Showing 48001 words to 51000 words out of 319356 words
Chapter 17 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
ya lulllu6esa, mutumin da sai ya yi shekara da shekaru bai yi ciwo ba saboda ƙoshin lafiyar dake gare shi to yau dai hada matsanancin ciwon kai, bazama a raza ciwon zuciya na farat daya ba saboda depression din da ya kama shi, gaba ɗaya suka zauna kewaye da shi kamar malami da almajiransa kuka hada majina, sun kasa tsayar da kan su. 😭
Daƙyar ya iya furta, "Idan na ce ku yi hakuri ban yi maku adalci ba, iya cutarwa na cutar da rayuwarku, ban cancanta na ci gaba da rayuwa ba, nasan a halin yanzu da kuka gano wanene ni kun tsane ni fiye da komai na duniyar nan, don haka na miƙa wuyana a gare ku, nasan na aikata maku ba dai dai ba, Ku yanke mini duk wani hukunci da kuka ga ya dace dani, ku azabtar da ni, sannan ku kashe ni, idan ba haka ba, Ni zan kashe kaina, saboda bazan iya cigaba da rayuwa da abun kunyar da na aikata muku ba..." Yana faɗa yana kuka haɗi da tari.
Sama sama khala dake a kwance kan Sofa take jiyo maganganunsu, baiwar Allah ita kadai tasan halin da take a ciki, ta tona masa asiri burinta ya cika sai dai bata yi farin ciki ba, saboda halin da ya'yan shi suka shiga shiyasa kafin ka fara aikata wani abu mara kyau ka fara tunanin makomarka da kuma halin da zaka jefa wanda ya yarda da kai abun yana da ciwo.
"Ku kashe ni, in har baku kashe ni ba mutane bazasu ƙyale ni ba, ku kashe ni kawai nafi so na mutu a hannunku, ko dan saboda ku dauki fansar abun dana aikata maku, ku kashe ni na ce, in ba haka ba zan kashe kaina..."
Zumbur ya miƙe jikinshi na kerma, Lokaci daya gabansu ya fadi ganin jinin da ya wanke gaban wandon shi.
Har suna haɗa baki gurin ambaton sunanshi, Allah sarki duk da abun da ya aikata hakan bai hana su ɗaga hankalinsu a kanshi ba,
"Mu kai shi asibiti kada ya rasa ranshi!" Sharafuddeen ne ya yi maganar a ruɗe.
Har sai da baba Obie ya dube shi da raunatattun idanunsa, ƙasa ƙasa da murya ya ce, "Duk abunda na yi maka baisa ka daina damuwa da ni ba Sharafuddeen....?" Girgiza kai ya yi, "Ku yi hakuri bazan je asibiti ba, ku barni a gida, in ma mutuwace ta riske ni a cikin ku...." Yana ƙarasa maganar ya shallake su ya juya a hanzarce ya nufi part ɗinsa, da gudu suka bi bayanshi kafin su ƙaraso tuni ya shige ɗakin ya ja ƙofa ya datseta ta yadda ba zasu iya buɗeta ba. 😭
Yanke jiki ya yi ya faɗi kan floor ya dinga birgima yana bubbuga goshinsa kan floor har saida ya fashe jini ya 6alle masa, daga waje suna juyo kururuwar azabar da yake fitarwa mai kuwar gaske kamar zai fasa dodon kunnuwansu.
Da iya ƙarfinsu na karshe suka dinga bubbuga ƙofar hadi da ambaton sunan shi da karfi.
Chief kamar zai 6alle ƙofar da kafaɗarsa ya dinga bangazarta duk da raɗadin da ya ke ji.
"Baba ka buɗe mana ƙofa, bamu gama magana da kai ba, baba kada ka mutu kabar mu, baba dan Allah ka buɗe bamu gaji da ganin ka ba, akwai tambayoyin da baka bamu amsoshinsu ba, baba! baba!!, zamu iya yafe maka amma ka buɗe mana kofar, baba pls, baba pls, idan ka tafi ka barmu a cikin wannan mawuyacin halin daka jefa mu ya kake so mu yi da rayuwarmu! Ka taimaka mana baba, ka fitar damu baba.. "
Ba irin bugun da ba su yi ma kofar ba amma ta ƙi 6allewa, a karshe da suka galabaita a gaban kofar ɗakin nashi suka zazzauna suna cigaba da yin kuka kamar masu zaman makoki.
