Showing 39001 words to 42000 words out of 44623 words
Murmushi husnah tayi ta ajiye basket din ta ajiye kan dining kafin ta koma kan bed koma bacci
Sai karfe goma dai dai ta tashi
Ta gyara bedroom dinta da falonta ta badeshi da kamshi
Ko ina yadau kamshi kafin tashiga bathroom tayi wanka tafito ta shirya cikin wani tsadaddar
super Holland dark blue sai adon pink ajikinsa
Yadda dinkin yazauna ajikinta shizaifi Baku sha'awa sosai das yamata dinkin ma kawai a in
kallone
Matsalarta daya bata son dankwali ta tace gashinta takama da ribbon pink
Kafin ta murza daurin Dan kwalinta abin wuyanta ma pink ne
Gaskiya husnah tayi kyau matuka
Tadauki ta kalminta plate shoe tasaka
Har ta zauna zatafara break fast saikuma taga rashin dacewar hakan
Bata je tagaida mummy ba
Gyalenta tadauka maishegen kyau tayafa
Pink colour
Tafita tayi hanyar kofarta tasaka key ta kulle
Bayan ta fita
Dama dole saitabi ta main falonsu gabadaya tana fitowa kuwa taga mutan gidan gaba dayansu
a falo
To itabasaninsu tayi ba
Ganin harda manya yasa husnah ta durkusa tana gaida su hajiya rukayya da kuma Laila
Laila ta watsa mata harara
Wai ita hakimar bata fitowa ne saike
Hajiya rukayya tace inazata fito ansamu duniya
An auri mekudi an asirceshi
Suby ta kalli husnah tace 'yar buzuwa kotafiya za ayi ne
Husnah ta kalleta tace inje ina ai munsamu gida nida antyna
Dan nadawo kenan gwamma muma muzauna muci arzikin Dan da alama bamu kadai bane 'yan
cin arzikin
Husnah tana gama yada musu magana tayi waje abinta
Har suby zata bita hajiya rukayya tace a a kyaleta kar ajimu tun yanzu mana
Laila race lalle ma Dan talaka be iya samun wuriba
Wannan zakewa haka harda dauko 'yar riko
To wallahi wannan yarinyar kamar aljana bazata tazauna min agida wallahi
Kalli yadda take tafiya kamar wata 'yar sarki
Hajiya rukayya tace aibakisan halin talakabakenan idan yasami guri
Kuma ke Laila da kike cewa bazata zauna ba yayar tata ma ba zaman zatayi balle ita 'yar cin
arziki
Nan dai suka muna funcinsu
Husnah tayi sallma a falon mumy shiru ba kowa
Ta nemi guri tazauna a tafkeken falon su mummy
Mummy ta sauko daga sama bata lura ba harzata shige kitchen
Husnah tayi saurin sauka kasa tace mummy ina kwana
Mummy hafsat tajuyo tayi tazali da surukar tata
Tace a a husnah ai ban lura bama meyasa kika zauna nan baki haura saman ba saikace
bakuwa
Husnah tace bakomai mummy nan ma yayi
Mummy hafsat tace a a nan gidanku ne ko ina zakishiga
Kina da damar hakan kinjiko
Ya bakunta husnah tayi murmushi kawai batace komai ba
Mummy tace kinci abinci ko husnah tace yanzu zanje nayi
Kafin mummy tayi magana Abdul Hakeem yayi sallama yashigo wata tsadaddiyar shadda milk
colour sai wata hadaddiyar hula da ya murza akansa Wanda yasake fito da kyakkawar
fuskarshi mai kewaye da kwantacen saje dayakarawa fuskar tashi kyau
Gaskiya PROF Fa kyakkawar mutumne bankarya
Yashigo idonsa yakai kan Husnah dake zaune kan kafet
Wani farinciki yaji sosai
Ya kalli mummy
Yace mummy na antashi lafiya
Mummy tace lafiya kalau son maza kuwuce dining kawai kuyi break idan kungama kukirani
zanje nayi salar walha
Hakeem yace angama dalibata
Mummynsa tayi murmushi tace a a tun yaushe daliba ta canja malami ai
Hakeem yace amma tunda yanzu nadawo gida
Sai kisake sayan form agurina Husna da mummy sukayi murmushi
Mummy tace kaga idan nabiye maka sai lokaci ya wuce banyi sallar ba
Ta kalli husnah tace 'yata tashi kije dining kinji kikarya abinki kinji
Ina zuwa yanzu
Mummy tayi sama tabarsu anan
Hakeem yakure wa husnah ido yace wana kama
Husnah ta saukar dakai kasa
Hakeem shima zamayayi shima tabayanta yakamota yasakalo Kansa tagefen wuyarta
hanunshi yakai cikin rigarta ta yashafo cikinta
