Showing 54001 words to 57000 words out of 76655 words

Chapter 19 - Idan Bake Book 1 Complete Naima Sarauta

Zahrah ta ce "magana ki kai?" Tai shiru ta kalleta da kyau ta ce..
"Ki gane baki da haɗi da dangin mijina, ke ƴar aikina ce, ki daina cusa kanki inda baki da mazauni ba zaki taɓa samun karɓuwa ba, saura ki faɗawa wani ke ba ƴar uwata bace kamar yadda nace"
"Sai dai kishiya ba ƴar uwa ba" da sauri Zahrah ta ce "kika ce me?" Ta girgiza kai ta ce "Salati nayi"
Ta ja tsaki tare da cewa "Get out jakar kawai"
11:00 Yaa Sheikh ya fito cikin wata haɗaɗɗiyar Alkyabba mai kyau da tsari, ya naɗa rawani wanda ya ƙara fidda haibarsa da cikar kamalar da yake da ita, fuska kame. Hannu goye abaya tare da carbi yana ja. Banda ƙamshin Roja babu abin da ke tashi a main parlour.
"Allahu Akbar Allah ya baka haƙurin zama da uwar mata Malam, ni tsoro na ɗaya kada a dinga nunaka da baki ana ka mijin sa'ar babar shi" Zahrah data ƙarasu parlourn tai tsaye a gefen Yaa Sheikh ba tare data kula Jadda ba ta ce.
"You look good My Excellency".
A can bedroom Kuka sosai Halisa take sai rigima take ita kawai wajan Dada zata, da ƙyar Mother ta rarrasheta, ta zuba mata komai na buƙata cikin torelly bag ba tare da sanin Zahrah ba.
Maimoon ta ce "Matar Yaa Lee ga gift inji Yarima Khalil" Mother ta ce "Gift?"
"Eh, shi ya bani wai na bawa matar Yaa Sheikh, ni kuma kawai zan bawa Halisa" Mother ta amshi box ɗin ta buɗe, wani gold ring ne mai kyau sai ƙyalli yake, ta ce "Zan ajjiye waje na, hannunta akwai ring har biyu ya isa, Allah ya tsare ya ki yaye sai na kira waya Daughter" Halisa ta kalli Maimoon tana mata gwalo ta ce.
"Yarinya na tafi gidan mijina, duk abin da ya faru zan ajjiye miki labari ko na dinga faɗawa Mother tana gaya miki" Mother ta ce "A'a na shiga uku bani a nan" Yaa Sheikh tuni ya shiga mota, shi kaɗai ne a baya Saif-wazir na driving..
Zahrah a motar Ishaq-Hakim ita da Halisa da Maimoon. Mother ta ce ba zai taje rakiya ba.
Kai tsaye gidan Abba Hakimi suka nufa. Yaa Sheikh ne kawai ya shiga sbd babu lokaci, ya shige jikin Abba Hakimi yana sauke numfashi, rauninsa ya bayyana kasancewar yana jikin Abban nasa, a karo na farko ya riƙe Abban da kyau murya bata fita ya ce.
"Ba zan iya ba Abba" Abba Hakimi bai fahimta dan haka ya ce "Kai mutum ne mai tsoran Allah da gudun hakƙin wani, balle matarka kada ka damu, ita Halisa ƴar riƙo ce shekara nayi zan amshi abata" ya zare jikinsa yana sauke numfashi tare da yin sallama.
Daga nan suka ɗauki Umar-khan kai tsaye suka shige Airport inda jirgi ke jira. Tunda daga jirgin hankalinta ya tashi amma bata nuna ba, ta riƙe hannunta da kyau, Umar-khan na gaba sai Zahrah Halisa na biye da ita a haka suka shiga cikin jirgin, suna shiga Halisa ta riƙe kanta sbd tsoro, Umar-khan ya kalli Zahrah ya ce "Wajenku na cikin vip" Zahrah ta kalle shi ta ce "Yana ciki ne?" Umar na zama a mazauninsa ya ce "Gaskiya ban sani ba, ku shiga ku gani" ba tare da Zahrah ta ce komai ba ta nufi vip ɗin, jin takun tafiya a bayanta yasa ta tsaya tare da kallon Halisa ta ce "Ke kuma lafiya kike boye ni? Na manta ba a saba ba, Umar nuna mata wajan zama"bai ɗago kai ba ya ce "Wajan zamanku ɗaya ne ai duk vip" Zahrah ta riƙe ƙugu ta ce "kan uba, tayaya haka ya kasance kana nufin tare zan zauna da ita ga mijina kuma?" Sai a lokacin ya ɗaga kansa tare da kallonta ya ce "To ai suna ɗaya kuka amsa, matsayi ɗaya"

"Kamar yaya suna ɗaya? Umar ya kamata kasan me zaka ce dani, ka gane" ya haɗe hannaye waje guda ya ce.
