Showing 15001 words to 17626 words out of 17626 words
Chapter 6 - Tawa Ta Sameni Book 2 Complete by Halima Abdullahi k Mashi
haka na
shiga aiki gasky na raina tsaftar matar gidan banyi
karambanin gyra mata kicin ba nidai nayi iya aikina
farar taliya da miyar kwai da hanta nayi mishi a
gabanshi na jera komai na koma na zauna ya dubeni zo
mu ci kai kawai na girgiza dai dai lokacin da naji ringing
a cikin jakata na ciro wayar har ta katse na duba 11
miss call na duba su Mami ne da Adams na dubi
yaynmu dake faman cin abinci nace su mami na jirana
ya dubeni kin san bana son nacin magana ko?ya
kamata ki rike wannan ya cigaba da cin abincin shi sai
da yayi dam sannan ya shige dakinshi wanda an rubuta
master bed room a jikin saman kofar dakin da yellow
din kala kamar minti biyar ya fito zo muje
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
A ranar haka muka yi ta yawo a gari dan mugunta har
magariba kuka ne kawai banyi ba dan haushi wai ace
biki kamar na mami bana guri ai da takaici gashi ya
amshe wayata ya kashe na rasa irin wannan ikon,
gidan shi muka koma ya tafi masallaci ya barni wai
nayi sallah cikin dardar na zauna sai bayan ishai ya
dawo ko sallar ma banyi ba ya kuma daukata ya shiga
gari sai tara ya maidani gida lokacin an tashi daga
lunchn din dan haka dakinmu na wuce na fada gado ko
da mami ta shigo da fushi ganin ina kuka sai ta sakko
tana tambayata menene?cikin kuka nakece mata
yayanmu ne ya daukeni sai yawo yake dani ya hanani
zuwa gurin lunchn dinki tace ba komai kila shima yana
da dalili nace wanne dalili?shidai burinshi ya ga raina a
bace nan dai ta shiga lallashina. Washe gari aka daura
wasu mami aure, da daddare aka kai mami gidan Nasir
dake unguwar sarki tun fara bikin sai yaune muka sake
nida Adams dan yayanmu ya kasa ya tsare yaki barina
na cashe ashe shi yana can suna yinta da anty mimi
yace ba zata zo ba ita kuma tace sai ta zo ya gama
shirinshi tsaf ta taso har gun mota ta biyo shi tana
cewa sai taje,ta shige mota itama tata kama murfin
motar yace sake min tace sai fa naje yace ke kina fa
cin darajar cikin jikinki ne bayan haka dakin san ina
fada kina fada ba zata yiwu ba amma zaki haihu ba zan
dau wannan iskancin ba wata macen arziki ce zata bar
gidan aurenta karfe goma kuma bata san sanda za'a
tashi ba to tunda lallashi baya miki zan biki da zafi yaja
murfin motar ya rufe sannan yaja motar,muna tsaka da
fira sai ganinshi mukayi tsakiya suka sani shida
Adams,Adams ya dubeni mun zata ba zaka zo dinner
kanwa ba?yace kasan mai iyali saida na lallameta tayi
barci Adams yana yayi kyau muma dai Allah ya kaimu
ga jarawa ,ni kam kumallon ya motsa don haka duk
haushi suka bani Adams ya dubeni yar gidana kina
gaya min kince zakuyi lunchn da mene?nace sai mun
zauna dasu Amira menene na sauri Adams da sauran
lokaci fa,yace ba wani lokaci gara ki fada min don in na
tafi sai ana sauran kwana daya biki zanzo in nasan
komi tun yanzu zaizo da sauki,na dubi yaynmu wanda
yake ta aikin danne dannan waya tamkar baya jin mu
nan ko yana sauraren komai nace to kafin ka tafi
zamuyi zancen, gobe fa zan tafi cikin kosawa da
maganar nace to baga waya ba Adams yace to shi