Yace bakice abinciba baby jicikinki fa kaman zai hade da baya
Itadai husnah wani iri takeji tabatan dayakeyi
Yace tashi muje nabaki abinci banason musu
Cikin shagwaba husnah tace ni anan zanci ba a dining ba
Prof yace angama baby dakanshi yatashi yakawo musu komai plate daya yazuba musu
Yace oya bude bakin bayan yadauko kofin kunun gyada tace dakaina zan sha kabari kawai
Yace bason musu fa
Badan tasoba tabude baki yabata
Nan yabata farfesun ma kosai da duk wani abin dake gun saida yashiga cikin husnah tace
mishi ta koshi yaki
Yace daman ya shamsu yamishi bayanin bata cin abinci
Cikin shagwaba husnah tace wallahi inaci kuma nakoshi sai da yaga tana shirin dawo Dana
cikin nata yabarta haka kafin shima yafara cin abincin
Bayan yagama ne yasa hanu zai dauke tiren abincin husnah targashi yace yadai yakureta da
ido
Tace kabarshi kawai zankai
Bai hanataba husnah tadauka tayi hanyar datake tunanin nan ne kitchen din
Tana zuwa ta ajiye a sink din wanke wanke ta wanke tas duk wani abin da za a wanke saida ta
wanke
Shikuma prof be biyo sa wuba saboda yana waya ne
Mummy tasauko daga sama tagashi shikadai ne a falon
Tace a a asmaun
Hakeem yayi sallama dawani abokinshi yace tashiga kitchen
Kai kwanuka
Mummy taleka kitchen dintaga ko ina tsaf an goge
Mummy tace kai haba husnah da kanki Aida kinbarima yanzu mai wankewar zatazo yau tayi
ranar dawowa ma
Husnah tace bakomai mummy
Mummy tace maza jeki huta kafin nafito
Husnah tayi murmushi tace
a a mummy meza adaura Dan naga kaman abinci kikeson daurawa
Mummy tace a haba dai daga zuwa harkifara shiga kitchen a a jeki huta
Idan kunyi sati saikifara dafa abincinki
Husnah tace mummy kigafarceni amma banzan taba zama inga kina shiga kitchen
Yakamata kema kihuta Dan Allah
Tunda na taso agidan mu Nina ke abinci umma ta na hutar da ita saboda haka Dan Allah
mummy kibari na ringa miki abinci kihuta kema kisan kinada yarinya a yanzu
Cike da mamakin kalaman husnah mummy tace lalle husnah kin haifu Allah ya wa iyayenki
albarka dasuka miki tarbiya maikyau
Nagode da kika daukeni matsayin uwa
Allah yabaku zaman lafiya keda mijinki yazaunar daku lafiya kinjiko
Husnah kai akasa tayi shiru
Mummy tace na'amince zaki rinkawa mummy abinci amma fa mummy ma tayi alkawarin satayi
sati kina cin abincin mummy kinjiko
Saboda haka kibar mummy tacika alkawarin ta
Husnah tayi murmushi kawai kafin tayi magana
Hakeem yayi gyaran murya mummy da husnah suka kalleshi
Mummy tace wato labe kake mana ko
Hakeem yayi murmushi yakaraso cikin kitchen din
Yakama hanun mummy yace haba mummy please kibar yarinki tasamu ladarki
Allah ne ya amsa adduarki yakawo mana husnah cikin rayuwar mu
Kinji mummyna
Mummy hafsat tayi murmushi tace shikenan tunda kunmin yawa Allah yayi albarka
amma bayanzu za adaura abinciba sai yamma idan anyi la'asar
Yanzu muje kawai muyi hirar mu
Mummy taja hanun husnah wacce tunda Hakeem yashigo takasa magana
Ranar dai a sashin mummy husnah ta wuni sai da ka kira isha tabar dakin mummy ganin
Hakeem da daddy sunfita sallah
Mummy tace yau husnah Allah yatashemu ki huta gajiya ko
Ita mummy a tunaninta husnah zata je tashirya ne kafin mijinta yasameta
Husnah kuwa tashiga falon taga Laila da suby a zaune
Ta wuce abinta batareda ta kalli kowa ba
aikuwa suby tace ke zonan
Kojuyowa husnah batayi bare ma tasan da ita sukeyi
Ke 'yar talakwa bakiji menace bane husnah tayi banza dasu kafin suby ta karaso husnah
tashige ta banko kofarta tasaka key
Direct wanka tafara kafin tayi sallah tayi karatun ta data saba
Suby tace anty anya kuwa ba wannan aljanar yarinyar bane kishiyarki kuwa
aikuwa jitayi Laila ta zabga mata mari
