Showing 15001 words to 18000 words out of 29006 words

Chapter 6 - Tawa Ta Sameni Complete Book 1 By Halima Mashi

Haj Shuwa da yanuwa Haj
Yaya,sai yan uwan Alh Mukhtar wato yan maska Aunty

Mimi ma a ranar tazo don ranar ne za'ayi
dayis,yayanmu ranar bai wuni gida ba sai yamma dama
ni banje masu wurin da suke yin lalle ba nida Amira
mukaje mukayi kitso sannan mukayo namu lallen a can
don dama mu ba ma saka mai a kanmu. Misalin karfe
biyar na yamma yayanmu ya aiko Kamal ya kira ni nazo
yace na kawo masa wani abu tabawa in akwai dan
yinwa yakeji na koma ba wani abin kirki sai na rana
kuma ya huce nasan ba zai ci ba,don haka sai na dafa
mashi indomie da kwai na kawo mishi natarar da Aunty
Mimi a dakin sai naji raina ya baci na ajiye zan juya
yace ke kizo ki zuba mani mana na dawo sai tace ka
barta sai na zuba maka ,bai dubeta ba yace min samin
mana kina kallona baki sanni bane?nayi kasa da kaina
sannan na zuba mishi na dauko mishi coke da ruwa
sannan na juya zan fita sai naji yace shiga bedroom ki
dauko wayarki tana nan a kan katifa,na dauko sannan
nayi mashi godiya,washe gari a command quest za'ayi
kowa ya shirya cikin anko nima na sanya nawa ankon
nayi kyau sosai na fito harabar gidanmu a nan ne ake
daukan yan matan tuni kowa ya tafi sai Amarya da
kawayenta wadannan kuma bana tunkare su ba itako
mami tuni dama tana can don sune masu shirya gurin
dasu bilkisu da sauran kawaye,ina tsaye na jingina da
bangon dakin yayanmu ina kallon kawayen amarya suna
ta kai da kawowa kowacce na rike da waya tamkar
masu gasarta nan na tuno da tawa mama tace na aje
sai mun gama zana jarabawa ina wannan tunanin naga
anty mimi sun fito itada yayanmu itama anko ne a
jikinta irin nawa tayi matukar kyau dama anty mimi ba
dai kyau ba gata fara yanda mami ke gaya mani
mahaifinta balarabe ne zamanin da Haj Laure
mahaifiyarta suke zuwa kano to jidda a can Allah ya
hadata da wani balarabe ta aura shekarunsu ko goma
ne da aure ya rasu lokacin Anty Mimi na shekara
shidda shine ta gudo da ita ba tare da sanin dangin
babanta ba,sannan ta sake aure shine ta haifi yaya uku
sanda naji wannan lbr a raina nace ashe jirgi daya ya
debomu ni da ita.....Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347


DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADDEEN SHOMAR
WHATSAPP 08168575100





Tawa Tasameni 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 02:31 AM, 29-Dec-15
Under: TAWA TASAMENI
__________NA HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
Garama ni ubana yana nan, haka danginshi, nayi nisa
cikin tunani na ji horn ba karewa na juya can wajen da
ake horn din bakin gate sai naga ashe su yayanmu ne
zasu tafi ban fahimci wai ni suke ma horn ba sai da anty
Mimi ta bude gaban mota tace ke na dubeta na dafa
kirjina nace ni?eh da Allah zo nan ana maki horn kinyi
banza da mutane, na nufi gunsu ina zuwa naga yayanmu
ya sako hannu ya bude baya yace shiga,gabana na
faduwa na shiga motar don nasan ba wanda ya taba
shigarta a yan gidanmu sai yaya Kabir na zauna sannan
na rufe sanyi da kamshi sune suka ziyarceni tamkar wata
munafuka haka na zauna a motar kaina a kasa, suko
suna ta labari bana jin dai muryar yayanmu sai ta anty
.Mun yi nisa sannan na dago idona sai kawai muka hada
ido da yayanmu ta madubi nayi sauri na sunkuyar da
kaina kasa har mukaje ban tanka ba,ban kuma daga
idona ba,sai da naji an tsaya sannan na dubi gurin yan
mata ne cike na buda zan fita sai naji yayanmu yace
karba,na juyo sai naga yana bani kudi ne sababbi yan
naira hamsin na amsa nace Allah ya saka da
alkhairi,anty Mimi ta shaka sosai da na kalli fuskarta ni
dai nayi ciki ko zan ga Mami, ana cikin hidima shalele
suka kira don haka gun ya cika da karan kidan police
band Sa'a tazo tace kije ana kira gabana yana faduwa
nace inji wa?ta harareni dole sai kinji? ki zo mana na
bita can baya mukaje ganin Anty Mimi da Amare da
kuma kawayensu yasa wata faduwar gaba ta sameni na