kenan ya canja zancen da hajiyata tana son jin
muryarki bari na kirata ku gaisa,nace haba dai daren
nan?ka bari sai da safe yace to na bari kinsan ni ba dai
cikin gimbiya ba nayi dariya nace to Allah yasa ka dore
ba sai naje gidan ba a canza min yace haba aini din
nan ko bawa kika samu kinsan yanda nake son ki
kuwa?kin san nutson da nayi a kogin kaunarki?in da
ace kinsan yanda jiki da jijiya da bargo da kashi da
tsoka........kai yaynmu ya daka tsawa ya cigaba haba
Adams ka tasa yarinya karama kana wannan
kauyancin?ai wannan soyayyar dace in kana sonta
idonka kadai ya isa sheda ba sai kanata wannan batun
ba ka gane wannan ai yar da girma ne da ga ni har
adams kallonshi muka tsaya yi sai da ya gama sannan
yace Maska kai komai naka daban ne kana da hali irin
na masu girman kai...yaynmu ya daga mishi hannu ya
isa yi tayi,Sai karfe sha biyu muka tashi daga dinner
washe gari muna sallama da Adams yace sam bikin
nan bai min dadi ba,dan naso muyi hotuna muyi hira
mai isarmu amma haka bai samu ba nace kar ka damu
tun daga waya maganar hoto sai na shiga na miko
maka munyi sallama nabashi hotuna ya diba son ranshi
mun rabu akan sai naji shi a waya haka muka
rabu,bayan gama bikin mami yaynmu bai kuma damuna
ba sam gaisuwa ke hada mu sai dai da naje gidan
babana ne yake cewa yayanmu yana zuwa yana
gaisheshi har yazo da mai dakinshi ya yabeni tare da
fadin kirkinshi,ranar ma muna zaune a falon babana
dani da Anty Maijidda sai ga yaynmu sun gaisa da anty
maijidda sannan na gaisheshi anty tace kije ki kira
babanki na tashi na dauki dan kwalina naje na sanar
dashi,yana fitowa naga ya soma fara'a ganin yaynmu
suka gaisa sannan yace yazo ne ya mishi sallama dan
gobe zasu koma sai kuma nan da wata hudu lokacin
bakina da abokinshi babana yayi mishi godiya gami da
sa albarka sañnan yace ga kanwar ka nan dama ta
dameni wai nayi sallar magariba na kaita gida don haka
sai ta tashi ku wuce,na ce sai gobe zani,babana yace
a'a ni kinga gobe kwatano ma zamu,na soma shagwaba
nayi takwa takwa da fuska nace nidai to ai baka sai
min abinda kace ba yace me nace zan sai maki?
computer yaynmu ya harareni na kauda kai babana
yace to in na dawo ranar sati monday sai na sai maki
shi kenan?nace eh yace to uwata maza tashi yaynki na
jiranki na mike ina fadin ko kana korata ne?ba zan sake
zuwa ba suka sa dariya shida anty Maijidda yace wane
ni na kore ki ban isa ba nayi kadan anty tace naje daki
na dauki kayana na dauka tace na gaida mamana,tunda
muka dau hanya ni da yayanmu ba wanda yayi magana
can yace gobe zamu koma sai kuma bikinki na dubeshi
to Allah ya tsare hanya na fada cikin karfin hali,tunda
muka zo gida muka samu haj yaya a harabar gidan na
soma tsuma,cikin tsoro nace gasu haj,to menene yace
yana fakin na fito da ido suka bini shi kuma ya nufi
gurin su ni kam gida na wuce,yace haj daga ina?ta
daure tace nan makwafta muka shiga barka ta cigaba
matarka tana jiranka ashe kai kuma kana nan kana
yawon banza daga ina kake?daga tudun wada,gurin
wa?gurin baban iman ta kuma dubanshi muje ciki gani
nan tana mamakin halinshi shi mutum ne wanda baya
shakka ko karya komai zai fada in dai gsky ne zai fada
