Showing 177001 words to 180000 words out of 319356 words
Chapter 60 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
gaba ɗaya, shiyasa ma muka shirya maku dinner, Please ku biyo mu mu je..." Kallon juna suka yi bakin su a buɗe da mamaki akan fuskokin su.
Basu yi ƙasa a gwiwa ba, suka bi bayan Chefs din, kaitsaye suka nufi garden din gidan.
Suna shiga suka fara yin arba da sparkling light din dake haskaka arean gurin, shimfiɗa aka yi masu ta alfarma, wata hadaddiyar carpet mai faɗi da laushi, daga saman ta kayan dinner ne..
Gaba daya farin Ciki ya hana su furta kalma, sai dai suka dinga bin Chief da kallo saboda sun san shine ya shirya komai don ya faranta masu.
"Chefs sun faɗa min tun safe baku ci komai ba, shiyasa na umarce su da su shirya maku dinner, tun da yanzu mun samu kwanciyar hankali, nasan akwai yunwa a tare da ku, Pls ku zauna ku ci..."
sun nuna farin cikinsu sun kuma yi mashi godiya, a zagaye da dinner din suka zazzauna.
Kowan nan su ya fara ɗaukar abunda ya ke son ci, a baki Ummi da Shureim suke ba Batool ta na ci, itama saita ɗebo ta sanya ma kowannansu a baki, sheikh Imam dake kallonsu ya rasa ina zaisa ranshi don farin ciki, Benazir ma a baki ta dinga ba Unaisah tana ci.
"Sir, kai ba zaka ci bane?" Aneelerh ce ta tambaya tana duban Owais da ya yi tsaye yana ɗan daddana wayarsa.
Da fara'a akan fuskarsa ya dago ya dubeta, kafin ya bata amsa wayarsa ta yi ringing, ganin kiran daga CSH ne yasa shi saurin ɗagawa yasan kira ne me muhimman ci.
Ji suka yi ya furta, "Alhamdulillah, Alhamdulillah! Meyasa tun da suka farfaɗo baku kira kun sanar da ni bane?"
"Okay, pls karku barshi ya taho, ku ruƙe min shi, nasan shi da kafiyar tsiya.." Ya fada yana dariya.
Bayan ya yi rejecting call din ya dube su, "Kira ne daga Combat Support Hospital, Omar da Salsalbeel sun farfado daga coma, sun samu lafiya tun jiya da daddare..
Hada baki suka yi gurin furta Alhamdulillah..
Juyawa ya yi da sauri ya nufi hanyar komawa parking space, yana 6ullowa ta gaba ya hango Security Officers sunyi gungu guda suna magana baisan me suke tattaunawa ba.
Nufar su yayi da ɗan saurin shi, suna ganin shi suka dare, a rude yake kallon yaran da yake ta ajiya a part ɗin Taj, daga kallon da yake yi masu yasa duk suka sha jinin jikin su.
"Tayaya akai kuka buɗe kofar kuka fito?" Tambayar da ya fara jefa masu kenan,
Da sauri suka nuna Sajeed da yatsan su, "Wallahi babu ruwanmu, Sajeed ne ya ƙulla mana igiya ta baya, da ita muka kama muka sauko ƙasa"
Abun da ya faru bayan da mazan suka gudo, suna ƙarasowa gaban kofar shiga falon Chief security Officers suka ritsa da su, suka fara tambayarsu daga ina suke? Waya buɗe masu kofa suka fito.
Suka yi shiru basu amsa masu ba, kwatsam suka jiyo takun tafiya suna juyawa suka hango ƴan matan dake 6ullowa ta bayan sashen Taj ɗayan bayan ɗaya, hankalin Officers din ya ɗan tashi a rude suke kallon su har suka ƙaraso, mazan na ganinsu suka ɗaura hannayensu a saman kansu alamar sun shiga uku, saboda rashin gaskiya sai suka rufe matan da faɗa akan don me za su biyo su.
Aikuwa Parveen ta tona masu asirin ta yadda suka samu hanyar fitowa daga part din Taj, ran officers din ya 6aci suka rufe su da faɗa kamar za su buge su, duk sun tsoratar da su.
Suna tsaka da korawa chief bayanin abun da ke faruwa suka jiyo ihu daga can nesa da su.
