Showing 147001 words to 150000 words out of 319356 words
Chapter 50 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
da ƴarsa, sun kuma ji bakin ciki mara misaltuwa.."
Akan idon kowa dake a gurin, har zasu zuƙunna kan gwiwowin su Sheikh imam yayi saurin dakatar da su, yace su manta da komai, ya yafe masu, duk abun da ya faru arayuwar shi da ƴarshi ya dauke shi a matsayin jarabtace daga Allah, bayan haka suma ai ba laifin su bane, Musa shi ne musabbabin komai da ya faru."
Farin ciki ne ya lullu6e su, suka dinga yi masa godiya kamar zasu durkusa ƙasa.
Daga bisani suka roki yafiyar Aisha akan abun da ya faru na rashin adalcin da basu yi mata ba, itama ta ce ta yafe masu, Allah kuma ya yafe masu gaba ɗaya suka amsa da Ameen..
Bayan komai ya ɗan lafa, kowa ya nemi yafiyar wanda ya 6ata ma rai, Abie da Mami su ka yi masu sallama suka tafi gida saboda halin da suka baro iyalin ɗan iya, suna bukatar su a kusa da su bayin Allah, Anila dai bata bisu ba tana a gidan Chief Owais, saboda aminnanta da suke a hali na jimamin ƙaddarar da ta same su, yanzu haka tana a ɗakin Aisha tare da Benazir.
"Aisha, duk da komai da ya faru ba laifin kowan nan mu bane amma hakan bazai hana mu baki hakuri ba. Ki yafe mana dan Allah, mun san kin cutu, amma komai ya wuce dan Allah mu koma kamar yadda muke a da..."
Benazir da Anila ne suka hada baki gurin yin maganar yayin da suke a zagaye da Aisha.
Suna a zazzaune kan rug fuskokinsu sharkaf da hawaye, idanunsu sun kumbura sunyi ja sakamakon kukan da suka sha jiya ga rashin baccin da basu yi ba.
da tafukan hannayensu suke share mata hawayenta dake sauka kuncinta.
"Ni yakamata in nemi yafiyar ku, ku yafe mini, na yi kuskure da na tafi batare dana faɗa maku ba, nasan da duk hakan bata faru ba. Bayan haka na yi maku laifi, ranar da muka hadu tabbas na ji dadin da ba zai misaltu ba dana sake ganin ku, amma zuciyata sai ta dinga zuga ni akan kada in kula ku, sakacin ku ne yasa kuka bar ƴata ta mutu, baku bata kulawa ba, shiyasa ko kun kira bana picking..."
idanunsu cikin na juna suke sauraronta.
"Amma daga baya da na ji komai a bakin Musa, na yi danasani,.."
Kifa kanta ta yi saman kafadar Benazir, "Kin yi abun da bazan iya biyanki ba Benazir, saboda kaunar da kike min yasa kika jefa rayuwar ki cikin hadari..."
Ɗagowa ta yi da kanta, ta ruƙo hannayesu a cikin nata tana murza su.
"Aisha, baki mana laifin komai ba, mu manta da komai da ya faru, mun yi imani da Allah, kuma mun yi imani da kaddara, kuma komai ya faru da mu jarabtace daga gare shi, tabbas uncle Musa ya zalunce mu amma ba mu ya zalunta ba kanshi ya zalunta, in sha Allah zai ga mummunar sakayya.." In a broken voice Benazir ta yi maganar.
In a cool voice Anila ta ce, "Dukkan mu mu yi hakuri mu rungumi kaddara, tuna abun da ya faru baya ba zai amfanar da mu komai ba, illa iyaka ya fama raunin da ke a zuciyoyinmu..."
nasiha mai dadi suke yiwa junan su.
"Yanzu ni damuwata ƴaƴan mu har yanzu ba wani labari, sun gano su ko ba su gano su ba, bana so ya cutar da su bana so ya kashe min su.." Aisha ce ta fada cikin ƙunci.
"Na fi jin Batool, yarinyar nan tun tana cikin mahaifiyarta take fuskantar jarabawa, ita ma kuma ta zo duniya ta dasa da fuskantar tata jarabawar..."
cikin raunin murya Benazir ta ƙarashe maganar...
Aisha ta ce, "Haka itama Unaisah, tun tana a cikin mahaifiyarta take fuskantar jarabawa, itama kuma da ta zo duniya ta dasa da fuskantar tata jarabawar, na daɗe ina nanata labarin Unaisah a zuciyata ban taba kawowa raina ke ce mahaifiyarta ba, amma Unaisah ta yi bajinta, gaba daya sun cancanta su yi rayuwar farin ciki a tare da mu..."
Anila da ke sauraronsu sai share ƙwalla ta ke yi.