"A'a ranki ya daɗe, mai da wuƙar mijin naki shi ne ya bada umarnin haka" ta haɗiye yawun takaici tare da shigewa vip, daman ita Halisa ta jima da shigewa, dan haka Zahrah na shiga ta samu Halisa zaune ta sunkuyar da kanta ƙasa, wajan ya haɗu sosai akwai duguwar kujera wacce Halisa take zaune akai, sai kujera mai guda biyu, tunanin Zahrah ya bata mai guda biyun ita ce wacce zasu zauna ita da Yaa Sheikh, ta nemi waje ta zauna idanunta akan Halisa ta ce.
"Ina mijina?" Tai shiru taƙi cewa komai. "Ba magana nake miki ba, na lura kin fara ganin wajan barcina?" Ta ɗago lulu eye's ɗinta wanda suke sheƙi kamar an tara musu ruwa sbd yadda hawaye ya kwanta cikinsu. A tsiwa ta ce.
"Ina mijina?" Zahrah ta zare ido tare sakin baki da jin abin da Halisa ta ce. Ƴar fillo tai murmushi kawai tare da girgiza kai ta ce "nifa kamar haka naji kince Anti shi ne nake ƙara tambaya, to a haka naga wajan kam" Zahrah ta ɗaga hannu zata ɗauke Halisa da mari suka ji gyaran murya.
Gaba ɗaya suka ɗaga kai a tare daga Uwar gidan har amarya Zahrah, basu yake kallo ba wayarsa yake sakawa a airplane mode. Yaa Sheikh ya riƙe ya saba akan duguwar kujera yake zama, sbd yana ɗan samun hutu yayi barci kafin ya isa inda zashi, kai tsaye ba tare daya lura da Halisa ba ya nufi duguwar kujera tare da zama dab da ita. Numfashin Halisa ya kusa ɗaukewa sbd wani mugun shaƙar ƙamshin Roja da tayi, gashi Yaa Sheikh ya zama ƙato babba sosai har kafaɗar shi na rufe kanta.
A karo na farko zuciyar Zahrah ta shiga bugawa gabanta ya faɗi,ta juya ta kalli Halisa wacce ta kafe Yaa Sheikh da idanu, a hankali kuma ta kalli Yaa Sheikh wanda ya nuna kamar bai san da mutane a wajan ba. Ta kasa magana ta rasa a wanne ma'auni zata saka haka, anya bata hau tsaunin da zai kaita zuwa ga hallaka ba?. A zahiri Yaa Sheikh ya mance ya taho da matayen nasa har biyu, da uwar mata da kuma ƴar rainon shi. A hankali aka fara sanarwar a ɗaura blet, Zahrah ta ɗaura Halisa kuma ta rasa me ake cewa sbd cikin harshen turanci ake maganar, sai faɗa computer take tana ƙara sanarwa.
A nutse ya ware rawani kansa domin duk a zaton shi, shi kaɗai ne a cikin vip ɗin, kyakkyawar sumar shi ta bayyana abin mamaki ilahirin sumar kan shi daga gaba jajir take tamkar wanda ya fara furfura, daga baya kuma baƙaƙirin tai luff har wuyan shi. Ya sauke hannunsa akan Alkyabbar jikinsa ya ɗan buɗe gaban kaɗan sbd nauyi da tayi masa, yana kammalawa yaja blet, daidai lokacin aka fara sanarwar a shirya jirgi zai tashi, Halisa ta razana ta ƙanƙame jikinta, kanta ya shiga juyawa sai tayi nan luu tayi nan luu, lokacin da jirgi ya ɗaga zuwa sama Yaa Sheikh ya lumshe idanunsa ba zato ba tsammani yaji an fasa wata gigitacciyar ƙara kafin ya buɗe idanu ta faɗo kan cinyarsa babu numfashi....

