Showing 18001 words to 21000 words out of 25074 words
saida ta 'kara kan
wanda suka zuba}```
Khaleed kuwa koda yaga yanda Auta ta fita hayyacinta, tanata kuka saboda yaji, besan sanda
yayi saurin zuwa inda takeba ya rungumota jikinsa, ya nufi kujera three saater da ita ya zauna
ya d'orata kan cinyarsa, yana rarrashinta kamar wata 'karamar yarinya, ruwa ya d'auko ya zuba
cikin cup yabata ta shanye amma yana cire cup d'in daga bakinta saita fashe da wani sabon
kuka,
Lokaci guda khaleed ya rud'e yarsa yanda zeyima Auta taji sau'kin yajin.
Bakinsa ya d'ora kan nata tare da tura harshensa cikin bakinta yashiga tsotsar bakin nata
kamar yasamu wani sweet , wai a dole ze tsotse mata yajin,
Dama abinda auta ke nema, itama tacigaba da kissing d'insa tana 'kara shigewa jikinsa, lokaci
guda khaleed ya susuce ya manta da maganar wani yaji dayakeji, yacigaba da aika mata da
sa'konni masu wuyar fassarawa, ita kuma sai wani 'kara shigewa take jikinsa tana shagwa6ewa,
Abu yayi nisa hannuwan khaleed kan 'kirjin Auta yanata wasa da dukiyar fulaninta, itako batayi
'ko'karin hanashiba saima 'kara mi'ka mashi kanta datayi.
Wani irin kukan ba'kin ciki Fadeela ta fashe dashi, dan duk abinda sukeyi gabanta sukeyi,
kallonsu kawai take takasa magana saura kad'an zuciyarta ta buga, wannan kukan dayazo
mata shine samun sau'kin takaici da ba'ki cikin da Auta ta 'kunzuga mata.
Da sauri ta tashi tanufi d'akinta, minti biyar batayiba da Shiga, sai gata ta fito, sanye da gyale,
da takalmi a 'kafarta, sai yar poss a hannunta,
Sai lokacin ta iske khaleed ya sake Auta, amma suna zaune kusa da juna kowanensu yana cike
da sha'awar d'an'uwasa saboda wasanni da sukayi, abin ba'a cewa kome .
Bata ko kallesuba tanufi 'kofar fita daga falon, fuuu kamar zata tashi sama, khaleed ne yayi
saurin tashi yabi bayanta yana tambayarta "Fadila ina zaki?
Bata ko saurareshiba tayi gaba abinta.
Tana fita get d'in gidan takoyi sa'a wani me napep ya ajiye wata mata wani gida kusa dasu, nan
tafad'a mashi inda ze kaita, tashiga.
Khaleed na fitowa napep d'in na barin 'kofar gidan, "ya salamm ya furta, can kuma sai yayi wani
guntun tsaki yace
```"kinyi laifi kuma kifi wanda kikayiyamawa zuciya```
Gida ya koma ya iske Auta zaune inda yabarta, nan take tambayarsa, "Lafiya kuwa saboda me
Fadila ta tafi, be bata amsa ba sai rungumota dayayi jikinsa yafara shafata ta ko'ina, Auta batayi
'ko'karin hanashiba saida taga yana neman wuce gona da iri, sannan tayi saurin tureshi, ta tashi
zaune, nan khaleed ya marairaice mata yayi kalar ban tausayi yace (please Auta help me) ki
taimakeni nariga na shiga wani yanayi, cike da tsoro Auta ta kalleshi taga yanda idanunshi suka
kad'a sukayi ja,
Lokaci guda ta langa6e tana bashi ha'kuri "kayi ha'kuri my dear kaga ba aykina bane, yanzu
idan nabaka kaina mun shiga ha'k'kin Fadila, kayi hakuri kada kasa kanka cikin maza masu
rashin Adalci tsakanin matayensu.
Haka Auta ta rarrasheshi har ya hakura, nan ya wuce dakinsa, ya shiga toilet yasake watsa
ruwa sannan ya dawo yabi lafiyar gado.