Gaba ɗaya abun da ke faruwa ƴan aikin gidan basu sani ba, saboda anyi masu iyaka da shiga falon dama ƙa'ida idan za'ayi family meeting ba'a buƙatar bare agurin shiyasa kwata kwata basu leƙo ba kuma basu ji sautin koke koken da ake yi ba, saboda akwai tazara tsakanin sashen su da main falo.
_____________________PRAVIN 🥵
Tun lokacin da khala ta fara fallasa asirin su, cikin rawar jiki ya bar falon batare da sanin kowan nan su ba, bai nufi ko'ina ba sai sashen yan aikin gidan.
A lokacin Hajjaty tana a ƙudundune cikin bargo har ta samu bacci ya ɗan dauke ta, kwatsam ba zato ba tsammani kamar daga sama ta ji an cakumeta, ta fasa ƙara tana kokarin kwache kanta cikin ruɗu da tashin hankali, kwata kwata batasan wanene ba saboda bargon da ya lullu6e fuskarta, a saman kafaɗarshi ya sa6e ta, tana kuka tana ihu tare da ambaton sunan pravin don ya kawo mata ɗauki, juyawar da zai yi keda wuya ya yi arba da hajiya Saratu dake shugowa ɗakin afujajan nan take gabanshi ya yanke ya faɗi ya zazzare idanunshi yana kallon ta kamar yadda take kallonshi da tsantsar tashin hankali akan fuskarta..
Numfashinta na fita da hucin bacin rai ta ce,"Munafiki, Gidan ubanwa zaka kai ta eye? Yan iska maciya amana, wato Kun daɗe kuna cin amanata, yanzu da ka ga asirinka ya tonu shine ka lalla6o ka saci jiki ka shugo don ka dauki kwartuwarka don ku gudu ko?" Ta faɗa tana zare idanunta.
Tsawa ya daka mata har saida ta razana, muryarsa na rawa ya ce, "Ki matsa ki bani wuri in wuce tunkafin in yi maki illah!"
Cikin fusatacciyar murya ta ce, "Illah kuma ta nawa? Ka bani mamaki pravin, Ka karya min zuciyata, munafuki dama na daɗe ina zargin Hajjaty ashe tare kuke aikata fasiƙanci, wai a haka na aure ka na haifa maka ƴa'ƴa, Ka cutar da rayuwata pravin, hakkina da na ya'yanka bazai ta6a bari ka gama da duniya lafiya ba wlh, kuma na rantse babu gidan ubanda zaku je, mayaudaran banza, dole ku gurbi abun da kuka shuka..."
Bata ƙarasa maganar ba, sakamakon naushin da ya sakar mata akan kuncinta, nan take gefen bakinta ya fashe ta fara bleeding, azabar zafin da ta ji ne yasa ta dafe gefen bakin, da mamaki ta furta,"Pravin! yau da hannunka ka dake ni? Inna lillahi..! " Rai a 6ace ta yi kukan kura ta haɗa su duka biyun da shi da Hajjaty ta hankaɗa su gaba ɗaya suka kife ƙasa, bargon jikin Hajjaty ya warware baiwar Allah tuni ta jima da sumewa sakamakon buguwar da kanta yayi dama ya lafiyar gwiwa.
Ransa ya 6aci matuƙa, a harzuƙe ya yunƙura ya mike Ya nufi hajiya Saratu batai aune ba, ya damƙi ƙeyarta da hannunshi ya jata ta karfi ya nufi mirror tana ta kokarin ta kwace kanta sai dai ta kasa saboda raunin da zuciyarta ta yi yasa ta kasa ta6uka komai.
Yana isa gaban madubin ya buga kanta jikin shi nan take madubin ya fashe, duk ya sossoke fuskarta, tuni ta fara bleeding, kukan ma ta kasa yi saboda zogin azabar da ya ratsa sassan jikin ta, ya ɗago da kan nata ya wurgar da da ita a galabaice ta kife kan floor ta mirgina numfashinta yana ta kokawar ɗaukewa.