Paid
It's 500
08119237616

Da fararen idanunsa masu tsari yake bin ta da idanu da mamaki, ganin da gaske bata mutsi tsoran da ya yi mata yawa ya sanya numfashinta ya ɗauke, hannunsa basu taushi ya sanya akan fuskarta kamar mai jin tsoran gently ya shiga bubbuga kumatunta amma ko motsi ba tayi ba, ya ɓata fuska ganin tun ba a je ko'ina ba, yarinyar zata fara bashi wahala.
Yatsun hannunta biyu ya kama yaja da ƙarfi yana buga tsakiyar kanta ajjiyar zuciya ta sauke da ƙarfi tana jan numfashi, sai kuma ta fashe da kuka tana riƙe wanda taji kusa da ita sosai cikin fillatanci take faɗin.
"Don Allah ku sakko dani ƙasa zan mutu wayyo Dada wajanki zan dawo" saukar numfashin da yaji yana sauka a fuskarta da ƙamshin da ba zata manta da shi ba ya sanya ta buɗe idanunta wanda ta rufe su saboda tsoro, wanda ta gani take jikinsa ya bata mamaki numfashinta ya kusan ɗaukewa, sbd yadda ya yi mata kwarjini a idanu ga Alkyabbar jikinsa duk ta rufe mata jiki, a jikinsa yaji shi take kallo bai kalleta ba, ya sanya hannu tare da riƙo kafaɗunta da kyau yana zaunar da ita akan kujerar sosai.
Yana daga inda yake ya ranƙwafa sosai tare da miƙa hannu zuwa inda blet ɗin take, kwantaccen sajansa ya shafi fuskarta ta sauke numfashi mai zafi wanda ya sanya Yaa Sheikh daka tawa da kama blet ya jima kafin ya zaro blet ɗin da sauri ya maƙala mata, yana ƙoƙarin janye jikinsa ta ɗora hannunta a tsakiyar tafin hannun shi..
"Uhmmm" ya ce a ransa yana ɗaga idanunsa zuwa gareta ya kalli cikin idanunta ba tare da ya ce komai ba, Halisa ta sake damƙe hannunsa da kyau cikin rawar murya ta ce. "Usako miyetti masin" idanu kawai ya lumshe mata tare da matsawa waje guda.
A fusace Zahrah ta kunce blet ɗin jikinta tare da tashi tayi kan Halisa tana kumfar baki ta ce.
"Ke dan uwarki mijina sa'anki ne da har zaki faɗa kansa da ƙazamin jikinki? Shegiya mara ƴan ci" Halisa ta kalli Zahrah ta ce "To Anti godiya nayi masa fa, kuma dana faɗa ƙasa naji ciwi ba ƙwara na faɗa kan shi ba, kuma ai ban masa nauyi ba ko kaji ciwo?" Ta faɗa tana juyawa tare da kallon Yaa Sheikh, shi gaba ɗaya hankalinsa baya kansu hannunsa riƙe da darija yana dubawa, tuni ya mayar da hiramin kansa baya buƙatar kowa yaga wani sashe na jikinsa.
"Kauuu!!" Zahrah ta ɗauke Halisa da mari tare da nuna ta hannu ta ce "zanci uwar data haifi babarki" ƙarfi da girman zagin yasa Yaa Sheikh kallon Zahrah a zuciyarsa yana Istigifari bai ɗauka wani zai iya zagin ba, ba a taɓa zagi a gaban shi ba, hakan ya zama abu sabo a gare shi. Bai ce komai ya ɗauke kai tare daci gaba da duba jaridar hannunsa, zafin marin yasa Halisa fashewa da kuka sosai tana kifa kanta a cinyarta, kuka take sosai wanda rabin kukan baƙin cikin zagin da Zahrah tayi mata ne. Yaa Sheikh kukan yake ji har tsakiyar kansa jin kukan na neman tarwatsa masa kai yasa ya miƙe tsaye tare da buɗe wata ƙofa ya shiga.
Zahrah ta kasa haɗiye mamakin yadda Yaa Sheikh ya nuna kulawa ga Halisa, haushin abin da ya yi yasa ta huce akan Halisa ɗin.
Sun yi nisa da tafiya sosai wata maid ta shigo cikin wajan tana tambayar Zahrah me za a kawo musu, Zahrah ta karɓi abin hannun matar ta duba, kana ta zaɓi abin da take so. "Nace ko zaki iya sauyawa wannan yarinyar waje?"Flight attendant ta ce.

