ya ci gaba
da bin mu yana magiya, duhun magariba ya
shigo na ce Aisha ko dai mu tsayar da mutumin
nan ya kai mu gida?Don ina tsoron fadan iya.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tace, nima hakan zan ce,dai dai lokacin ya sake
cewa ku kuwa tunda na ce Allah ya kamata ku
saurare ni, dan kun san mugu dai ba zai yi muku
sallama ba.Aisha ta ce unguwar Mu'axu muke.Ya
ce, ai hanya ta ce ni kuma Nasarawa zanje.Cikin
far gaba muka shiga motar ya ce mun a'a ke
dawo gaba dai ki nuna mun hanya , na koma ga
ba.Ya tam bayi sunayen mu, ina shirin xollo masa
karya sai naji Aisha daga bayana ta ce, ita Sadiya
ni kuma Aisha .Ya ce, masha Allah , sunaye masu
ma'ana.Ya dube ni, Sadiya dan ke fa nake ta

wanan bibikon sai aka ci sa'a kina da sunan
matata, ni sunana Auwal.Hakika jin sunanki ya
kara samun sonki Halimatu duk wace ta amsa
wanan sunan takan zama mai hakuri da hange,
bata rani bata daukar raini, macen rufin asiri zan
so na sake samun ki.Na ce matar taka ta hada
duk wanan halin shine zaka yi mata kishiya?Ya ce
jin dadin halinta yasa zan kara.Aisha ta ce bakai
mata adalci ba, au, ke fa sunan uwata ne ke da
zaki tayani yakin neman shiga?Aisha ta ce, nan da
sati biyu ita ma tana dakin angonta.Da sauri ya
ce, da gaske?Ta rantse mashi tare da fada mashi
ashobe muka zo siya.Daga nan nayi shiru bai
sake magana ba harya shigar damu layin kasuwa,
na ce sauke mu a nan ma mun gode.Sai mu
karasa.Ya tsaya muka fito, ya ce marya ba
godiya?Na dawo dai dai saitin shi na ce, mun
gode, na ce kayi hakuri muna sauri ne dare
yayi.Ya ce shi kenan, Allah ya baki zaman
lafiya.Juyawar da zanyi in tafi tare da cewa amin,
sai maganar ta tsaya, sa kamakon ya Aliyu da
nagani tsaye yana kallon mu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347




Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100



Darajar Yayana 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 10:51 PM, 14-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
__________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Duk da kasan cewar duhun magariba ba zai sa in

kasa gane bacin ran sa ba.Gaba na ya fadi, irin
wanda ban taba yi ba.A fili na furta na shiga
uku!Aisha ta ce, me nene?Bakinta yayi shiru
sakamakon ganindatayiwa abin da nagani.Kusan
minti biyu yana kallo na, ko da banga fuskarshi
sosai ba na san a daure take .Sai yaja tsaki sanan
yayi babban titi abin shi.Muka kwashi sauri ni da
Aisha inayi ina waiwaya shi, a zuciyata ina cewa
yau na kade, Aisha ta ce muyi wa ni kin ga da
sauki tunda mama ta san mun xo mun koma
ne.Munyi sallama iya tana tsaye tsakar gida tana
cewa, kai ni wadan nan yara ko ina suka shige
ne?Kai Sadiya bata da hankali, ki fita tunda
hantsi har magariba, to ko kasuwar kwari ta kano
suka je?Ko jiran mu gama sallamar bata yi ba
bare ta amsa ta hau fada, Aisha ta shiga jero
mata dalilan mu, ta ce ku refa mun baki, ko
kasuwar kano kuka je ya ci a ce kun dawo tadubi
Aisha ta ce uwaki ta ganki hankalinta ya kwanta,
masu shegen rawar kai.Ta bini ke kuma, sai ki
jira xuwan gadanga don tun yamma yake shige
da fice bai ganki ba, har dai ya kare ya ce ita
wanan yarinyar ina tayi ne?Ina son ta hada mun
abin shan ruwa ina azumi, na dafa kirji na ce, to
me kika ce masa?Ta harare ni karya zan masa?Ce
masa nayi kinje kasuwa sayan anko, yayita fada
me yasa na barki don baya son xuwanki kasuwar
ne yasa shi siyo ankon dakansa.Na ce, na
kade.Na dauki buta dan yin auwala, a xuciyata
inatuno yanda ya ganmu muna fitowa a motar,
da nayi salla nayi addu'a Allah ya yayyafawa abin
ruwan sanyi.Da a zamar sa ya shigo da sallama
ga ba naya fadi da sauri, don haka ma ban iya
amsa sallamar ba, dakinsa ya shiga bayan wasu
mintina ya fito tsaf tsaf cikin shirin fita.Ban taba
ganin dansanda da kaki yake masa kyau matuka
ba irin ya Aliyu, kan cinya ta na dora fiskata
ganin ya nufo dakin Iya.Ga zato na da ya karaso
zai zabga min mari,ina jiyoshi yana cewa iya ya
tafi sai da safe, ta ce, can zaka kwana?Ya ce eh,
ta ce, Allah ya tsare mun kai, ya kuma bada sa'a
ka yawaita adu'a.Ya ce to ina yi iya, zan kara
kulawa.Ya sake wuce ni ya nufi fita, da kallo na