Hakan bai masa ba sai da ya take yatsun hannayen ta da tafin ƙafarsa duk ya murjesu suka faffashe jini ya soma tsastsafowa.
kwata kwata babu imani a zuciyarsa, ga idanun nan nasa sun kaɗa jawur kamar an watsa barkono a cikin su, Ya na huci ya furta, "Allah ya isa tsakanina da ku, Dangin matsafa masu arziƙin jini, Duk ubanku ne ya ja min shiga halin da nake a ciki, shine mugun da ya sa na jefa rayuwata cikin halaka ina zaman zamana lafiya, dama ni ban ta6a son ki ba, dukiyarki ce tasa na aureki da kuma kwaɗayin surar jikin ki, Kin daɗe kina baƙanta min rai ke ga mai arziki ɗiyar ƙaruna, ki yi ta min gorin arziƙi don ina zaune a gidan ku, to ai ga irinta nan, yanzu ai kin gane arzikin naku bana halal bane ko? Ya faɗa yana tottafa mata yawu a kan fuskarta.
"Kuɗin jini ne kuke tunƙaho da su, wlh badan ƴa'yan dake tsakanina dake ba da ba abun da zai hana in huce haushina a kanki, zan bar ki da ranki ne ba don na so ba.."
Ya faɗa yana kallon fuskarta da ta jiƙe sharkaf da jini kamanninta har sun sauya saboda azaba ta gama fita hayyacinta, juyawa ya yi da sauri ya nufi bargon Hajjaty ya janyo shi ya rufa mata a jikinta tare da nannaɗeta a cikin bargon ya mayar da ita kan kafaɗarsa, Ya tsallake hajiya Saratu dake a kwance rai hannun Allah cikin sauri ya fuce daga ɗakin, batare da sanin kowa ba ya gudu daga Estate ɗin......💔
___________________________________✍️
*_(SHIN ME KUKE TUNANIN ZAI BIYO BAYA IDAN SAURAN AHLIN FAMILYN SUKA KARASO SUKA JI ABUN DA KE FARUWA❓GA HAJIYA SARATU AKWANCE RAI HANNUN ALLAH! WA ZAI KAI MATA DAUKI❓ YA RAYUWAR BABA OBIE ZATA KAYA ZAI KASHE KANSHI NE KO KUWA❓ ME KUKE TUNANIN ZAI BIYO BAYA IDAN SAURAN ELDERS SUKA JI LABARIN ASIRIN ELDER YA TONU❓YA LABARIN PRAVIN DAYA GUDU DA HAJJATY GIDAN UBAN WA ZAIJE❓ DA WANI IDO YA'YAN BABA OBIE ZASU FUSKANCI DUNIYA? KUNA TUNANIN BA ZASU FUSKANCI KALUBALE BA AKAN MUKAMAN SU❓ TAYA ZA'A HADA KOWANI PRISONERS DA IYAYENSA❓ TAYA ZA'A KAMA SAURAN ELDER❓ TO WAINI TAYAYA MA AKAI TSOHUWA KHALA TA RAYU?😳 YANZU NE LOKACIN DA ZAKU ƊAURA ƊAMARARKU TAMAU DON JIN YADDA ZATA KAYA🔥💪_*
*Gani ga wane Ya ishi wane Jin tsoron Allah😭 page din nan ya taba zuciyata)*
*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE🔥🔥🔥🔥😭*
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*~___________________________________🌹💋🫀☠️💗🔥✍️~
Ɗayan bayan ɗaya suka soma shigowa cikin main falo, twins ne a gaba daga bayan su Captain Yaseer ne sanye cikin pilot suit dinsa da bai kai ga cirewa ba, bai jima da ƙarasowa ƙasar ba, su twins ne suka je ɗauko shi a airpot.
Justice Nadeem da Ziyad sun saka shi a tsakiyar su, shigar su keda wuya saiga Mommy Turai tare da Jazz sun shigo suma, fuskokinsu da fara'a, a mutunce suke gaisawa da junansu, hayaniyar hirar da suke yi ce ta cika falon yayin da suke tafiya atsanake suna tunkarar interior din sa.
"Mommy Zaki bai zo bane?" Ziyad ne ya tambaya yana kallon Turai, ta ce, "Bai zo ba wlh, daddynsa ya faɗa mun sunyi waya yace bazai samu damar halarta ba saboda ayyuka da su ka yi mashi yawa, amma yace a kira shi video call idan aka fara don ya samu jin abun da za a tattauna..."
Ziyad ya ce, "Na so ace ya zo wlh, munyi missing nashi, amma bakomai zamu yi magana idan an kira shi video call din.."
Turai ta ce, "Ai wannan karon naga bakowa ya samu damar halarta ba, kowa ya shiga busy, wasu suna school wasu kuma aiki ne ya ruƙe su.."