Gaban kowan nan su ne ya fadi, a ruɗe Sarah ta ce, "Mun shiga Uku, Azeeza ce, wallahi ita ce, Kuma bata gani sosai idan dare ya yi, kada ta faɗo ta ji rauni..."
bata ƙarashe maganar ba, da gudu suka dunguma izuwa bayan sashen, tunkan su isa suka hango Azeeza da ta maƙale a igiya jikinta nata kerma.
Ga Jemimah ta biyo bayanta, ba dan Allah Ya sa sun ji ihun su sun zo ba da tuni sun salwanta saboda igiyar tana gab da kwancewa.
Cikin zafin nama Chief Owais ya taimaka masu suka ƙarasa saukowa.
Ransa a matukar bace ya rufe su da fada ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, abun da ya 6ata masa rai, igiyar da suka ƙulla yanzu da ta kwance sa'ilin da suke hawa ko ta subuce ma wanin su har rai zasu iya rasawa.
Kuka suka kama yi mashi suna bashi hakuri, bai sauraresu ba, ya damƙi damtsen hannun Sajeed ya wurga ma Officers shi ya ce "Ku sanya min shi a boot din mota dina, ba abun da zai hana in hukunta ka, saboda ka yi yunkuri aikata kisan kai.."
gaban Sajeed ne ya fadi rass! A tsorace ya dinga masa magiya yana fadin ya tuba bazai ƙara ba, ƴan uwansa ma suka dinga kuka suna rokon Chief ya yafe masa kada ya hukunta shi.
Bai saurare su ba, akan idon su Officers suka ciccibi Sajeed dake ta turjewa, su kansu sun yi mamakin ƙarfin shi, da kyar suka ɗaga shi sama suka nufi parking space, ƴan uwanshi suka bisu a guje, kafin ma su karaso tuni Officers sun jefa shi cikin boot din motar Chief suka kulle shi.
Bayin Allah ba yadda suka iya, dole suka haƙura, basu ta6a ganin fushin Chief irin na yau ba.
Ko da suka matsa mashi akan ya yi hakuri ya yafe ma Sajeed, nuna su ya yi da yatsa ya ce duk wanda ya kuskura ya ƙara ko da tari ne sai ya sanya shi a boot an tafi da shi, da jin hakan nan fa kowan nan su ya shiga taitayin shi.
Kafin tafiyar shi saida ya mayar da su part din Taj ya kuma kulle su.
A saman floor suka zazzauna suna ta kuka, sautin koke koken da suke yi ne ya farkar da Danejo da Deeja, kusan a tare suka fito daga dakunansu suka nufo su.
Hankalin Danejo ya tashi da ganin halin da suke a ciki, da damuwa akan fuskarta ta tambaye su meya faru? Meyasa suke kuka?
Dakyar ta samu suka labarta mata abun da ya faru.
Ta ce Allah shi ƙara in ma da ƙari ya kara, Chief ya yi daidai da ya tafi da Sajeed saboda baya jin magana, dama ta na lura da take takensa na son guduwa daga part din.
Cikin shesshekar kuka su ka ce in bazata lallashe su ba, ta yi shiru ta barsu da abun da ke damunsu.
Tana murmushi ta ce ai basu ga komai ba, su jira Chief ya gama hukunta Sajeed zai dawo kansu ne, saboda suma sun bada gudummuwa gurin aikata laifin.
wani sabon kukan suka fashe da shi jin abun da ta ce.
Deeja da ke sauraron su kuwa bushewa ta yi da dariya hada dafe cikin ta, tana fadin, "Allah ya ƙara maku, masu kunnan ƙashi, maganinku kenan. Ni dai Allah ya so babu ruwana, bansan anyi ba."
Ta ƙarashe maganar tana yi masu gwalo, haushin ta duk ya cika su kamar su rufe ta da bugu.
Daga bisani Danejo ta soma lallashin su ta ce su yi hakuri ita wasa ta ke yi masu tasan shima Sajeed din ba lallai ya hukunta shi ba.
~________________________________💫~
CSH (Combat Support Hospital)
Katafaren Military Hospital ne masu jinyar majinyatan sojojin da suka samu rauni a gurin yaƙi, asibitin ba a cikin garin Abuja ya ke ba, a kusa da sansanin su yake.