Itako Auta yana shiga d'akinsa, itama nata d'akin tanufa tana ahiga ta she'ke da dariya tace
~_(Fadila dani kike magana)_~
Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 7:55 PM] +234 816 616 9254: [13/08 7:03 am] .:
*AUTAR HAJIYA*
®NWA
_ZEE MMN KHADY_
```Page``` 141-145
✍ Da sallama Fadila ta shiga gidan, falo ta tarar da momynta tana zaune hannunta rike da
(newspaper) jarida tana dubawa,
Cikin fara'a ta kalli Fadila ta amsa mata sallama, dai-dai lokacin Fadila ta tsinci kanta da tinanin
yanzu idan momynta ta tambayeta meya kawota me zatace,
Muryar momynta ta katse mata tinanin datake,
"Ina me gidan naki na ganki ke kad'ai? Fadila tayi saurin dawowa daga tinanin datake ta
kalli momynta tayi murmushi, dan bataso ta gane tana tattare da wata damuwa, tace "shine ya
saukeni yana sauri ne yanada meeting a office d'insu shine ya wuce, yace idan yadawo
d'aukata ze shigo, Momy tace "owk" Sukayi shiru na 'yan wasu mintittika, Fadila kuwa tunani tashiga yi, a zuciyarta tana cewa:
*_Yanzu wannan 'karyar danayi idan khaleed ya'ki biyoni ya zanyi, kokuma idan yazo yace bada
izininshi na fito ba , Allah dai yasa ya rufa min asiri_*
"Fadila lafiya naga kinyi shiru kamar kina tunanin wani abu, kodai akwai abinda ke damunki ne?
Da sauri Fadila ta washe ta tashi tana murmushi tace "lah ba kome Momy, tanufi hanyar
kitchen tana fad'in me kuka dafa wlh yunwa nakeji,
Bata jira amsar Momy ba tashige kitchen tazubo tuwon shinkafa da miyar d'anyar ku6ewa,
sannan ta d'auko lemu a pridge ta dawo falo ta zauna tafara ci, Momy kuwa kallonta kawai take
azuciyarta tace *Anya Fadila*
"Fadila yanaga kinatacin abinci haka kamar wacce ta kwana bataciba?
Fadila tayi saurin kai dubanta ga momynta tace " banci abinciba na fito saboda ina d'okin
ganinki Momy, tafad'a tana murmushi,
Itama Momyn murmushin kawai tayimata tacigaba da duba jaridar dake hannunta.
Har misalin 'karfe shidda da rabi na yamma khaleed bezo d'aukar fadila ba, momy ta kalleta
tace "khaleed shuru kodai ya manta dake ne,
Fadila taji gabanta yafad'i tace "a'a Momy yana zuwa, inaga har yanzu begama abinda yake
bane.
Fadila tashiga damuwa hankalinta yafara tashi ganin har angama sallar magrib amma khaleed
bezo d'aukar taba, gashi bataso dadynta ya tarar da ita kuma tasan ana gama sallar isha'i ze
dawon gidan.
Karar tsayuwar motarahi ce ta dawo da ita daga dogon tinanin datakeyi,
Da sallama ya shigo gidan, Momy ta amsa tare da yimashi sannu da zuwa, falo akayimashi
masauki, bayan sun gaisa ya kalli fadila wacce dama on ready tagama shirin tafiya zuwanshi
kawai take jira, yace "ki taso muje ko kinga dare yafara,
Wani sanyi fadila taji cikin zuciyarta, da khaleed be fad'i dalilin tahowarta ba.
Haka suka bar gidan, Fadila, nata godema Allah daya rufa mata asiri, dan yau da Momy tasan
da yanda ta taho gida da ranta idan yayi dubu sai ya 6aci.
Haka suka shiga mota suka d'au hanya, tinda suka fara tafiya ba Wanda yacema d'an uwansa
kome har suka isa gida.
Koda fadila tafito daga motar kasa shiga tayi gidan saida tajira khaleed sannan suka shiga tare,
Falo suka iske Auta zaune kan kujera, sanye take da wata riga me hannun bes da wani d'an
'karamin siket iya gwiwa, hannunta ri'ke da remote tana canja tasha zuwa *ZEE CINEMA*
dayake ita meson kallon Indian film ce, kanta babu ko d'an kwali gashin nan ya zubo 'kan
kafad'unta, cike da murna ta taso ta rugume khaleed, "sannu da zuwa mijina, murmushi yayi
tare da bata kiss a kumatu yace "yauwa matata.