dai daure na isa wurin,Anty Mimi ta kai mani rankwashi
akai tace ina jakarki?nace tana gun Mami tace nawa
yayanmu ya baki?nace ban kirga ba nan ta shiga
zayyane masu wai wannan wace irin yarinyace,Anty
Hadiza tace ai wannan daga ita har uwarta annoba
ce,Anty Mimi ta cigaba da cewa kunga jiya a gabana ya
bata waya irin tawa ce sak koda ganin kwalin sannan yau
zamu taho nan ta zo ta rabe ya dauko mu tare kunji
biyu,cikon na uku kuma sai gashi ya raba mana kudi
kilan ma daidai ya raba tamkar wasu kishiyoy,nan suka
taru a kaina wannan ya kai mani bugu kowa dai na fadin
albarkacin bakinshi, Mami ta iso daidai lokacin da wasu
kawayen Anty Mimi suke cewa asiri tayi mishi daga
gani,in ba haka ba me zaiyi da wannan mummunar
yarinyar gara ma ki dauki mataki tun da wuri akan abin,
Mami tazo tana cewa Anty Mariya kuzo anguna sunzo fa
ana ta nemanku,kan suyi magana Anty Mimi tace Mami
muga jakar wannan jakar,sai sannan Mami ta ganni ina
kuka tace Iman menene?Bilki tace ba'a sani ba ke dai ki
bada jaka a kace Mami tace bazan bayar ba nace Mami
bata ta mika mata sai da suka kirga kudi daidai da nata
dubu ashirin da biyu ne dama ban kirga ba,saura sukace
kar ki bata ko sisi Mami tace wllh sai naga ya wa
yayanmu in har kika dauki kudin nan,Anty Mimi ta watso
kudin da jakar a jikina sannan tace ki jira abinda zai biyo
baya ta wuce sauran suka bi bayanta aka bar daga ni sai
Mami inata kuka,Mami ta kwashe tana tambayata abinda
ke faruwa na zayyane mata komai itama na kula ta dan
yi mamakin kudin da ya bani tace Iman yayanmu yana ji
dake fa nace Nami ku kula da wani abu daya yayanmu
nice nake mashi aiki,shiyasa yake mani alheri amma wai
suna zargin wai yana sona ne ni nasan ko mata sun kare
yayanmu ba zai taba cewa yan sona ba ke kinsani balle
yana da kamar Anty Mimi,Mami tace ai itama anty Mimin
ba wani kyau ne da ita ba uban gashi ne kamar jirgi ya
daso tasha kuma a tsaye take ba wani diri kirji kamar na
bera ba wasu nonuwan kirki nace to shi dai tayi mashi
Mami tace ke zo muje ba wani yi mashin da tayi kawai
saboda mamansu zai aure ta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
TAWA TA SAMENI,haka na fada ranar daurin auren anty
mariya ba wani abu yasa na fada ba sai ganin munsa
less iri daya da Anty Mimi wato wanda yayanmu ya bani
nasa daya daga ciki me ruwan lemun tsami takalmi da
jaka iri daya itama ni take kallo ta zauna kofar dakin
yayanmu a fararen kujerunshi ranta yayi matuka gun baci
naga ta yi cikin gida ni kuma sai na nufi gidan su
Amira,dama dazun ta aiko Faruq wai ta dawo dama jiya
ne ta tafi unguwar dosa gun kanwar mamansu da suka
dawo kwanan nan shine taje kwana,ta fito wanka na
sameta nan nake zayyane mata abin dake faruwa ta
dinga mamakin karfin halin irin na nasu Aunty Mimi dan
yayanmu ya min kyauta ta kara da cewa komai ya sai
maki ba zai biyaki ba irin dawainiyar da kike mishi ba
nace suna zargin fa wai sona yake yi,Amira tace haba
dai nasan ma ba zai fara ba domin kin......na katse
Amira nace ni ba ajinshi bane nasan da haka kuma ko
mata sun kare ba zai so ni ba Amira tace ba nufi na
kenan ba ina nufin matsalar dake tsakanin mahaifiyarki
da tasa ai yasan da wannan matsalar ba zaima ce yana
sonki ba.Nace ato su sai hauka suke yanzun nan na
hadu da anty Mimin shine ta ganni da kayan nan har
jakar to tayi cikin gida ban san me zai faru ba,dama
bikin nan sai yan tsegungumi sukeyi dangin Haj Yaya
naci gaba da cewa kinsan abin da ya faru ne da babansu
Mami ya tambayi Haj Yaya game da kayan da za'a siya
don yayanmu ya riga ya sai masu sai yace to suyi mashi
list din kudin sukayi mashi hauka to hauka mana wai fa
miliyan daya da rabi suka rubuta shiko ya kira mama tayi
mashi lissafin kayan dakin mata mata har da na jere da
na kicin duk ta sanar dashi naji ya bata kudi sukaje ita
da Anty Yagana suka sawo mashi komi don Mama cewa
tayi sai da tayi ciko suka kawo ya dinga sa mata albarka
itama ta bashi nata gudummuwar na zannuwan gado to
wannan abin shi yayi matukar tada hankalinsu Haj Yaya
da har sunce sam kayan nan bai masu ba shine baban
yace yayi in baiyi masu ba to su sai nasu da kudinsu
kafin Amira tayi magana sai ga Jamila kanwata da
kukanta wai ana fada da Mama nace mama da wa tace
Mama da mutane yan biki nace yau mun shiga uku ko
takalma bansa ba na nufi gida Amira ta biyoni,tun a