Yana da matuƙar tsaro, cikin shi da wajen shi soldiers ne ke tsaron shi, ga na'urorin dake sanya ido ga duk wani mai motsi ciki da wajen asibitin.
Lokacin da Motar Chief Owais ta ƙaraso cikin asibitin, drivern dake driving nasa yana yin parking sojoji suka bude mashi motar ya fito, a hanzarce suka buga ƙafa tare da sarah ma shi.
Zagayawa ya yi ta bayan motar ya buɗe boot dinta, lokacin da ya ɗaura idanunsa akan Sajeed da ya duƙunƙune a ciki kamar musaki saida ya ji tausayin shi ya kama shi, ganin yadda idanunsa suka yi jawur saboda kukan da ya sha.
Ruƙo hannunsa ya yi tare da taimaka mashi ya fito daga motar, koda ya ga sojoji ta ko'ina suna sintiri ruke da bindigu a hannunsu sai ya kuma fashewa da wani kukan yana roƙon chief ya yafe masa kada ya hukunta shi bazai ƙara ba, ya taimaka ya maida sa gurin ƴan uwansa.
Wani baƙin soja mummuna mara fara'a dake tsaye a gaban su ya ce, "Sir wannan ɗan shilan fa? Karairaya maka shi kake so mu yi ko tsallan kwadi zamu sanya shi?" Da jin wannan maganar, yasa jikin Sajeed ya kama kerma kamar mazari, a tsorace ya la6e bayan Chief Owais ya rurruƙesa yana roƙonsa, dariya sosai sojojin suka yi.
Da yasan yadda Chief ke ƙaunarsu da bai ɗaga hankalinsa ba, ko sauro baison ya ta6a lafiyarsu balle shi ya hukunta su da hannun shi never.
Ruko hannunsa ya yi suka nufi cikin asibitin yana ta zare idanunsa cike da zullumin Ina Chief Owais zai kai shi.
Duk inda suka gifta military doctors din dake zarya tare da nurses with respect suke sara mashi tare da gaishe da su..
Sajeed dake ta ƴan kalle kalle idanunsa suka dinga hango masa patient din dake a ɗakunan da aka kwantar da su, ta glass din jikin ƙofofin yake hangosu, wasu ma sai yawon su suke yi a ciki, ƴan matasan mata da samari irin shi.
A gaban wani medical room suka tsaya da tafiya, wani doc ne ya fito da fara'arsa ya sara ma chief shima ya sara masa bayan sun gaisa.
D.r din har ya buɗe baki zai yi magana ya katse shi tare da kashe mashi ido ɗaya sannan ya nuna masa Sajeed.
"Me laifi ne! Baya jin magana, ina so ka shiga da shi cikin dakin, ku cire masa kunnansa daya, sannan ku yanke harshen sa.."
Sajeed ya fasa ƙara yana fadin, "Nashiga uku, wayyo Inna lillahi! Yaya Owais na tuba bazan kara ba, na roƙe ka dan Allah ka yi hakuri, ka yafe min, wlh mutuwa zan yi idan suka cire min harshe na.."
a gigice ya zu6e kan gwiwowinsa ya rurruke kafafun Owais, ya dinga rokonsa yana kuka..
Murtuke fuska Owais ya yi, "Ku yi abun da na ce! Kar ku saurare shi." Rushewa ya yi da wani kukan,
Docs din suka ce, "An gama sir,"
Da ya ga dagaske suke, jikinsa na bari ya mike tare da watsawa da gudu, sai dai kafin ya fuce, sojojin dake sintiri suka cafkoshi suka dawo da shi gaban Chief Owais, Docs din suka rurruke shi yana turjewa tare da waiwayen Owais da ya kawar da kansa gefe, docs din suka tura shi cikin dakin..
"Ku sake ni, ku kyale ni in tafi, wallahi kada ku ta6a ni.." Bai ƙarasa maganar ba, sakamakon abun da idanunsa suka nuna mashi wanda yake ganin kamar ba gaskiya ba ne..
Tana a kwance kan medical bed sanye da patient gown, sai sharar baccinta take yi, daga kan table din gefenta kayan marmarine a cikin plate data fara sha ta rage sauran.