bishia raina na ce, zaki na maza sarkin jin
kai.Nan ya tafi ya barni da kamshin sa sai dai da
dukkan alamu yana fushi dani.Da dare ina cikin
daki kwance kan gado, juyi kawai nake zuciyata
tana mun nazari a kan kallon da ya Aliyu zai
mun, ganin da yayi mun a motar wani kamar in
kira shi in bashi hakuri, sai na fasa.Na rubuta
sako kamar haka:YA ALI DON ALLAH KAYI
HAKURI IN NA BATA MAKA RAI.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ban jira amsa ba don nasan ba samu zanyi ba,
amma ga mamaki na sai naji sautin shigar
sako.Da sauri na bude na soma karantawa.KUL!
BANA DAYA DAGA CIKIN MUTANEN DA SUKE
DAUKAR LOKACIN AIKINSU, SUNA HADA SU CIKIN
LAMURANSU NA DABAM.SAI KI RIKE WANAN DAN
GABA.Na lumshe ido ina son yin nazari a kan
kalaman nasa, na san dai kul! Dan gargadi ne ya
yi mun kenan ba ya bukatar a shigar masa
lokacin aikin sa.Nayi juyi ina mai yiwa kaina jajen
auran ya Aliyu, yanxu auren ya fi ban tsoro fiye
da birgeni.Washegari sukuku na tashi,Iya ta ce
jiya kuna can kuna gararin yawon ku mahaifinki
ya zo yayi ta jiranki har ya tafi.,na ce kash!Ko da
yake na san dole ya dawo kafin bikin.Ta ce ba
dole ne ba , kudi ne ya kawo sadakin ki da akayi,
sai gudumawar su dubu hamsin.Na ce hamsin
iya?Yaushe hamsin zatayi mun kayan daki?Ta ce,
ina laifi, mahaifinki fa yanxu ba aiki yake yi ba,
tunda yayi ritaya sai dai dan noma.Shi ko noma a
kasarnan yanxu dai ba a dauki maiyinsa da
mutunci ba, shine koma baya a gurin gwamna
ti.Su ba ga taki ba ba ga tallafi ba, dan
gurarenda suke nomawan ma kwanaki
yakecemun gwamnati ta ce zata amshi wurin.Na
ce iya gurin da ma ba nasu bane?Ta ce, Sadiya
kenan, dama talaka yana da guri ne a a wanan
karnin?Sai wanda Allah ya taimaka ya kuma tsaga

da rabonsa.Gurinka da takardu da komai za a
amshe maka,dubu hamsin ai yayi kokari.Na ce
haka ne Allah ya rufa asiri, duk abindaza ayi dai
dai karfinmu za muyi.Iya ta ce, in sha Allahu sai
kin zaba yata.Jugun nayi ina kallon Iya, baiwar
Allah nan tana sona fiye da yayan da ta haifa,
abin da take min ko ita ce ta haifeni sai
haka.Kusan duk dare sai bacci na ya katse, in yi
kiri kiri ni kadai cikin xullumi irin zaman da zanyi
gidan ya Aliyu.Na gama duk hashashen da zanyi
ban hango jin dadi ko kulawa a cikin auren ba, sai
yanxu na gane nufin iya ta guje mun wahala ne,
gashi lokaci ya kure mun bani da damar in ce
bana so.Kusan karfe uku na rana ina zaune ina
yankan farce na tare da gyarawa, sautin shigowar
sako naji, sharewa nayi amma naki dubawa don
nasn MTN ne.Sai kuma wata zuciyar ta ce mun in
duba, gaba na ya fadi ganin sunan ya Ali, na
duba cewa yayi.KI SAMENI A DAKI NA
YANXUN.Duk da cewa ina fargaba sai da na dan
sakemurza hoda tare da man lebe, sanan na
fesaturare.Iya ta kalle ni tana zaune gefe tana
gyaran goron ta da yayi tsutsa
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login