harabar gidan nake jin hayaniya yaya Kabir na gani ya
fito daga cikin gidan ranshi a bace da ganina ya nufoni
yace kar ki shiga zo nan,na soma kuka ina cewa ni dai
na shiga uku ya ja min hannu zo muje karki shiga,nace
ina kuka yaya Kabir barni naje naga Mama yace
Mamanki tana dakin Alhajinmu zo muje ya jani dakinshi
ya zaunar dani kan kujera sannan ya tsugunna gabana
yace kiyi shiru zan tambayeki ne,nayi shiru ina share
hawayena yace yaya Abdulrahim yace yana sonki? nace
aah yayi ajiyar zuciya sannan yace alhmdll yayi shiru
zuwa can yace a gaskiya Iman na dade ina sonki shiyasa
ma har yau na kasa kula duk wata ya mace da sunan so
na mike tsaye na ce Kabir tun ina ganinka da gashi kar
ka yarda na kuma jin wannan zancen kana ganin balain
da muke shiga kullum a gidan nan sannan zakace wai
kan sona ni dai ba ruwana,ya zaro mani ido gami da
tasowa kamar zai bugeni yace sai kin soni kuma ni da
ruwana ba abinda ya dameni da fadan iyayenmu,na mike
zan fita yace kar ki yarda ki fita su Haj Laure zasu dake
ki muddin kika shiga,jin maganar duka ni uwar yan tsoro
na dawo na zauna na sanyaya muryata nace sun doki
Mama ne?yace suna hauka ne?ita ko kulasu ma batayi
ba shine yar Alhajinmu da tazo daga maska tace ta
shuga dakin Alhajin tasa na mashi waya yanzun nan yana
zuwa shiyasa nace kar kije,na cigaba da kukana yaya
Kabir yana lallashina har nayi shiru ya dinga shigar
dakan shi a guna yana ce min in na yarda yasan
Akhajinsu zai tsaya man kuma zai nemi canjin gun aiki
mu bar kaduna haka ya yi ta cusa min raayi har na soma
yarda,sai dai ina tunanin mama ba zata amince ba na dai
yanke shawarar zan ci gaba da addua. wayar yaya kabir
tayi kara yace in dauka don nafi kusa da wayar,na dauka
sai naga sunan yayanmu sai na mika masa yace ya baki
dauka ba?nace yayanmu ne ban san mai yake ce mazhi
ba na dai ji yace gata nan sai na kuma jin yace dakina
sai gabana ya fadi,sai naji yace to gata nan zuwa,ya
dubeni yace alhaji yazo yana dakinshi an ce kije,nace
yayanmu na gurin ne?yace shi ne yayi min waya wai
Jamila tace nine na tare ki ina kike yanxu sai shine nace
gaki nan ki tafi ko na raka kine?nayi saurin cewa a'a don
kar agan mu tare,cikin dar dar na shiga gidan yan biki
sai ni suke kallo gashi ko takalmi babu a kafata na shiga
ciki nayi sallama a kofar falon Alhaji na shiga Alhaji na