Murza idanunsa ya yi da hannayensa don ya ga ko gizau take yi mashi amma still ita ya gani.
Gaba ɗaya ya ruɗe ya rasa gasgata abun da yake gani.
"Kamar twin sister dina? Ni kaɗai nake ganinta! Ko mafarki ne..?" Fusge kanshi ya yi daga hannun docs din a rude ya nufi gadon ya ɗan zauna daga gefe ya ƙura idanunshi akan fuskarta.
Jini ɗaya ba wasa ba, ko a mafarki ya ganta zai shaidata, duk min canzawar da za ta yi, saboda warinsa ce.
A hankali ya ɗaura yatsunsa dake kerma saman fuskarta, ya ɗan shafa ta har izuwa kan curly hair ɗinta, komai nasu iri ɗaya, jinsi ne kaɗai ya bambanta su.
Muryarsa na rawa ya furta, " GAB.. riella! Da gaske ke ce? Ke nake gani? Ba mafarki nake ba.?"
Sambatunsa ne suka katse mata baccinta, a hankali ta buɗe idanunta, tana ɗaura su kanshi ta zabura ta miƙe zaune, wani irin tsantsar farin ciki ne ya bayyana akan fuskokinsu.
"My twin Bro! Kai ne da gaske nake gani a gabana? Ashe da rabon zamu gana da juna, na yi zaton bazan ƙara ganinka a rayuwana ba.."
wata irin ruguma suka yi wa junansu kamar zasu koma mutun daya, a lokaci ɗaya suka fashe da kukan farin ciki.
"Kasan irin uƙubar dana sha? Baka ta6a nemana ba, Ka manta da ni! Ba ka damu ina a raye kona mutu ba, ni kadai nake hauka na akan ka, ganin ka da na yi ya tabbatar min da ka riga ni barin kurkukun ƙaddara.."
cikin kunci ta furta tana kallon shi.
Duk sai ya ji ba dadi, cikin karyayyar murya ya ce, "Ba haka bane, kina a raina, na damu da ke, kamar yadda kike nema na nima haka nake neman ki, ki yi hakuri nasan ban kyauta maki ba, ba yadda zan yi ne..."
Bai ƙare maganar ba ta daka mashi tsawa, "Ƙarya kake yi Gabriel, na tsani kaina dana damu da kai. Dama na sani na kashe kaina tuntuni, kalli yadda ka sauya kana cikin kwanciyar hankali, ni ina a can cikin azabar rayuwa, ban taba mantawa da kai ba, in ni ce wallahi bazan iya barin ka ba, koda zan rasa raina ne .."
Kasa ƙarasa maganar ta yi saboda bakin cikin da ta ji, jikinshi duk ya yi sanyi zuciyarshi ta karaya, yasan sister din nashi da zuciya, sai anyi da gaske zata sauko daga kan dokin zuciya..
"Dan Allah ki daina kuka zanyi maki bayani.." Bai ƙare maganar ba ta rufe shi da bugu kamar ta samu jaki, ta dunkule hannu ta shiga kai mashi naushi.
saboda yasan bai kyauta mata ba yasa shi kasa dakatar da ita.
Komai dake faruwa akan idanun Chief Owais da Docs din dake a ɗakin, tsantsar tausayin su ne ya kama su.
"Gabriellah, ki daina bugunsa, i will explain to you.. "
Owais ne ya faɗa, cikin shesshekar kuka ta ce, "Ka barni in ci ubansa, baisona banza shasha, wa nake da shi in bashi ba? Ni fa ƙanwarsa ce, twin sister ɗinsa, ciki ɗaya muka fito, don me zai barni cikin wahala ya tafi? Kunsan irin cin zarafin da aka yi min? Wannan mahaukaciyar karyar ta sa giant ya yi raping ɗina, ni kaɗai nasan azabar dana sha, mutuwa kadai ne ban yi ba..."
gaba ɗaya ta labarta musu abun da ya faru da ita, Gabriel ya yi kukan bakin ciki kamar ransa zai fita.
Docs din dake a dakin duk saida idanunsu suka ciko da ƙwalla saboda tausayinta.
Chief Owais ya karaya da jin abun da ya faru da ita.