Suby tace mena miki anty Laila
Cikin tashin hankali Laila tace damme zaki min wannan mugun fatan
Taya za ayi yaje ya auro 'yar cikinsa
Bama hakaba idan yakasance wannan yarinyar ce ai yayi abinkuya
Nikuma nashiga uku taya zafara kishi da wannan yarinyar
Suby tace aiko dai koki kokiso itace
Dan agabanki tasa mukulli ta bude sashinta kuma dazu Dana kai mata abincin ma ita nagani
kawai raina mana hankali take
Laila ta daura hanu akai tace nashiga uku ni Laila wannan ai inaganin ko meenat ma ai tagir
meta
Lalle Hakeem yacuceni
Yanzu sakayya da zaimin kenan ya auro 'yar cikina inyi kishi da aita ina Sam bazaiyuba wallahi
Suby tace wallahi idan kika bari aljanar yarinyar tazauna agidan nan
Zikidawo jaka wallahi Dan abinda kike samu bazaki samu ba
Yarinya kaman ita tayi kanta Dan kyau tahada komai da d'anamiji yake bukata
Laila tace ya isa haka suby zakisa zuciyata tafashe kibarni naji da Abu daya Dan Allah
Hakeem yashigo falon da sallama Laila ta taso sannu da zuwa baban meenat
Hakeem yace yauwa yashige bedroom dinshi Dan karya taba kofar husnah yaji akulle agabasu
su fahimci wani Abu
Laila tabishi har yafito Daga wanka yana yashirya ya kwanta
Laila taga bashida niyar kulata yasata ce baban meenat har yanzu fa bansan kanwartawaba
Sai kanwarta muke ta gani tana shige da fice
Hakeem yayi murmushi Dan ta tabo inda yake mishi kaikayi
Yace kanwa kuma ai bata da kanwa itadai wacce kikagani din itace amaryata
aikuwa Laila ta tashi tace amma wallahi kaji kunya Hakeem yanzu da girman ka da darajarka
zaka auro 'yar cikinka wannan ma ai zubda mutuncin Kaine da zubar wa 'yarka da mutunci
Prof baki kawai yasake kallon ta
Yayi murmushi yace kinyi sake maman meenat da kika auri mijin asmau saboda yanzu nasan
nima namijine kuma na auri dai dai Dani kije aduba miki nidake bamu taba dacewa ba kuma
bazamu daceba
Meenat da Allah yabani na karba kuma inason 'yata
Idan tazo ruwantane taso matata ruwantane takita
amma zanfada miki wannan Kalmar mummy da daddyne kawai bazan iya rabuwa dasu ba
saboda husnah
Amma bayansu zan sabama kowa akan matata so get out of my room
Cikin tashin hankali Laila tafito Daga bedroom din Hakeem
Kuka sosai taci suby nabata hankuri
****
Bayan sati uku Hakeem ya Dade da komawa aikinsa gashi aikin yamishi yawa ga kullum
tunanin husnah ne da sha'warta acikin ranshi
Ba inda yake samun ganinta sai a part din umma Dan Anna take wuninta
Tana fita sallar isha zata gudu
Hakeem zaune kan kujerar office dinsa Ahmad kuma yana cike wani file's
Ahmad yace yauwa kagani ko yana nuna wa Hakeem abinda yacike
amma hankalinsa baya taredashi
Ahmad yace wai meke faruwane Prof
Hakeem yayi murmushi wallahi baby ce take bani ciwonkai
Taki bari na rabeta Sam wallahi
Bana ganinta idan ba a gurin mummy ba
Ahmad yace zanbaka shawara idankabi yau din nan kadaina damuwa
Hakeem yabada hankalinsa sosai
Ahmad yace bakace agurin mummy take wuniba prof yace a
Ahmad yace sallar ishar dazakaje yau kabari kawai kamuku jam'i
Kana shiga kacewa mummya da daddy da ciwon kai kadawo
Idan kaga zata tashi saikace jirani mutafi tare agaban mummy nasan bazatayi musu ba
Hakeem yace kuma wallahi sai dai kuma yau laila ce da kwana
Ahmad yace saikayi hakuri yau da gobe ai duk dayane yayi dariya
Hakeem yace a a baduk dayabane wallahi kai bakasan halin danake cikibane shiyasa
Ahmad yace kai haba mai mata biyu fa amma kana fadin haka ai saika kabani tsoro nakasa
kara tabiyu
Hakeem ya harareshi
Husnah falonta suna waya da ummanta da ya shamsu da anty kubra
Bayan sunagama wayarne ta dauko mayafinta zata koma banngaren mummy
Sai taji Laila tana waya amma bata San dawa take ba
