Showing 45001 words to 48000 words out of 319356 words
Chapter 16 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
yi, "Hmmmm Saratu dama kin daina wahalar da yawun bakin ki, saboda a halin yanzu mahaifinku baida bakin magana, wannan kaɗai ya isa yasa ku gasgata magana ta..."
Ta faɗa tana kallon fuskar baba Obie dake fitar da gumin zufa, shatun jijiyoyin wuyansa sun fito ruɗu ruɗu, jikinshi ya ɗauki wani irin mahaukacin zafi.
"Duk wani jariri da matayenku suka haifa ya zo ba a raye ba sune suke ɗauke shi daga gare ku, da haɗin bakin munafukan likitocin asibitinsa, Ku tambayi munafuki MD Dr Jidanna, da Dr Adam da kuma Dr chisom, da sa hannunsu ake yi maku wannan aika aikar...."
"Zaku haifi ɗa ku ganshi a mace alhalin ba shi bane rufa ido su ke yi maku su yi musayar shi da aljani su ɗauke na gaskiyar su tafi da shi gidan kurkukun kaddara, ku kuma ku dauki aljanin ku yi jana'izarsa ku rufe a ƙabari da sunan jinjirinku ku ka rufe...." ta faɗa cike da takaici,
"Haƙiƙa Obie ya zalunce ku wlh wata shari'ar sai dai a lahira, amma fasiƙin mutumin nan ya daɗe yana aikata luwaɗi da zina da jikokinsa da ya sadaukar a gidan kurkukun kaddara, ya sha jininsu, ya kashe su saboda neman duniya, bashi kaɗai ba harda sauran fasiƙan da suke aikata fasadi a bayan ƙasa, Elders din suna da yawa sune miyagun dake sadaukar da jininsu matsayin fursinoni, da yawa ma ƴa'ƴan naku azaba ce ke kashe su, cikin ka so ɗari baifi ka so goma ne ya rage daga cikin su ba...."
Numfashinta ne ya fara tsaitsayawa, jini ya fara bleeding daga cikin hancinta hakan ba ƙaramin ɗaga hankalin Sharafudeen da Hateem ya yi ba..
Daurewa ta yi duk da azabar da ta ke ji a jikinta a haka ta cije ta ci gaba da cewa, "Na rantse da wanda raina ya ke a hannunshi duk abunda na faɗa maku ba ƙarya bane, idan baku yarda ba, gayanan agabanku ku turkeshi ya fada maku gaskiya...."
Tsayawa ta yi tana haki fuskarta ta jiƙe sharkaf da gumi, ta dafe saitin zuciyarta da tafin hannunta...
"Kamar yadda na faɗa maku, bashi kaɗai bane Elder, akwai muƙarrabansa da suke take masa baya, Amininsa Ifeanyichukwu inkiya Jan kunne amma a gidan kurkukun kaddara jan harshe shine nickname dinsa, shine Mataimakinsa a tare suke aikata fasadi, abun takaici sun auri junansu tun da daɗewa saboda tsantsagwaran jahilci da tumasanci...."
Kutumar U! Zaro idanu suka yi kamar ƙwayar zasu faɗo ƙasa, sun shiga matsanancin tashin hankali, maganarta ta ƙara dagula masu lissafi, jin abun suke kamar wasan kwaikwayo.
"Bayan haka, surukinku mijin Saratu, shine Jan kunne na gidan kurkukun ƙaddara..." Tunkan ta ƙarasa maganar hajiya Saratu ta daddafe kanta da tafukan hannayenta, ta dinga girgiza kanta, tsabar kiɗimar da ta yi ne yasa ta dinga sambatu kowace addu'a ta zo bakinta furta ta kawai ta ke yi..
Runtse idanunta ta yi ruɗu yama hana ta iya tantance me Khala take nufi, buɗe idanunta keda wuya Unexpected ta hango Pravin da ya arta a guje ya nufi sashen yan aikin gidan, aikuwa jikinta na 6ari tabi bayan shi...
Khala bata dakata ba, ta ci gaba da cewa, "Sir Benjamin baturen amuruka, abokin mahaifinku wanda suka yi tashen yawon duniyarsu atare da obie da amininsa, shine jan le6e na gidan kurkukun ƙaddara, mugun fasiƙi ne....."