sai dai a mutu
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Haj yaya fada take tana karawa tace eh dan shashanci
matrka ta na nan tana jiranka kai kuma ka tafi gidan
kanin ubanka yace to haj dan naje munyi sallama shine
damuwa?to kiyi hakuri ta dan sassauto kai baka da
tunani yanzu in kai wanine yaushe zaka bar Adamu
abokinka ya nemi yarinyar nan ga kannenka?yace
wadanne kannen kuma bayan sunyi aure?ko ba ma
haka ba ai matar mutum kabarinsa....tace nasan haka
amma ni na sha alwashin sai na hana auran Iman da
Adamu in dai ina numfashi yanda bana son ta rabeni
kaima bana son ta rabi na kusa da kai kaf yayana
wacce ce ta samu mai kudi dan mai kudi kamar
Adamu?babu dan haka itama ba zata aureshi ba,sororo
yayi yan dubanta sai da ta gama sannan yace to haj ke
me zakiyi akai?dan Allah ki bar maganr nan,tace nasan
abinda zanyi kai dai tashi ku tafi Allah ya tsare hanya
kana can zakaji lbr,yaso yayi mata nasiha gami da
shawara amma sai taki ta hau shi da fada,dan haka sai
yace to haj zan wuce ba zan samu dawowa da safe ba
saboda sammako zamuyi ta kano zamu tashi sakon ki
gobe in Kabir ya kaimu kano ya dawo zaije banki ya
amso maki kudin,ta ce zaka kara min dubu talatin akan
na da yace ba komai zai kawo maki ina Mimin mu
wuce,haj tace tana gidansu, ya dubi haj wa yace taje
jiya fa can ta yini haj tace ai ba'a gajiya da gida ka dai
biya ka dauketa yace Allah ba zan biya ba tunda ban
aiketa ba in ta dawo shi kenan in bata dawo ba ta
zauna,Haj ta dubshi gara da ka nuna na gani dama ta
kawo min kara kana wulakantata son ranka yace haj ni
kinsan abinda take min ne? bata san kula da miji ba
bata san darajar miji ba bare yanda zatayi biyayya son
jiki bata iya girki ba,ni nasan ina da mata amma sai na
fita yawon gidajen cin abinci,tace to ai komai dan
lallashine yace wane lallashi ne ban mata ba amma
nasan maganinta zata gane bata da wayo,ya mike mun
tafi haj tace Allah ya tsare kar dai ka yarda naji wata
magana.
Sosai su haj yaya suka hau shiga malamai duk wai dan
araba Iman da Adams ko ina ruwansu oho?nikam
bansan me suke ciki ba,muna hira da Adams yanzu na
sadaqar shine mijina kuma na hakura shirye shiryen
dasu mama keyi na bikin nan ba dama har dubai su
mama sukaje da anty yagana ga wasu jike jike da suke
faman dirkamin bansan ko na menene ba sunce ma in
saura sati biu bikin zamuje maiduguri a gyarani bansan
gyaran da za'a min ba tunda dai nasan nima ba dan
laifi baka ce amma ba bakikkirin ba hancina ba dogo
bane kuma ba gajere ba bakina mai dan fadi da sirrin
lebuna idona farare kal kuma ba kanana ba ne gudar
gadar ne musamman ma in na tsorata kamar yanda naji
ana cewa,sai muryata ni kaina nasan ina da murya mai
shegen dadi game dajiki nasan akwaini dan kasa da
sama ba matsala mutane da yawa jikina ke rudarsu ba
wai so ba to ban san gyaran da suke nufi ba.Yau ni da
Amira gidan mami muka je dan shirye shirye bayan
munci munsha sai muka shiga abinda ya kawo mu can
nayi tsaki gara mu tsaida magana don sati na sama
zamuje maiduguri mami ta ce yin me?na dan tabe baki
wai gyarani za'ayi har ma dariya abin yake bani mami
tace ba sauki nace dan Allah wai gyaran menene?