Fadila kuwa tana tsaye tana kallon ikon Allah, sai lokacin Auta ta kalleta tace "Andawo lafiya,
Bata amsa mataba illah wata uwar harara data buga mata sannan taja dogon tsaki "mtswwwww
ta wuce d'akinta.
Khaleed ma d'akinsa ya wuce,
Auta kuwa dariya tayi, dan ganin tagama 'kule fadila, ta koma ta zauna taci gaba da kallonta,
canja tasha tayi zuwa *STmusic* aiko ta iske an sanyo wa'kar *justing viiver* cikin wa'karshi me
taken _(Love me love, kiss me kiss me)_ dama tana masifar son wa'kar duk ta iya ta, saboda
haka taciga da bi, tana 'yar rawa daga inda take zaune.
Lokacin Fadila tafito daga d'akinta tanufi kitchen, ta kai dubanta ga Auta wacce tayi kamar
batasan da mutum a falon ba, wani 'kululun ba'kin ciki ya tsaya mata tayi tsaki Mtsww "Aykin
banza tafad'a sannan tawuce kitchen din.
Zee Elkaseem
Mmn Khady
[13/08 8:10 am] .: [13/08 7:40 am] .:
*AUTAR HAJIYA*
®NWA
_ZEE MMN KHADY_
```Page``` 146-150
✍ Washe gari, Fadila tagama had'a musu break fast, kunun gyada ne ta she'ka musu, yayi
gwanin kyau, dan ta masifar iya kunun gyad'a dan duk cikin abinda take girkawa a gidan shi
kad'ai ne takeyi susha cikin kwanciyar hankali, kuma wani lokaci har khaleed ya yaba.
Yauma shine ta she'ka masu, tare da soya masu dankakali da kwai, bayan tagama ta jera kome
kan dinning ta koma d'aki dan yin wanka.
Auta kuwa dayake ba itabace meyin girkin tuni ta dad'e da yin wankanta ta shirya cikin Riga da
siket na material tayi kyau sosai.
Tana jin shigewar Fadila d'aki, sai tafito tana tafiya ahankali, sad'af-sad'af yanda ba Wanda ze
iya jiyo 'karar takun ta, hannunta ri'ke da wani 'karamin cup, dining tanufa inda fadila tagama
jera kayan break fast d'insu, ta bud'e, plask d'in dake d'auke da kunun gyad'a wanda yaji peak
milk yayi fari 'kar, ta zuba abinda ke hannunta cikin cup, ta d'aga plask din tad'an jijjiga yanda ze
gauraye kada a gane anzuba wani abu daga baya, tayi saurin komawa d'akinta.
Zazzaune suke kan dinning kowane da cup me d'auke da kunun gyad'a a gabansa, dankalin da
kwai suka fara ci saboda kunun akwai zafi,
Khaleed ne yafara d'aukar cup din gabansa yakai baki, dan yana sauri yafita aiki dan yau
yanada patient's dayawa a hospital,
Wani irin d'and'ano yaji na daban, cikin kunun Wanda ko a mafarkin baya tinanin jinsa cikin
kunun,
Cike da 6acin rai ya kalli Fadila, ya daka mata harara tare da Jan wani irin dogon tsaki
"Mtswww,
Fadila bata kai ga fara shan kununba saboda haka batasan yanda testing d'insa yakeba, cike
da 6acin rai tatashi tafara magana tana d'aga murya "gaskiya khaleed nagaji da cin mutunci da
cin zarafi dakakemin cikin gidannan, shikenan ni kullum nice abin wula'kantawa dan kana ganin
wannan kod'dad'iyar yarinyar tare da kai.....
Kafin ta ida rufe baki, sai jin abu tayi ajikinta, wata irin 'kara ta saki dan kunun yanada sauran
zafi, zuciya takai khaleed ya watsa mata shi, cike da masifa yatashi yana cewa "ke har kinada
bakin dazakice anyi maki rashin adalci, kenan adalcinne yasa zaki zambad'a mamu uwar kanwa
cikin kunu, wannan kanwar da kika zabga ko kunun kanwa aka zubamawa baze shawuba,
barantana kunun gyad'a wanda beda had'i da kanwa.
Sai lokacin Auta tayi magana, tace kayi ha'kuri mijina, kayimata uzuri, wata 'kila da kunun
kanwa zatayimana, kasan shima yanada dad'i sosai.