"Bayan shi sai baƙin shaidanin da taƙadarancin sa yafi na fir'auna, zan iya cewa tun da Allah ya halicce ni ban ta6a ganin mugun bawa irinsa ba, bazan iya misalta mugayen zunubban da yake aikatawa ba, shine mai bada shawara kuma head na kula da bangaren bada horon giants ɗin kurkukun ƙaddara, baida imani ko misƙala zarratin, asalin shi bawan Obie ne daga baya da likafa ta ci gaba sai ya bashi muƙamin Elder...shish.. Shish.....
Kasa ƙarasawa ta yi saboda abun da ya sarƙe maƙoshinta, dama ba koshin lafiya ne da ita ba, jiri ne ya kwasheta a galabaice ta yanke jiki zata faɗi, cikin sauri Sharafudden ya sungumeta ya kwantar da ita akan doguwar kujera, sai kokarin ƙarasa maganar take yi amma ta kasa...
Wai shin Ina Chief Owais? bawan Allah Komai dake faruwa akan idanunsa kuma kunnuwansa na sauraro, kwata kwata baya acikin hayyacin shi, zufar dake tsastsafowa ta saman fatarsa ta jiƙe jikin shi sharkaf, kwata kwata ya gaza yarda da abunda Khala ta faɗa, Gani yake kamar mafarki yake yi ba gaske bane, duk da ya gama raunana zuciyarshi ta karaya da ganin yadda baba Obie ya yi shiru bai tanka ba! Hakan na nufin da gaske ne ba kazafi aka yi masa ba tun da ya kasa kare kan shi, inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un! La'haula wala quwata illa billah, da wannan ranar ƙwara mutuwarsa, addu'o'i yake ta nanatawa acikin zuciyar shi..
Jiki a mace Sir mubarak ya zauna kan Sofa, zafi ne ya taso mashi har ta kai ga ya tu6e rigar shi ya jefar da ita ƙasa, ya ɗaura gwiwar hannunsa akan hand sofa ya zagba uban tagumi, kamar wanda ya rasa gata a duniya.
"Deen! kana jin abun da nake ji kuwa? Deen Ka tsunƙule ni dan Allah inaso na tabbatar in ba mafarki nake yi ba..."
Cikin raunanniyar murya His excellency Abdul Razak ya faɗa yana kallon His excellency Deen da ya haɗa uban gumi a jikin shi, girgiza kai ya yi cikin karyayyar murya ya ce, "Ba mafarki bane, kada mu yaudari kanmu! Da gaske ne komai ke faruwa, baba da muke sa ran zai kare kansa daga ƙazafin da tsohuwar nan ta yi masa ya kasa, gashi nan yana ji ya yi shiru..." Ya faɗa yana nuna Obie..
Muryar Sharafuddeen ce ta katse shi da cewa, "Abun da momma ta faɗa akansa ba ƙarya bane, ya aikata ne shiyasa ya kasa kare kansa....."
"In kuwa hakan ya tabbata gaskiya ne, Baba ka kashe mana rayuwa, ka gama da mu, mun mutu, mun bani mun shiga Uku! Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un......"
Senate Lateef da ya ɗauko maganar bai kaita karshe ba Ya yanke jiki ya faɗi a sume, a firgice Deen da Abdul Razak suka rufa akan shi suna ambaton sunan shi haɗi da bubbuga jikin shi don ya tashi..
"Ruwa, tana buƙatar ruwa..."
Hateem ne ya yi maganar, cikin sauri Sharafuddeen ya je ya dauko bottle water me sanyi yana gab da zai ƙaraso Ya lura da Owais dake a tsaye baya motsi da alama suman tsaye ya yi, wuce shi yayi ya nufi Hateem ya miƙa masa robar ruwan Ya kar6a yatsun hannunsa na kerma ya kanga ma tsohuwa Khala a baki, kusan rabin ruwan ta shanye sam ta kasa magana idanunta ma sun rufe gam bata iya buɗe su.
Kar6ar robar Sharafuden ya yi daga hannun Hateem cike da rashin kuzari ya nufi su Deen Ya mika masu bayan sun yayyafa ma Senate Lateef ya farfado yana sambatu kamar mai tabin hankali har yana fadin Allah yasa mafarkine abunda ya ji.
Kar6ar robar ruwan ya yi daga hannun Deen ya je gaban Owais ya daddage ya watsa mashi ruwan a saman fuskar shi, lokaci ɗaya yaja dogon numfashi ya furzar da shi da wani irin zafi.
Kamar mahaukaci haka ya damƙi gaban rigar Sharafudeen hawaye na zarya akan kuncinsa da wata irin karyayyar murya ya ce,"Ka faɗa min kaima kana ɗaya daga cikinsu?"