Laila tace dadin abinma fa yarinyar baso shi take kullum a dakinta take kwana
amma wannan aikin bokane yace bazai taba bari harya kusanceta ba
Yanzu fa kusan sati uku kenan amma suna wasan buya bata ma bari yaganta
Shikuma na mamajo kina gani shi kisan yana cikin damuwa
Can ta matse mishi kinga haka malam zaicire mishi sonta aranshi kwatata
Dan nima yace karnabari ya kusanceni har sai yarinyar tabar gidan
Kinga kuwa ai yana cikin matsala dannima bana zuwa bedroom dinsa harsai ranar da wannan
aljanar yarinyar tabar gidan
Nan dai sukayi sallama da kawartata
Ta kalli suby tace insha Allah saura kiris yarinyar nan tabar gidan nan
Daga nan kuma sai mufara shirin yadda zamuyi mukasheshi idanba haka ba wallahi wata
zaisake hangowa
Suby tace wallahi da dai yafikam
Dan wallahi nima inason naga munfara fantamawa fa anty
Laila tace kidai yishirunki kawai saura kiris
Husnah toshe baki tayi sai kuma wani jiri data ji yana dibanta dakyar tasamu takai kanta kan
kujerarta
Tace innalillahi qainnairraihirraju'un nashiga uku meya musu suke son kasheshi
Gaskiya bazantabari kuyi nasara da yardar Allah
Kuma mijina zaisamu abinda yakeso insha Allah
Allah yakaimu gobe nashiga ukuna ni husnah wani irin zunubi na daukarwa kaina
Tabbas yaya Hakeem bai can canci wannan sakaiyar daga garaniba kayafemin Dan Allah duk
da banasonka nayi alkawarin faranta maka kamar yadda kake faranta mana nida iyayena
Duk wannan maganar da husnah take yi tanayinsane itakadai
Hmmmmmmmm
Next page
Your comment is needed fan's. Love u all
Duk wacce bantaba bata page ba
Tayi comments mezafi next page natane 踫踫
踫踫踫踫踫踫
[05/05, 8:53 PM] UMMU AFAN 潤撕: 潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤潤
潤潤潤潤潤
潤潤潤潤
潤潤潤
潤潤
潤
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
踫踫踫踫踫踫踫
潤撕FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION潤撕
潤撕潤撕 (F.C.T.W.A)潤撕潤撕
潤撕HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION潤撕
潤I DEDICATE THIS PAGE TO YOU BINTA ADAM (MAMAN IMAM) 潤COMMENTS DINKI
YANA SANI SANI CEWA NIMA WATACE SO PLS KEEP IT UP
INA ALFAHARI DAKE 踫踫踫
潤AKWAI LOKACI潤
潤PAGE 96 to 100潤
YAU take asabar daurin auren prof da husna
Wanda za adaura karfe uku na rana saboda bakin da zasuzo daga kasashen waje saudiya da
sauransu
Duk Wanda baisamu yakaraso tun juma'a ba saboda wani uzirin
Shine aka daga daurin auren
Kuma a yaune ake kai za akai lefe gidansu husna anasu aladarkenan
Mummy hafsat ce zaune cikin kawayenta matan mayan mutane
Da kuma 'yan uwa da abokan arziki
Kowa taganta yasan tana cikin farin ciki Mara misaltuwa
Ana ta kallon lefen Hakeem Wanda za akaima husnah anata yabawa
Mummyn Ahmad tace kafin atafi kai lefen yakamata akira uwargida tazo taga kaya ko
Mummy hafsat tace to akirasu mana
Dai dai lokacin Aisha matar Ahmad tashigo da daukar wayarta data saka caji Dan tunda aka
fara hidam bikin nan agidan mummy take kwana
Mummy hafsat tace yauwa 'yar albarka mazaje kicewa su Laila suzo zuga kaya
Aisha tace to mummy tayi part din Hakeem tashiga part din Laila
anan ta tarar da suby kanwar Laila da hajiya rukayya da hajiya suwaiba da ita Lailar kanta
Sai kuma kawayenta
Aisha ta gaishesu bawanda ya kalleta suby kanwar Laila ce tace dalla malama meyakawoki
nan
Aisha tace to bani nakar zomom ba nima rataya akabani
Hajiya rukayya zatayi magana Laila tace yishiru kawai hajiya bake yakamata kimayar mataba
Suby tace kema anty bake yakamata kibata amsa ba nice dai dai da zamaninta
Aisha dadina da jaki duk yadda akayi da shi saiyaci kara
To nima bazuwan kaina nayiba mummy ce tace kuje kukaga kaya Dan za a wuce da shi
Tajuya tayi waje abinta
aikuwa Laila ta mulmulo zagi tabita da shi
Hajiya rukayya ta yi saurin rufe bakin Laila