"Pls ku kwantar da hankulanku in sha Allah babu abun da zai same su, kada ku manta addu'ar iyaye akan ƴa'ƴan su kar6a66iya ce, Kuma addu'ar wanda aka zalunta akan wanda ya zalunce shi itama kar6a66iyace, daren jiya mun kwana muna yi masu addu'a, bi'iznillahi addu'oin da muka yi masu zasu isa gare su ne, In sha Allah ina ji a raina zasu dawo da ransu da lafiyarsu.." Cikin kwantar da murya take lallashin su..
Knocking Kofar dakin aka yi..
"Wanene"? Aisha ce ta tambaya,
"Shureim ne..." Daga waje suka ji ya ambata..
Kallon Aisha suka yi, ganin ta sadda kanta ƙasa..
"Nasan da ke yake son yin magana, tun jiya ya ke neman hanyar da zaku ke6e, dan Allah ki je ku gana." Benazir ce ta faɗa.
Share hawayen fuskarta ta yi tare da mikewa ta nufi kofar ta ɗan buɗe tare da leƙa kanta, kaitsaye idanunsu suka shiga cikin na juna, wani irin kwarjini ya yi mata ta yi saurin kawar da idanunta daga kallon shi, mutuncinsa da ya zube a idanunta ada yanzu ya dawo sabo, tun da ta ji komai a bakin Musa.
Ya kafe ta da idanun shi yanata kallonta kamar zai haɗiyeta..
"Zamu iya magana"? Kamar jira take ya tambayeta, da sauri ta ce, "Eh."
Juyawa ya yi tabi bayan shi suka nufi back yard din gidan, a saman park chair suka zauna wata irin ni'imtacciyar iska ce ke ratsa fatarsu
Ta yi shiru tana jira ta ji me zai ce mata, Idanunta na akan yatsun hannunta da take wasa da su.
Yayin da ya kafe ta da idanunshi, sai kallonta ya ke yi.
"Aisha am..." Katse shi ta yi, "Nasan me zaka ce, komai ya wuce ya Shureim, kada ka yi min magana akan abun da ya faru baya, idan ma akwai wanda ya cancanci ya nemi yafiyar to ni ce, ka yi hakuri ya Shureim na munana maka zato bisa rashin sani, idan na tuna marin da na yi maka a ranar sai in ji bakin ciki ya turnuƙe zuciyata, ashe ba yin kanka bane, meyasa banyi maka uziri ba? Meyasa ban saurareka ba? Meyasa lokacin da ka ce na tsaya zaka aure ni mu rufawa juna asiri ban yi ba...?"
Bata ƙare maganar ba ya yi saurin toshe mata baki da yatsan shi, suka ƙurawa junan su ido yayin da hawaye ke zarya kan kuncinsu, wani irin kallon so da kauna suke ma junan su..😍
"Aisha bana so kina magana akan abun da ya wuce, mu manta kawai, ina mai baki hakuri akan zaluncin da Uncle Musa ya yi maki, na ji bakin cikin da bazai misaltu ba.
jinjina mashi kai ta yi alamar ta yi...
"Ki yafe min Aisha, na yi kuskure tun farko da ban bayyana maki soyayyata ba, zurfin cikin da na yi shi ya ja min, ban tashi sanin kina sona ba sai da na ji a bakin mahaifinki, a ranar da ya kira ni don ya tuhumeni akan abun da na yi maki...."
labarta mata tattaunawar da suka yi da imam malik ya yi..
"Lokacin da Benazir ta zo dake ɗakina don ta nuna min ke a ranar dana dawo daga Egypt, na nuna kamar bansan ki ba, amma wallahi Allah shine shaidata Aisha, na yi maki son da ban ta6a ma wata ƴa mace ba, tunkafin in mallaki hankalina nake son ki, da soyayyarki na girma a cikin zuciyata, lokacin da ina Egypt, bani da abun kallo a wayata da ya wuce hotunanki da videos din da ake yi maki a gurin musabaƙa, da zarar an saki videos dinki jiki na 6ari nake zuwa in kalla, dake nake kwana dake nake tashi a raina, kamar yadda kike addu'a a kaina nima haka nake yin addu'a akan ki, kin sha hanani bacci Aisha ..."
Kalamansa sun karya zuciyarta, yanzu ta gane ba ita kadai ta yi dakon soyayyar shi ba, ashe shima ya so ta kamar ran shi..