Ya fahimci ba ya acikin hayyacinshi, tsigar jikinshi duk ta tashi haiƙam zuciya ta riga da ta tsinke.
Tsananin tausayin shine ya kama shi, Cikin sanyin murya ya ce, "Bana ɗaya daga cikin su Owais..."
"Meyasa ka kasa kare kanka lokacin dana tambayeka?"
Girgiza kanshi ya yi, "Saboda na daukarwa baba alƙawarin bazan faɗa ma kowa ba..." Katse shi ya yi, "Wani alƙawari ne ka daukar masa?"
"Shine ya kira ni a waya ya faɗamin zaku je kai farmaki gurin matsafa masu haɗarin gaske, ya gargade ni akan kada in kuskura in barka ka je, nace mashi ai yafi kusa da kai kafi jin ma maganarshi, me zai hana ya yi maka magana, sai ya ce min ba ya son bacin ranka ne yasan idan ya hana ka zuwa baza ka ji daɗi ba, shiyasa ya kasa amma yasan ni idan na yi maka magana bazaka ji komai ba, kawai in baka umarnin kada ka je, nace mashi baba ban ta6a hana Owais ya je kai farmaki ba, hasalima ni nake ƙarfafa masa gwiwa akan aikinsa idan na hana sa wannan karan dole zai ji ba daɗi ne, sai ya fara min faɗa yana fadin har shi zai bani umarni in ƙi bi! Yana magana ina magana, da ni da owais din duka ba a ƙarƙashin ikon shi muke ba? Na dinga bashi haƙuri har saida na amince zan yi maka magana tukunna ya haƙura, Sannan ya ce zai turo da ɗan saƙo da maganin bacci in saka maka a cikin Coffee, saboda in kasa kafiya ka turje akan ba zaka bi umarnina ba, sai in baka kasha coffee din, kuma baya son kasan shi ya sakani, nayi masa alkawarin bazan bari ka sani ba, kaji dalilin da yasa lokacin da na kira ka a resting home dina ka ƙi bani hadin kai ni kuma na baka coffeen dana zuba maganin baccin ka sha...."
Gaba ɗaya maganganun Sharafudden a cikin kunnuwansu sun ji komai, hankulansu sun ƙara tashi, cikin rawar murya Owais ya ce, "Kana nufin baba shine ya hanani kai farmaki, kuma shine ya sa ka bani maganin bacci, amma a daren ranar ina ka je saboda an faɗa min ba a gan ka ba?" Ya fada a ƙagare da son jin amsar shi..
"Owais ni ban je ko'ina ba, ina a villa, adakin mommynka na kwana zaka iya tambayarta ka ji, bayan haka sanin kowannanku ne Villa tana da tsaro, ba yadda za'a yi shugaban ƙasa ya yi fitar sirri in the midst of the night batare da wani daga cikin security ya bi shi ba, Allah shine shaida ta..." Ya fada fuskarsa a yamutse.
"Hakan na nufin Baba shine ya ƙulla maka makirci saboda ya ɗaura maka laifin sa? Ko don ya shiga tsakanina da kai?"
Jinjina kai Sharafudden ya yi,"Babu tantama Owais, baba shine Master planner ɗin da ke shirya maƙarƙashiya atsakaninmu, bansan meyasa ya yi hakan ba..."
Cikin shesshekar kuka ya ƙarashe maganar, wata irin juwa ce ta ɗibi Chief ya yi taga taga zai kife ƙasa cikin zafin nama Sharafudeen ya janyoshi ya rungume abunsa akan kirjinshi, atare suka fashe da matsanancin kuka tamkar ransu zai fita.
Haƙiƙa baba Obie ya muzanta, kunyar duniya ta kama shi, ya shiga matsananciyar damuwa, bai ta6a zaton wannan ranar zata zo ba, Wani irin azababben ƙunci da bakin ciki da takaici ne suka turnuke zuciyar shi, jin kanshi yake kamar ba mutun ba saboda tashin hankali.
A zabure ya miƙe kamar mahaukaci ya juya jikinsa na 6ari zai bar wurin sai dai kafin ya kai ga tafiya Owais ya hango shi, a zuciye ya 6an6are jikinsa daga na daddynsa ya nufi baba Obie cikin zafin nama ya damƙi damtsen hannunsa ya juyo da shi suka fuskanci juna gaba da gaba, kunya ta hana baba Obie ya haɗa ido da Owais saidai ya sadda kanshi ƙasa.