Bebi takansuba suduka, cike da 6acin rai ya d'auki makullin motarsa yafita,
Har yabar falon Fadila na tsaye gurin kamar an dasata, ba abinda take sai zubar da hawaye,
Auta ta tashi ta kalli fadila, datayi tsaye da kunu ajiki, har ga Allah tabata tausayi, amma kuma
koma miye ita ta fara,
Dariya tayi, tace *"Kije ki wanke*, tashige daki tana cigaba da dariyarta, har Fadila na jiyo sautin
dariyar.
Haka Fadila ta tattare rigar tanufi d'akinta, tacire, sannan tafad'a toilet ta sakarma kanta showar,
bayan ta gama wankan ta dad'e toilet tana kuka.
Bayan tagama wanka ta sake shafa lotion me dad'in 'kamshi, ta saka wasu kaya.
Auta kuwa tana d'akinta ta kwanta ruf da ciki kan gado, tana danne-danne cikin wayarta, kawai
jitayi kamar alamar mutum a kanta, da sauri ta d'ago takai dubanta kan Fadila wacce ke tsaye
tana cika tana batsewa.
Take wani irin mugun tsoro yakama Auta,dan ganin Fadila yau har cikin bedroom d'inta, tasan
idan za'a barta da Fadeela sai dai taci na jaki.
*_innalillahi'wa,inna'ilaijirraji'un_* tashiga furtawa duk illahirin jikinta kyarma yake, gashi ba kowa
gidan daga ita sai Fadila.
```Su Auta anbani ga tsoro ga jan fad'a nidai zee barin gidan nayi dan bazan raba wannan
fad'an ba, tsuntsun dayaja ruwa shi ruwa kan doka```
Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 7:55 PM] +234 816 616 9254: [13/08 5:47 pm] .:
*AUTAR HAJIYA*
®NWA
_ZEE MMN KHADY_
```Page``` 151-155
✍ Tafiya yake a mota amma zuciyarsa cunkushe da tinani kala-kala, saida yakusa kaiwa
asibiti, ya tuna da ya manta wasu muhimman takardu wanda yau ne yakamata yaje dasu,
Juya akalar motar yayi, ya koma gida, me gadi yatashi da Sauri ze bud'e mashi get, amma
sai ya tsaidashi, yace" kabarsa kawai zan ajiye anan dama wata yar mantuwa nayi zanshiga na
d'auko, me gadi ya russuna yace "to ranka ya dad'e.
Shiru ya iske falon alamar matan gidan kowace na 'dakinta, sallama yayi sannan yashiga,
d'akinsa ya wuce kai tsaye,
Auta kuwa tana kan gado ido ya raina fata, ga fadila na tsaye bata dai tankamata ba, kuma
batada niyyar barin d'akin,
Cikin sa'a Auta tajiyo sallamar khaleed a falo, wanda ko kad'an fadila bata jiba, kodan tana cikin
6acin raine, oho
Saukowa tayi daga kan gado, tazo gaban fadila ta kama wuyan rigarta tacimata kwala, sannan
ta kwanta kasa ta fasa ihu tana cewa "dan Allah kiyi hakuri, wayyo nashiga ukku zata kasheni,
menayimaki zaki kama dukana, wayyo Hajiya kizo zata kasheni, iya karfinta take maganar cikin
murayar kuka tana kuma buga 'kafarta jikin gado da bedside, sannan kuma takama wuyan rigar
fadila ta ri'ke sosai, hakan yasa dole fadilar ta duko yanda idan kagani sai kace dukanta takeyi
da gaske.
Fadila kuwa mamaki ne yagama rufeta, tanata kokarin 6am-6are wuyar rigarta daga hannun
Auta amma ta kasa, saboda Auta ba 'karamin ri'ko tayi mataba.
Khaleed na d'akinsa yana tattara takardun dayazo nema, yajiyo ihun Auta tana Neman taimako,
aiko da hanzari yanufi d'akinta dan ganin abinda ke faruwa.
Fadila yagani duke kan Auta, itakuma tana kwance 'kasa tana Neman taimako, da sauri ya Isa
gurin ya jawo fadila da iya karfinsa, wadda ganinsa yasa Auta tasaketa daga sha'karar
datayimata,
Wani lafiyayyen mari ya d'auketa dashi, Fadila tayi saurin dafe gurin daya mareta, zatayi
magana ya'kara d'auketa da wani lafiyayyen mari, yana huci yace "bakida hankali fad'ila zaki
kama 'yar muatne da duka haka, so kike ki kasheta.