"A ranar da na gaji da azabtuwa da sonki, na yanke shawarar zan tunkare ki in faɗa maki halin nake a ciki, a ranar ne na jiyo firar da ku ke yi ke da su Benazir a ɗakinta, na ji kina fadin kinsan babu namijin da zaiso ki tsakani da Allah sai don surar jikin ki, da na ji wannan maganar nan take gwiwata ta sage, na ji tsoron ma in tunkare ki da maganar saboda nasan nima zaki iya tunanin saboda surar jikin ki na ke son ki, dama tun farko abun da ya hana in faɗa maki saboda ina jin tsoron amsar da zaki bani, shiyasa na kasa tunkarar ki da maganar, saboda ina jiye ma kaina tsoron ki ce baki sona, zan shiga mawuyacin hali, haka na ci gaba da tunanin ta wace hanya zan tunkare ki da maganar batare da kin zargi jikinki nake so ba, ban kaiga samun mafita ba, wannan mummunan al'amarin ya faru..."
bata san sa'adda ta kife kanta saman kafaɗarshi ba, wani irin son shi ne ke ninkuwa a cikin zuciyarta.
"Yaya Shureim, gaba daya mun yi kuskure da bamu bayyana son da muke ma junan mu ba, nima abun da ya sa na kasa fada maka ina son ka, saboda ina jin tsoron ka ga kamar na zubda ƙimata, duk da ba haramun bane don mace ta ce tana son namiji, amma wasu mazan na zamanin nan ba su daraja macen da ta ce tana son su, hada kuma ƙarin nima ina zallumin ka ce baka sona..."
gaba ɗaya jikin su kerma ya ke yi, sun kasa tsayar da hawayen dake sintiri kan kuncinsu.
"Amma yanzu daka bayyana min soyayyarka, hankalina ya kwanta, sai na ji kamar an yaye min wani sashe na damuwata, ka yi haƙuri ya Shureim na ji kunya, na kuma ji tausayinka da na ji irin izayar da iyayenka suka yi maka kai da babynmu, ashe haka kake son jinina?"
Ta tambaya batare da ta ɗaga kanta ba..
"Tayaya ba zan so jininmu ba Aisha? har raina zan iya badawa a kanta, a lokacin da nasan tana a raye wlh har raina zan iya sadaukarwa saboda in ceto rayuwarta. Ina son ta kamar yadda na ke son ki."
"Ya Shureim ko bayan da abun ya faru ban tsaneka ba, saima sonka da ya ƙara ninkuwa a zuciyana, kawai dai na yi baƙin cikin ta yadda abun ya faru, amma ya wuce..."
murmushi ya yi, still idanunsa akan ta, ko kyaftasu bai son yi
"Ya Shureim ka ta6a ganin ta?" Ta tambaya tare da ɗago kanta ta dube shi.
"Eh, a ranar dana kawo su Benazir gidan nan na ganta, har na taimaka mata gurin cire mata mayafinta da ya sargafe kunnanta.." Murmushi ta yi. "Ya ka ganta?"
"Kamar na yi kakinta." Ya fada tare da jan hancin ta, murmushi suka sakar ma juna..
(Allah sarki Soyayya ruwan zuma, su boss ko yaushe romeo zai zo😂 Oh ni, inata aikin jiran baby Junaid.)
"Tun a ranar farko da na fara ganinta nake ta kokarin in tuna dawa ta ke yi min kama, ban tashi tunawa ba sai ranar da na sake ganin ka. Ina son ta Ya Shureim, ina son jininka sai dai..."
Kasa ƙarasa maganar ta yi saboda ƙululun bakin cikin da ya tokare makoshinta, sakamakon tunawa da ta yi a yanzu yarinyar bata a tare da su, tana can hannun azzalumin mutumin da ya cutar da rayuwarta.
Gefen fuskarta ya shafa,"Aisha nasan me ke damunki, nima ina jin raɗaɗin da kike ji a zuciyarki, but pls, mu yi hakuri mu jure, in sha Allah ba abun da zai faru da su, Allah ba zai bari ya cutar da su ba, tun da mun yi masu addu'oi toh mu jira muga abun da Allah zai yi akai tun da mun yi imanin shine mafitarmu.."
Kalamai masu dadi da kwantar da hankali ya ci gaba da furta mata har saida ya samu ya shawo kanta..
Mayar da kanta ta yi saman kafaɗarshi ta dan lumshe idanunta.
~________________Benazir & Anila~
Suna tsaka da yin firar abun da ya faru da su jiya, knocking din kofar da aka yi ne ya katse su.
"May be Aisha ce ta dawo, bari na duba. " Anila ce ta fada tare da miƙewa..
Benazir ta ce, "Anya Aisha ne? Ke kina tunanin ya Shureim zai kyaleta yanzu? Tun fa jiya da muna yin salla na lura daga an sallame sai ki ga ya juyo da kai ya dube ta.." Duk da halin da suke a ciki na zullumi da fargaba sai da suka dara.