"Mutumina ya gajiyar aiki? Na ga ko kakin baka samu ka cire ba.." Justice ne ya faɗa yana dafa kafaɗar Yaseer, yamutsa fuska ya yi tamkar baison furta maganar ya ce, "Alhamdulillah, bana so a fara meeting din batare dani ba, bayan haka na yi missing naku sosai, bazan iya jure rashin ganin ku ba, tun da jirginmu ya yi landing nake ta zumudin in ƙaraso don inga yan uwana..." Murmushi suka saki, gaba ɗayan su sun ji dadin maganar shi.
Zayn ya ce, "Muma mun yi kewarka Bro, kuma mun yi murnar ganinka..." Sumar kan Zayn ya shafa da yatsunsa da zolaya ya ce, "Nima na yi kewarku, dangin lord shiva, ay na ga yau indiyancin ne ya motsa, kun yi gayu abun ku" Dariya suka saki.
Zaid Ya ce, "Aikin daddy ne, shine ya matsa mana sai mun saka kayan india..." Jazz dake sauraronsu murmushi ne dauke akan fuskar shi, yana jin dadin yadda suke fira da junan su burge shi su ke yi, ba halin ya saka musu baki saboda shakkar Captain Yaseer ya ke ji, Ya tsani bare yana da girman kai sosai, haka zalika Zayn halin shi kusan ɗaya dana Yaseer bambancin su kaɗan ne.
Lokaci ɗaya suka Ci burki ganin babu kowa A falon, ko gifcin mutun babu, kallon juna suka yi..Justice ya ce,"Bangane ba! Ina mutanan gidan nan ne? Ba dai har sun kammala meeting din ba?" Ya faɗa a ɗan rude.
Captain Yaseer ya ce, "In kuwa hakane basu kyauta mana ba Allah, duk saurin da na yi ace har an gama, ai dana sani ban zo ba ke nan.." Ya faɗa fuskarsa a haɗe ya ɗago da wuyan hannunsa yana duban diamond wrist watch dinsa.
"Wataƙil mun makaro ne, amma ni abun da bangane ba Ina mutanan gidan ne? Babu kowa kodai sun bar gidan ne?" Zaid ne ya tambaya,
Zayn ya ce, "Ko dai sun canza gurin da za a yi meeting dinne?"
"Nafi tunanin haka, cos duka baifi karfe hudu da rabi ba akwai sauran time" A cewar Captain.
Mommy Turai ta ce, "Gaskiya bana tunanin sun canza wurin yin meeting din, ko a wurin birthday din Owais sai da Baba Obie ya ƙara jaddada mana a nan za'a yi, kuma ina ji a raina ba'a gama meeting din ba sai dai idan wani abunne na daban..."
"Bari na kira daddy na ji ina su ke ne..." Jazz ne ya faɗa tare da zaro wayarsa daga aljihu, har ya fara danna wayar kwatsam Idanunsa suka sauka akan rigar shaddar dake yashe kan floor..
Cikin sauri ya nufi rigar duk suka bi shi da ido, Ya zukunna tare da ɗaukar rigar ya kanga ta a hancinsa.
Dubansu ya yi fuskarsa da ruɗu ya ce, "Rigar daddy ce, na ji ƙamshin turarensa.." Maganar da ya yi ta jefa su a a ruɗani, Turai ta ce, "Hakan na nufin yana acikin gidan nan kenan! To amma ina suka shiga? Sannan meyasa ya cire rigarsa ya bar ta akan floor"?
Ta faɗa a rude, ɗan dafe kai Captain Yaseer ya yi, cike da rashin walwala ya dan ja da baya, juyawar da zai yi keda wuya idanunsa suka sauka akan dattijuwar dake a kwance kan doguwar sofa rai hannun Allah.
A firgice ya daka tsalle ya ja baya yana faman zare hazel eyes dinsa, labbansa na kerma ya furta, "Wa'inna hu min sulaiman wa innahu bismillah!Kuna ganin abunda nake gani kuwa? Wacece tsohuwar nan?" Gaba ɗaya ya bi ya ruɗe yayi zaton ba mutun bace.
Hankulansu a tashe suke kallon tsohuwar gaba ɗaya basu lura da ita a kan kujerar ba saboda sun bata baya shiyasa basu ganta ba, kuma Sofas din suna da yawa two sets ne.
gaba ɗaya sun razana da ganin ta, basu san wacece ita ba.