Lokacin kuma Auta ta tashi daga Inda take kwance tayi wujiga-wujiga, fuskar nan sharkaf da
hawaye, idan ka ganta saika rantse kace mugun duka akayi mata.
Fad'awa tayi jikin khaleed tana kuka, shikuma ya rungumeta yana rarrashinta kamar wata
yarinyar goye, sannan ya maida dubansa ga Fadila wacce ta dafe kunci tana zubar da hawayen
takaici,
Yafara bal-baleta da masifa, ta inda yake shiga batanan yake fitaba, iya tsawon rayuwar Fadila
bata ta6a sanin khaleed nada fad'a haka ba sai yau.
Bayan yagama zazzagamata bala'i sannan ya nuna mata Kofa yace *(Get out)* ki fita nace
daga d'akinnan tin kafin inyimaki mugun bugun dazaki kasa tashi, sha-sha-sha wacce batasan
girmantaba, in banda sakarci me zaki daka jikin Zainab,
Ki duba girmaki ki duba nata, kin kai biyunta,
duk maganar nan dayake Auta na rungume jikinsa tana kukan shagwa6a.
Haka fadila tabar d'akin cike da takaici, tana mamakin yanda Auta ta Jamata sharri cikin
'kan'kanin lokaci.
Babban falo ta zauna tana sharar hawayen ba'kin ciki,
Kusan kimanin minti talatin Fadila na zaune falo tana kuka, sannan khaleed yafito shida
Auta,yana mata magana wacce fadila batajin me suke cewa amma dai taga Auta na dariya
hadda kyalkyatawa,
Saida sukazo gab da ita khaleed ya kalleta ya buga mata wata uwar harara, yace "gatanan zan
tafi gurin ayki, idan kin isa' kin haihu ga iyayenki, kuma kin isa marar mutunci to in dawo in iske
gawar Auta a gidannan, yabuga wani dogon tsaki "mtswwww sannan ya wuce, tare da ba Auta
lafiyayyen kiss a kumatu yace saina dawo matata, *(Tak care of your self)* ki kulamin da kanki,
wani lafiyayyen murmushi tayi mashi tace *(never mind my husband)* karka damu mijina.
Haka tarakashi har bakin get saida taji 'karar tashin motarshi Alamar yatafi, Sannan takama
hanyar komawa cikin gidan.
Saida tazo 'kofar shiga falon tatsaya tana tinani,
"{```Yanzu idan nashiga Fadila takamani ba abinda ze hana ta rama marin da nasa akayimata,
me sau'ki kenan idan batayimin d'an banzan duka ba}```
Tsayawa tayi tana shawarar yanda zata shiga d'akin, ga kuma fadila zaune.
Ta dade nan tsaye kafin ta yanke shawarar ta wuce d'akinta da gudu kada tabari Fadila ta
kamata.
Haka kuwa akayi da gudu, tashigo falon da niyyar ta wuce d'akinta ta kulle kanta, bazata fitoba
sai khaleed ya dawo, amma ina, tariga ta makara, dan ko kusa da 'kofar d'akin bata kaiba Fadila
ta dam'kota.
Zee Elkaseem
Mmn khady
[13/08 6:54 pm] .:
*AUTAR HAJIYA*
®NWA
_ZEE MMN KHADY_
```Page``` 156-160
✍ Auta tagama tsorata da yanda Fadila ta dam'kota, tanayimata wani mugun kallo,
Lokaci guda 'yan cikinta suka motsa saboda tsoro, harta hangoma kanta irin dukan dazatci
gurin Fadila.
Amma a fili saita nuna dakewa, ta kalli Fadila Alamar ba tsoro ko 'kadan a tartare da ita, tace
"dallah malama sakeni, kin wani kamani kin ri'ke ko nayimaki satane, tafad'a tana wani hararta.
Wani guntun murmushi fadila tayi mai d'auke da takaici, ta kama hannun Auta ta kaita kan
kujera ta zaunar da ita, sannan itama ta zauna kusa da ita, ta kalleta tace "Yanzu Auta abinda
kakayimani kin kyauta, ki duba kiga yanda kika shiga tsakanina