Cikin raunanniyar murya ya ce, "Baba kai kaɗai ne zaka share min shakku na, Ina so na ji daga bakin ka, da gaske kaine Elder na gidan kurkukun ƙaddara? Kuma kaine mutumin da ya fitar da ni daga fagen yaƙi ya jefa ni a daki uhum??"
Ya faɗa cike da fargaban amsar da zai bashi, wlh ya yi fatan ace zai iya kare kansa sai dai ya kasa saboda asirinsa ya riga da ya tonu.
Gaba ɗaya idanunsu na a kan fuskarshi amsar shi kawai suke jira su ji, batare da ya ɗago da idanunshi ya dube shi ba ya jinjina mashi kai alamar Eh, a lokaci ji ya yi kamar ya haƙa ƙasa ya binne kansa saboda baƙin cikin da ya ziyarci zuciyarshi, raɗaɗin da suka ji yafi na ƙunar wuta zafi..Ya Ilahi!
Zuciya ce ta ɗibi Owais baisan sa'adda ya ci kwalar rigarshi ba, da hannu biyu ya damƙe shi sosai jikinshi na 6ari.
Hakan ba ƙaramin karya zuciyar Obie ya yi ba, duk irin jarumtakar namiji hakan bai hana sun fashe da kuka ba kamar ƙananun yara, gaba ɗaya sautin koke kokensu ya cika falon, wasu suka dafe kawunansu da tafukan hannayensu saboda azabar radadin da zuciyarsu ke yi musu, wlh sun yi danasanin zuwansu duniya a lokacin, sun ji ɗaci a ransu, ranar ta zame masu mafi muni a rayuwarsu. Gaba daya suka kewaye shi suna tambayar shi don me zai yi musu haka? Meyasa ya ci amanarsu ya ha'ince su? Wannan wani irin neman duniya ne? Me yasa ya aikata musu hakan? Wlh Hankalinsu ya tashi matuƙa, duk sun fita hayyacin su, kuka kawai suke yi kamar ransu zai fita..
Hakan ba ƙaramin karya zuciyar Obie ya yi ba, bai ta6a danasanin irin rayuwar da ya daukarwa kansa ba irin yau, saboda Allah ya jarabce shi da masifar son ya'yan shi, Koda ya ke sadaukar da jikokin shi bai ta6a sadaukar da ya'yan shi ba.
daƙyar ya iya haɗiye baƙin cikin shi, da wata irin karyayyar murya ya furta, "INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJI'UN!!! Na shiga Uku! wlh na daɗe ina fargaban zuwan wannan ranar, dama nasan duk mun daran daɗewa asirina zai tonu ne sai dai ban ta6a zaton zai tonu ta wannan hanyar ba! Ranar da nake jin zullumi da fargaban zuwanta, ranar da nake jiye ma kaina tsoron zuwanta, ya zan yi da rayuwana? ya zan yi da rayuwarku? Nasan na cutar da rayuwarku cuta mafi muni, na zalunce ku, na kuma zalunci kaina, Amma koma dai menene bakin alƙalami ya riga da ya bushe, na riga dana tabka babban kuskure, ban kuma san da wasu kalmomi zan roƙe ku gafara ba, banma cancanci in nemi yafiya agurinku ba, wlh na muzanta, na tozarta, na ji kunyar haɗa idanuna da ku, kaicona!...."
Bai ƙarasa maganar ba ya fashe da kuka, hawaye suka wanke fuskar shi, mutumin da sun manta when last suka ga hawaye ya zuba daga cikin idanunsa saboda jarumtakarsa ashe tsantsagwaran matsafine, Yana kuka suna kuka an rasa me lallashin wani, daƙyar yake kallon fuskokinsu cike da jin nauyin abun kunyar da ya aikata musu.
"Nasan na biyewa son zuciya, amma wallahi ba laifina bane, Nima gado na yi, tun kakanninmu da iyayenmu na taso acikin matsafa, shine hanyar samunmu, na yaudare ku da musulunci amma ni ba musulmi bane, arne ne ni kamar yadda ta faɗa muku, tun da na taso rayuwata bansan mai kyau da mara kyau ba haka iyayena suka tarbiyantar da ni, duk abubuwan da suka faru son zuciya ne da son ɗaukaka, buri na in tara dukiya, in ɗaukaka in zama shahararre a duniya, ƴa'ƴana ma su ɗaukaka a idon duniya, wannan dalilinne yasa gaba ɗaya kuka ɗaukaka kowannanku na nema masa duniya kuma ya same ta..." Bai ƙare maganar ba HATEEM ya katse shi ta hanyar cakumar shi cikin tsananin tashin hankali ya furta, "Baba! Baba!! baba!!!...." Idanuwansu cikin na juna a marairaice yake kallon shi..