kan wata kujera irin ta karfen nan ne dama nan ne gun
zamanshi sai Mama akan kujerar gefen damanshi dayan
gefen Haj Yayace sai Haj Shuwa kusa da ita Haj Kulu na
dakin sai yaya ta maska(wato yayar Alhj)yayanmu na
kan kafet kusa da kafar Alhaji nima na shiga na samu
guri kusa da Mamana na zauna a kan kafet.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Alhj na gaisar sannan yayi gyaran murya yace to gara ke
Murja(haj yaya)menene sanadin wannan fadan?na
tambayeki dazu kince sai an kira Iman gata tazo sai ki
fda muji ynxu,ta soma magana cikin sababi ni dai Alhj
kawai kayi mani tsakani da Habiba da kuma 'ya'yana in
kai ta gama da kai to ni da 'ya'yana li'ilafi,,tashanye min
yara basa cin girkin kowa sai na 'yarta sannan yanzu shi
wannan miskilin dana gani kamar zai zama namiji amma
ba haka bane ya tashi sai kashe mata kudi yakeyi harda
yi mata anko da matar da zai aura me hakan yake nufi?
na dai san rokonshi sukayi don haka ayi mana iyaka dasu
ba 'ya'yanta ba nawa,tun da ta soma bata tsaya ba kuma
ba a katse ta ba,jin tayi shiru sai na dago kai na dubi
kowa kowa dai ita yake kallo sannan na dubi yayanmu
wanda kanshi yake kasa Alhj yace to naji naki ke kuma
Habiba ya abin yake?Mama ta soma magana cikin sanyin
murya lafuzza masu kyau tace ni dai Alhaji a gefena ba
wani matsala yarinyar nan dai itace matsalar, da zaka
amince min da sai na dauketa na maidata wajen
kawunta don inda bata nan gidan da baza ta ga ma
'ya'yan Haj Yaya ba bare su sata aiki sannan muddin
tana nan gidan ba zan hanata aiki ma kowa ba har Hajiya
Yaya inda zata sata,amma kiyi hakuri Yaya zan maido
maki da dukkan abinda Abdulrahim ya sai ma Iman
sannan kuma sai kiyi mashi magana ya daina sata aiki a
zauna lfy,na dubi Mama hankalinta a kwance tayi
maganar sabanin Haj Yaya wadda ke cika tana batsewa.
Dakin yayi shiru sai can a
Alhj ya soma magana yace Murja! Haj Yaya tace na'am
da karfi tana karkada kafa yace ina son kisan cewa
'ya'yan nan nawa ne kuma wancan ma tawa ce don ni da