sukayi dariya Adamu zai baki amsa gabana ya fadi
nace kuyi min bayani mana,mami tace kefa mukayi
magana dake kwanaki nace ni duk ynxu tsoron Nasir
nakeji kikace ke bakya tsoron Adams to zaki ji tsoron
nesai kin shiga hannu,mu dai ynzu mun ketare sai ku,
gashi har wani gyara za'ayi mashi Amira ta yi dariya
tace nidai hankalina kwance nace zaima tashi ne na
dubi mami nace da wuya ko?mami tayi dariya tace
bance ba sai ta kuma kwashewa da dariya nace
muguwa tace ba komai zan dai ji jiki ne.Tin ana sauran
sati uku biki Adams ya aiko min da katuna ban taba
ganin kati mai kyau irin wannan ba tunda naga katin sai
jikina yayi sanyi na shiga daki sai kuka,babana ya kirani
yace duk abinda nakeso na fada nace komai yayi min
yayi,yayi yayi muje kasuwa na zabi kayan daki da kaina
naki,yan uwan Adams sun kawo kaya akwatina saiti biu
sai naga ma kamar ba gaske ba,yau juma'a maiduguri
ta dauka tun da muka je sai aka shiga gyara ni daki aka
ware mani nida mai gyarani nan gidansu anty yagana
satinmu daya mun dawo ana saura sati daya bikinmu ni
kaina nayi mamakin kaina dana dubi madubi sai kace
bani ba yanzu kam na yarda gyara na mukaje dan nayi
kyau san da na dawo su Amira sunyi nisa da rabon kati
duk wanda ya kamata sunkai mishi batun yan gidan mu
su haj yaya sunsha mamaki ganin shirye shiryen da ake
ganin gyare gyaran da ake min ya kara firgita su gashi
boka ya masu alkawari za'a fasa auren gashi har lefe
yazo mai yawa koda mama tace sujesuga kaya ba
kunya sukaje don gulma ganin kaya da gwala gwalai
sai jiki ya kuma sanyi waya haj yaya tama laure akan
tazo da magana bayan sun shiga uwar daki haj yaya
tace laure zama bai ganmu ba kaya tun ana kirga
zannuwa da nazo hamsin sai na daina ganin gwala
gwalai sai hawan jini na yaso taso ya tashi ba arziki na
fito daga dakin haj laure tace ynxu menene abinyi?yaya
tace innaga gurin malamin nan zamu koma....
Adamszaune gaban malami ko nace boka ya dubesu
kin cika gajan hakuri an daura auren ne?suka ceaah
yace to na gaya muku ba shi ne mijinta ba zaa ba wani
ne adakaa zaku sha mamaki kuje ku nutsu nan da
kwana uku zakuji lbr ya canza rauhanai sunanan suna
aiki yanda ya kamata nan suka yi godiya suka fita.Yau
sauran kwana uku biki zaune nake akan kujera a wani
daki gidan anty yagana nan muke nida kawayena yar
borno wacce ta gyarani a maiduguri itace ta zo yau
danmin lalle na musamman an zana shi hannu da kafa
an ratsa jan rani dama kafin a fara sai da aka milkeni
da wasu mayuka na gani na fada masu tsananin kamshi
da su launin fata dama tun da muka dawo daga
maiduguri kamshi duk inda na ratsa sai na barsu da
kamshina yar borno na zaune tana kankare min lallan
ba bose wata mai gyaran gashi ce ma kwaf tun su anty
yagana ne ta hadda ai gyaran gashi ita ce tasa man
gashi mai tsada tana min shampoo sai tabke min gashi
takeyi wai nayi dabara da ban fara sa mai ba sai da na
tashi aure ni dai jinsu kawai nakeyi saboda yau haka
nake jin jikina,can text din da aka saba yimin ya shigo
Amira ce ta miko min waya gashi ango yayo text nace
ba ango bane na duba sai naga ina miki murna amma
har ynxu bancire rai da samun ki ba har sai na ga an
daura miki aure abinda bana fata dan ban san ya zan
kasance ba wannan ranar,nace kaini wannan mutumin
ya dameni Amira karanta ki gani wanda nake gaya maki
din nan ne ta amsa tana kokarin dubawa tana cewa kila
ma Adams ne kin kasa ganewa kafin ta gama dubawa
sai ga call ganin sunan Adams ya sanya ta bani tace to
ga ango ki ce mishi ya fa iso yau don gobe zamu soma
shagali kuma muna so kowanne yaje,duk surutun da
take yi ban saurare taba dan sai samu kaina da wata
mummunar faduwar gaba na amshi wayar na daga sai
naji muryar Adams cikin sanyi da sakewar murya yace
Amina gabana ya fadi dan bai taba kiran sunan ba,na
kwace kaina daga hannun bose nace Adams menene
yace dan Allah kiyi hakuri banyi niyar yaudarar ki ba
amma am sorry ba zan aure ki ba na fasa sai dai still
ba zan daina sonki ba,jikina ya soma rawa nace adams
ka cuceni me nayi maka? A...A....Adam...ka,ban
karasa ba sai kirjina ya tokare jikina yana ta
karkarwa,na dai ji su bose da yar borno suna tambayata
lfy?Amira na salati daga nan sai na fadi
Kash sai mun hadu a na uku don jin yadda zata
kasance
Halima Abdullahi k/mashi