"Her name please?" Zahrah ta ɗan kwaɓe fuska ta ce "Something Halisa.." ta ɗan danna wani abu a jikinta tare da yin magana bayan ta gama ta ce. "I think ita ce Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu right Maah?" Zahrah ta ce "No, bana tunanin ita ce her name is Halisa Danejo Rome" Flight attendant ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Sorry Maah babu da wani suna a jerin wanda za su yi tafiya yau, Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu shi ne" A fili Zahrah ta ce "Kan uba" sai yanzu ta tuna sunan Yaa Sheikh kenan, da sunansa akai mata visa kenan?.
"Oh maybe she's the one, zaki iya sauya mata wajan zama?" Matar ta ce "Yes Maa, daman yanzu na duba ta samu sauyin wajan zama tuni" Zahrah tai murmushin jin daɗi matar ta kalli Halisa wacce ko inda suke bata kalla ba sai Ajjiyar zuciya take saukewa.
"Can you follow me please?" Zahrah ta ce "ki mata hausa maybe she understand you" matar tai murmushi ganin yadda Zahrah take kwaɓe fuska ta ce "But she's your daughter?" Wata uwar harara Zahrah taiwa matar ta ce "Kinga alamar ina da ƴar ne?" Ita ma tai murmushi ta ce "Ai babu mmki idan nace miki a tunani zaki haifi yara biyar ma" Zahrah ta kalli jikinta da kyau ta kasa cewa komai, sbd baƙin cikin Flight attendant.
"Halisa biyo ni kinji" a sanyaye duk da tsoran jirgin da take tabi bayan matar har zuwa champer 2 na jirgin. Nan ma dai kujeru biyu ce kawai a wajan ba kowa, ta nemi waje ta zauna cike da tsoro.
Not too long da zamanta ya shigo tare da zama kan kujera da sauri ta sunkuyar da kanta domin a tunaninta faɗa zai mata, sai taga mai kulata ba ƙafarsa kawai ya miƙe. Tana zaune aka turo basket na abinci, zallar fruits ne sai gorar ruwa, aka ajjiye a gaban Yaa Sheikh ita kuma aka ajjiye mata chips da egg sai haɗin salad da ruwa. A hankali ya ɗauki orange ya saka bakinsa ya shiga taunawa cikin nutsuwa, Halisa ta kalle shi bakinta na rawa ta ce.
"Amma wannan abin yabann sha'awa ɗan sammani" ya jita sarai amma yai mata banza sai da orange ya ɗin ya rage guda uku ya ɗauki guda ɗaya zai ƙara sakawa a bakinsa tayi saurin riƙe hannun shi, bai zaici haka ba ya kalli hannunta tare da kallon gefen fuskarta ta langwaɓar da kanta gefe ta ce "Ayya ka sammin bana, ni ma idan kaga abuna zan maka naga kana ta haka da idanu" yabi idanunta da kallo yadda ta lumshe su tare da buɗewa tana gwada masa yadda yake, ta kwance na hannunsa tare da kawai bakinta, ta ɗauka wani daɗi ne a orange ɗin.
Ya sauke numfashi ganin hannunta na neman taɓa dugun gemun shi cikin ƙasa da murya mai sanyi ya ce. "Ci kani" ta yi saurin saƙona tana komawa wajanta, bai ƙara taɓa komai ba a kayan sai ruwa daya sha sosai.
Misalin 10 na dare jirginsu ya sauka a Prince Muhammad bin Abdul'aziz International airport, sai nasarwa ake kowa ya saka blet jirgi zai sauka, ganin bata fahimci me ake cewa ba ya kalleta da kyau, ya riƙa ya saka blet a jikinsa ba damar cirewa kuma sun ɗan bada tazara, a hankali jirgi ya fara girgiza yana rawa Halisa ta rikice daga tai nan sai tayi nan, shuuuuu jirgin ya yo ƙasa tai gaba luuu zata kifa shiru tayi jin an riƙo kafaɗar ta, ya haɗa da gefen ƙirjinsa tare da riƙeta.