kaina na daukota ko uwarta bata san zan kawo ta sai dai
ta ganmu Allah yasan wannan don haka ba zaki raba min
kan 'ya'ya ba kinyi kadan,Habiba yarinya ce a kanki
amma tafiki hankali da tunani saboda haka kar ki yarda
ki amshi duk wani abu da yayi mata kuma aiki duk wanda
yayi niyyar sata kar ya fasa don haka na gama wannan
maganar sannan ki gargadi laure ta kiyayeni da wasa naji
ta taba Habiba ko Iman sai nasa an daureta gara ma ta
tabaki zaifi mata sauki,Haj Maska tace yayi daidai
hakan,Murja in ka girma to kasan ka girma don haka sai
ta soma kuka tana cewa dama namiji ba dan goyo bane
nan na dauki kudina na baka ko basu ne silar arzikin naka
ba?daban haka ai da har yanxu kana a fakirin ka dole ka
min sakamako da mun wulakanci ta nuna ni tace ke
kuma zakiga hukuncin da zan yanke a kanki muddin kika
kuma ko kallon min 'ya'yane na durkusa da sauri(don har
ta mike)nace don son Annabi(SAW) kiyi hakuri bankade
ni tayi waje sauran kishiyoyinta suka take mata baya,Alhj
ya bisu kallo sannan yace Allah sarki to Allah ya sa ku
gane,ya dubi yayanmu yace kaima kayi hakurin dai zan
baka cikin sanyin murya yace Alhj kaimin izinin na koma
england jibi,yace na maka amma yaushe zaka dawo?kar
kaje ka kuma zama yace nan da wata shida ne yace to
Allah ya kaimu ya fita na bishi da kallo.
Karya ne gane halin da fuskarshi take ciki wato laifinmu
yake gani ko na uwarshi,ban taba ganinshi cikin dogayen
kaya ba tunda yazo sai yau boyel ne baki amma kanshi
ba hula Alhaji ya dubeni yace Allah yayi maki albarka
Iman kiyi koyi da halin mahaifiyarki kinji?na daga kai ya
cigaba da cewa muddin kikayi halin uwarki to kin
dace,sannan mijin da zaki aura ma yadace,su Abdulrahim
da Kabir duk yayyanki ne duk abinda suka saki
kiyi,sannan in sun maki kyauta ki amsa kice kin gode
nace to Alhj na gode,na mike na fita dakinmu na wuce
kai tsaye kan gado na fada raina a cunkushe na rasa me
ke daga min hankali son da Kabir yace yana min ko
matakin da Haj Yay tace zata dauka a kaina ne?wata
zuciyar tace duk ba wannan bane tafy yayanku ce
wannan amsar da zuciya ta bani itace sanadiyar tashina
zaune saboda tashin hankali da naji ni a ciki na mike ina
safa da marwa nace a fili ban so akayi wannan rikicin ba
ba zanji dadi ba muddin yayanmu ya tafi kai zanje na
bashi hakuri in ya tafi na mutu,da sauri na dauki hijabina

na fita falo nan nayi turus ganin mama a falon tace ina
kuma zaki?karon farko da na soma yi mata karya nace
gidansu Amira tace me xakiyi?nace takalmina da gyalena
dauko tace ko bari zata aiko maki ko ki aika Jamila kar
ki fita ko ina ynxu zo nan kiji,na isa gunta na zauna tace
kin dai ga abinda ya faru ko?nace eh tace to ina son kiyi
taka tsan tsan da kowa a gidan nan banda yawan
shigewa duk wanda ya saki aiki to kiyi masa kamar
yadda kikaji Alhaji yace maki,nace to ta kuma duba na
tace yanaga kinyi wani sukuku dake?nace bani son
tashin hankali ne mama shiyasa tace kar ki damu aikin
shedan ne kuma ki cigaba da addua sannan daga ynxu
zan na tashin ki duk dare in tashi yin nafila sannan zaki
dinga yin azumin litinin da alhamis,sai mu dinga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login