"Meyasa ka za6i ka ciyar da mu haram? Baba duk irin ƙaunar da muke yi maka, kullum burinmu mu kare maka mutuncinka sai gashi kai ka zubar mana da namu mutuncin, ɗaukakar daka sama mana ta tashi a banza wlh! Saboda da zarar mutane sun ji abunda kake aikatawa wlh mun zama abun gudu, za'a juya mana baya ne a tsangwamemu zamu zama abun ƙyama, makiya zasu samu damar cuzguna mana, Baba ka bar mana mummunan tabon da mutane zasu dinga cin zarafin mu da shi! Haba baba! Wlh ka bamu mamaki baba, wai mahaifinmu ne yake aikata munanan zunubban nan?" Ya faɗa yana haɗiyar yawu mai tsananin ɗaci cikin mutuwar jiki ya sake shi..
Sharafudeen ya ɗaura da cewa, "Baba yanzu ina amfanin irin wannan? Wace riba ka samu baba? Ina hankalinka yake? Tayaya ka bari shaidan da zuciya suka rinjaye ka? Kamanta da wata rana zaka mutu ka koma ga Allah, baba Idan ka nema mana duniya lahirarmu fa? Ya kake so mu yi baba? Muna alfahari da kai, kaine abun tunƙahon mu, kaine silar ɗaukakarmu ashe mun yaudari kanmu baba, A yau mutuncinka ya zube acikin idanunmu baka da sauran daraja baba, wlh da wannan bakin cikin daka ƙunsa mana da kashe mu ka yi kamar yadda ka saba kashe ya'yan mutane...!"
Kuka ne ya ci ƙarfinsa har ya kasa karasa maganar..
Baba Obie sai kuka yake yi babu ƙaƙƙautawa..
Senate Lateef ya ce, "Baba wace shafewar basira ce ta same ka? Ni abun da ya dauremin kai yadda har ka iya kashe mutun ka sha jinin shi, ka kuma lalata rayuwar yaran da basu ji ba basu gani ba, baba wa ya koya maka zaluncin nan? Har yanzu na gaza yarda kaine kake aikata hakan Baba, Tsawon shekara nawa kana aikata fasadi a doron ƙasa! Wallah baba da ace ka yi hakuri tun fil azal ka yi rayuwarka cikin talaucinka da sai ya fiye mana kwanciyar hankali, shi arziki da daukaka na Allah ne, sai wanda ya so yake bawa, watakil ma kana ɗaya daga cikin wadanda Allah ya tsaga da rabonsu kaine baka sani ba, ka biyewa son zuciyar ka baba, gayanan ka jefa rayuwarmu a halaka, bayan haka jin dadin duniya ƙalilan ne baba, gaba dayanmu mutuwa zamu yi, komai muka mallaka anan gidan duniya zamu barshi, lahiri itace dawwamammiya, wlh da wannan masifar daka jefa mu a ciki wlh gara ace mun taso rayuwarmu a matsayin musakai marasa gata a duniya da dai irin wannan rayuwar, baba yanzu da ka ɗaukakamu ya zaka yi da mu? sai da ka bari duniyar tasan da zamanmu ana yi mana kallon mutane masu daraja da ƙima, masu martaba a idon duniya, yanzu idan suka ji miyagun laifukan da kake aikatawa me kake tunanin zai biyo baya?" Ya jefa mashi tambayar yana kuka yana girgiza kai.
kafafunsa ne suka gaza ɗaukarsa ya zube kan gwiwowinsa, idanunsa sun rune jawur, kumatunsa sun yi jajir, duk ya faffasa labbansa da haƙoransa, gemunsa ya jiƙe sharkaf da ruwan hawayensa, Ko'ina na jikinsa zufa ce take tsattsafo masa kamar babu A.c a falon.
Wlh ya sadaƙas bai ta6a zaton zai ji kunyar zunubban da yake aikatawa ba sai yau da Khala ta fallasa asirin sa a gaban ya'yansa mafi soyuwa a gare shi.
Dukkan ilahirin jikinsa kerma ya ke yi, ga wani irin azababben zazzabi da