Haɗuwa suka yi su duka suka dinga lallashinta har saida suka samu ta tsagaita da kuka.
Chief Owais ya ce ta yi hakuri, sun san an cutar da rayuwarta amma ta sani Gabriel bada son ranshi ya tafi ya barta ba, bashi da mafita ne saboda ba a guri ɗaya suke ba, bayan haka sune silar da har suka san labarin kurkukun ƙaddara, da labarin ita kanta, saboda Sajeed shine ya dinga yi masa maganar ƴar uwarsa dake a kurkukun kaddara akan ya taimaka ya ɗaukko ma shi ita, bayan haka mahaukaciyar karyar da take magana akanta ta riga da ta mutu tun ranar da suka kai farmaki!
Maganganun Chief Owais sun yi tasiri a cikin zuciyarta, jikinta ya yi sanyi har ta nemi yafiyar Gabriel akan faɗan da ta yi masa ya ce mata kada ta damu komai ta yi shi baiga laifinta ba, shi yakamata ya nemi yafiyarta, ta ce ta yafe masa amma kar ya ƙara tafiya ya barta, ya yi murmushi ya ce bazai ƙara maimaita wannan kuskuran ba, hugging din juna suka ƙara yi cike da farinciki.
Daga bisani Sajeed ya dubi Chief Owais da hawaye akan fuskarsa ya ce shi baisan tayaya zai gode masa ba, yau ya shammace shi, ya yi mashi surprise din da bai ta6a zato ba, da farko ya yi zaton hukunta shi zai yi, ashe yar uwarsa zai nuna masa, ya ce, " Chief kai wani irin mutunne mai kyakkyawar zuciya? Na yi imanin zuciyarka ta daban ce, samun irin ka zai yi wuya a duniyar nan. Ka kyautata mana a rayuwa, ka yi mana abun da baza mu ta6a mantawa da kai ba, Allah ne kadai zai iya biyan ka..."
Yayin da Sajeed ke furta masa kalmomin nan murmushi ne dauke akan fuskarsa.
Itama Gabriella ta yi masa godiya, ya ce su godewa Allah, saboda shine ya kaddara zai zama silar taimakon su.
Da sauri Sajeed ya sauko daga kan gadon ya yi sujjada don godiya ga Allah, da ya ga shiru Gabreilla bata sauko ta yi ba, ya miƙe ya ruko hannunta ya ce ta zo suyi sujjada su gode ma Allah, a rude ta ce, "Bansan me kake nufi ba, bazan yi sujjada ba, ni ba musulma bane, ko ka manta?".
"Har kina da za6in addini a yanzu? baki ga wadanda suka taimake mu musulmai bane! Nima yanzu musulmi ne, Ki daina kira na Gabriel, bana so sunana Sajeed, kema na musuluntar dake, sunanki Sajeeda daga yanzu."
maganar shi taba su nishadi.
A nan take ya biya mata shahada ta musulunta ya kuma raɗa mata suna SAJEEDA, dama tuntuni ya ke ta tanadin sunan da zai sanya mata kalar na shi idan Allah ya haɗa su, bayan da ya samu sai ya adana sa a cikin zuciyarsa.
Chief ya ce su jira shi zai shiga cikin asibitin gurin su Omar, suka amsa mashi da toh.
Bayan fitarsu daga dakin ya rage saura su biyu.
Sai dadi suke ji kamar yau suka fara sanin juna.
Ta tambayeshi ya bata labarin ta yadda suka ku6uta daga kurkukun ƙaddara kuma a ina yake da zama?
Bayan da ya labarta mata, ta ji dadi sosai har ta ƙosa ta ga sauran prisoners ɗin da yake a tare da su, sai ta ji dama tun farkon kai su kurkukun ba a raba masu ɗaki ba, saboda ta ji sun fi su samun gata ba kamar su ba da aka maida dabbobi.
"Ina son nasan meya faru da khala, itama ta ku6uta ko bata ku6uta ba, na ga babu ita cikin wadanda sojoji suka ceto, ina son ta, itama tana sona, ba don ita ba da yanzu babu ni..."
Ta fada idanunta cike da ƙwalla.
"Ban so wani abu ya sameta, ina so ta rayu saboda in taimaka mata, ta faɗamin bata da kowa, itama cutar ta aka