Ƙuri tayi masa da idanu ganin nasa idon a rufe ta kasa motsawa shima kuma bai saketa ba, tunda har lokacin jirgin bai gama daidaita ba, balle ya samu damar sauka a titinsa. Ɓangaren Zahrah sosai taji daɗin ganin an ɗauke Halisa yanzu zata samu damar kasancewa da mijinta hankali kwance, sai dai tun tana jiran dawowar shi amma shiru gashi bata da ikon tambayar wani, bisa dole tai shiru. Bata tsammaci abin haka ba, sai ji tayi ana faɗin sun ƙarasu Madina tuni ai. A hankali ta saka blet tasan dai dole tare zasu tafi gida. Jirgi na yin parking ya saketa da sauri kafin ta buɗe ido ya fice daga cikin wajan, ta shiga zare idanu yanzu idan guduwa sukai yaya zatai?. Tana wannan tunanin Umar-khan ya shigo yana murmushi ya ce "Matar Malam tasu muje" ta miƙe tana kallon Umar-khan ta ce "To kai gida kaje ka dawo ne?" Yai dare ya ce "Hhhhhh ai kam na koma Nigeria na dawo" tabi bayansa da sauri ta ce "Kasan me" ya ce "sai kin faɗa" ta lumshe idanun ta buɗe ta ce "A ciki da abin ya tashi sama kawai na faɗa kan Malam na ɗauka zai dukeni kamar yadda anti da dake ni, sai naga kawai ya lumshe idanu ni kam nace masa na gode"

"Uhm" kawai Umar-khan ya ce domin bashi data cewa a wanann batun, suna fitowa Zahrah na fitowa suka kalli juna da Halisa kowa ya ɗauke kai. Bayan sun sauka daga jirgin Zahrah ta kalli motar dake gabansu ta ce "Ina My Excellency?" Ya ce "Yana da meeting ne, sai zuwa 12 zai dawo" Zahrah ta ce "meeting da wannan daren?" Umar-khan ya ce "Manyan mutane daman sai dare suke meeting, muje kada mu ɓata lokaci" Zahrah ta shiga bayan mota Halisa ba haka, Umar-khan na gaba shi da driver.
Wata haɗaɗɗiyar area suka nufa gaba ɗaya mazauna wajan larabawa ne, gidan dake kusa da na Yaa Sheikh sune hausawa, faɗar kyau da tsarin gidan Yaa Sheikh ɓata baki ne, flat gida na zamani, motoci birjik a harabar gidan ga tarin flowers da ɓangaren swimming pool, ga
Wajan tsuntsayen shi kusan duk rubutun gidan da rabci ne, yana da ɓangare na Musamman da yake bawa manyan mutane darasi.
Zahrah ta dubi haɗaɗɗan parlourn mai ɗauke da wasu ƙawatattun kujeru, sai ƙamshi yake, ga wasu fitito masu kyau iya haɗuwa ya haɗu. Umar-khan ya kammala shigo da kayansu ya ce. "Ɓangare uku ne a gidan, wancan ɓangaren Yaa Sheikh na tsakiyar kenan, na gefen dama babu na kowa na hango ma babu kowa, ya ce ki zaɓi wanda kike so, ɗayar ki bawa mai aikin naki" Zahrah ta kalli part ɗin hannun hango taga bayan na Yaa Sheikh yafi kyau dan haka ta ce "Na ɗauki na ɓangaren hango ka shigo mini da kayana ciki" tana faɗin haka ya miƙa mata key ɗin ɓangaren ta amsa hana shigewa ciki. Ya kalli Halisa ya ce.
"Daman girman kine shiga ɓangaren damar" murmushi kawai tayi, Umar-khan ya riga yasan da ɓangaren Yaa Sheikh da wanda Halisa zata zauna a manne suke, domin akwai ƙofa kai tsaye daga ɗakin Yaa Sheikh wacce zata kawo shi ɓangaren Halisa ɗin. Ya ja mata kayan zuwa jiki, ya yi mata bayanin komai da kitchen da banɗaki komai dai, kana ya nuna mata yadda ake amfani da kayan kallon ɓangaren ta.. "Sai da safe Matar Malam" ta jinjina masa kai. Zahrah ma ya kai mata kayan kana ya nufi nasa gidan.
Misalin 1:30 motar Yaa Sheikh tai parking driver ya buɗe masa ƙofa, a hankali ya fito ya ɗan tsaya yana duba ko wanne ɓangare yana yin addu'a sbd ya saba, ganin hadari a garin kuma yasa duk ya rufe Windows na gidan. Ya nufi ɓangaren shi, wanka ya yi ya ɗora jallabiya mai kyau a jikinsa, black tea yake son sha amma bai san yarda zai ba, gashi kuma yasa a sallami masu aikin shi. Haka dole ya zame jallabiyar ya saka kayan barci yana buƙatar hutawa sosai, sbd

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login