Ziyad ya ce, "Ko dai baƙuwa ce muka yi?" Girgiza kai Yaseer ya yi, "Bazai yiwu ba, bana tunanin mutunce, sai dai idan Aljana ce, ni hankalina bai kwanta da ita ba, jibarta fa ka ga ni.." ya faɗa yana nunata da yatsan sa dake ɗan kerma.
"Duk ƙasusuwa a jikin ta, kamar mai fama da cutar ƙanjamau..."
ya faɗa yana yamutsa fuskarsa..
Ta6e baki Zayn ya yi, "Na fi tunanin mutum ce, amma waya kawo mana bare a family dinmu? Bai kamata aga wannan halittar a gidan mu ba." A wulaƙance ya faɗa, kwata kwata basu damu da halin da take a ciki ba, har gwara justice da bai tanka ba shida Ziyad.
Jiki a sanyaye Turai ta nufe ta duk da tana jin fargaba, zukunnawa ta yi daga gaban sofa din ta ƙura mata idanunta, tsantsar tausayinta ne ya kamata ganin jinin dake ɗan ɗiga daga hancin ta, gashi a wahalce take jan numfashi, ta fahimci bata acikin hayyacinta sai sambatu ta ke yi ƙasa ƙasa.
A hankali ta shafa forehead ɗinta da tafin hannunta ganin fatar wurin ta yi tamoji tamoji ta yi duhu kamar ta ta6a ƙonewa.
"Ina tunanin bata da lafiya, amma wacece ita? Wa ya kwantar da ita anan? Ta ya za'abar majinyaciya ita kaɗai batare da likitan da zai duba ta ba.." Ta faɗa cikin nuna tausayawa.
Yaseer dai tsoronta Yake ji sai faman zazzare eyes ɗinsa ya ke yi.
Twins ma duk sun sha jinin jikin su.
"Jazz zo ka dubata pls, mu taimaka mata kada ta rasa ranta.."
Matsawa Jazz ya yi gaban kujerar ya zauna saman hand sofa din, kafin Ya daura tafin hannunsa saman kan Khala a hankali ya kamo tafin hannunta ya ƙura mashi ido yana nazari akan ta, har wuyanta ya shafa.
"Jazz baka da hankaline! Kasan wacece ita da zaka ta6ata, salon ka kwaso mana cuta?"
Zayn ne ya faɗa da tsawa, Ko kula sa Jazz bai yi ba hankalinsa na akan Khala da tausayin ta ya fara kama shi.
Ziyad ya ce, "Koma wacece ita ina ji araina mutunce ita, dole akwai wanda ya kawota gidan nan, abunda yakamata mu yi shine mu tuntu6i baba a waya muji ina suke, in ya so sai mu tambayeshi game da ita..."
Ya ƙarasa maganar tare da zaro wayarsa daga aljihu ya shiga kiran layin Baba Obie.
Almost 5 times tana ringing ba'a yi picking ba (rashin sani yafi dare duhu)
"Wayar na shiga amma ba a ɗauka ba" ya faɗa yana dubansu.
Cikin sauri Captain Yaseer Ya zaro wayarsa daga aljihu ya kira layin daddynsa His excellency Abdul Razak..
Shima Almost 5 times tana ringing ba'ayi picking ba..
"Me zai hana mu je part din baba? Nasan ba su wuce can"
Zaid ne ya faɗa, basu tsaya 6ata lokaci ba suka dunguma izuwa sashen baba Obie ya rage saura Turai tare da Jazz dake duba momma.
Tunkan su ƙarasa suka hangosu zazzaune bakin door room din baba Obie sun raku6e jikin ƙofar, kwata kwata basu motsi sai numfashin su dake fita da ƙarfi, ga wani bugun barazana da zuciyoyin su ke yi, fuskokin su sunyi sharkaf da jirwayen hawayen su, idanun su sun kaɗa jawur sun kumbura tamkar yaji ya shiga cikin su.
Wani irin faduwar gaba suka ji, lokaci ɗaya yanayinsu ya sauya zuwa tsantsar tashin hankali da fargaba, a hanzarce suka ƙarasa gabansu kusan atare suka zube kan gwiwowinsu suna fuskantar su.
Cike da tashin hankali suke tambayar su meya faru da su? Meya sanya su yin kuka? Meke damun su?"
Hakika sun razana da ganin halin da iyayensu suke a ciki, basu ta6a ganin rauninsu irin na wannan ranar ba, ko magana basa iya yi sai dai suka dinga bin su da raunatattun idanunsu da suka galabaita.
gaba daya gumi ya