Buɗe kofar ɗakin Anila tal yi,
Taj ta gani a tsaye ya rungume Junaid dake ta yin kuka a ƙirjin shi..
"Anila tayaya akai Junaid ya ga gawar Ana? Gashi nan tun da ya farka yake ta kuka yana ambaton sunanta, wlh na yi mamaki, inata lallashin shi ya ƙi yin shiru." Tausayin shi ne ya rufe Anila, da sauri ta kar6e shi ta rungume a kirjinta tana dan jijjiga shi, fuskarsa ta jiƙe sharkaf da hawaye, ta yi mamakin yadda har Junaid ya iya ruƙe abun da ya faru bayan baccin da ya sha.
"Ka yi shiru my baby boy, ka daina kuka, ba abun da ya faru da Ana, tana nan.."
Cikin shessheka ya ce, "Mom.. mommy ai na ga Ana, ta mutu, dodo ne ya kashe ta, ba na faɗa maki ba, kuma na ganta bata motsi, Ana ta mutu, ta tafi lahira gidan Allah..."
ɗan zaro ido Anila ta yi ta ɗan kalli Taj suka hada ido, murmushi suka yi..
"Kana so Ana ta shiga aljanna?" Jinjina mata kai ya yi yana faman mutsustsuke idanunshi..
"To ka yi mata addu'a, amma in ka ci gaba da kuka Ana bazata shiga aljanna ba, ka ga ko mun je wata rana ba zamu ganta ba."
da sauri ya soma share hawayen shi, "Bazan ƙara ba, na daina, ina so Ana ta shiga aljanna."
Shafa sumar kanshi ta yi. "that's my boy."
"Anila, ke da waye ne? Na ji kamar kukan Junaid."
"Wlh shine Taj ya kawo min, Yaro ya burkice yana ta sambatu kan Ana.." Fitowa Benazir ta yi daga dakin.
hada ido suka yi da aj, gaba daya sun fahimci damuwar da kowan nan su yake a ciki..
"Daddyn Unaisah, ka tashi lafiya? Ka ci abinci? Ka yi bacci kuwa?" Da damuwa ya ce, "In har kin yi duk abun da kika tambaye ni toh nima na yi, in kuma baki yi ba, nima ban yi ba.."
Murmushi ta yi, "In har ba su Unaisah ne suka dawo ba, bana jin zan iya cin abinci ko in yi bacci."
Bata ƙare maganar ba ya katse ta, "Inason magana da ke." Kallon Anila ta yi a lokacin har ta juya ta shige ɗaki da Junaid..
Bin bayan shi ta yi, suna gab da zasu gifta ta falo Alhaji Ubaid ya yi masu gyaran murya, sam basu lura da su ba.
Shi da Hajiya Layla ne zaune kan kujera..
Cikin nutsuwa Taj ya nufe su, with respect ya gaishe da su..
Cike da jin nauyin shi hajiya Layla ta ce, "Taj kaima mun yi maka laifi, tun jiya nake ta so in nemi yafiyarka amma kunya ta hana ni Taj." Ta faɗa idanunta cike tab da ƙwalla tana ɗan girgiza kanta cike da danasani.
"Tun da ka auri Benazir ban ta6a nemanku ba, lokacin da kuka 6ace, na ji labari amman ban nuna damuwa ba ko kaɗan, saboda banso Alhaji ubaid ya baka auren ta ba, shiyasa na zame hannuna a cikin rayuwarku tun da kai ba za6ina bane, na yi maka wulakanci saboda kasantuwarka ɗan jarida mai rufin asiri, a lokacin da idanuna suka rufe da son siyasa, a ganina zaka jaza mana matsala ne, ashe ba haka bane, kai din Alkhairi ne a cikin rayuwar mu, samun suruki irinka zai yi wuya a duniyar nan, gashi ta silar haɗa zuri'a da kai mun samu lu'u lu'un da kowa ke alfahari da shi.
Murmushi suka yi shi da Benazir, har ga Allah bai ta6a ruƙe su aran shi ba, tabbas bai ji dadin halin ko in kulan da Hajiya layla take nuna masu ba, Amma saboda Alhaji ubaid yana son Unaisah yasa bai ta6a ruketa aran shi ba..
"Kada ki damu, komai ya wuce, na yafe maki, Allah ya yafe mana baki ɗaya." Ta amsa da Ameen.
Alhaji Ubaid yana murmushi ya ce, "Gaskiya ni ban yafe mata ba, tsakani da Allah bata kyauta ba, ko fa fuskar jikarta bata ta6a sani ba, sannan kuma ka ce ka yafe mata ta cikin sauki, lalala, sai ta ji jiki tukunna." Dariya suka saka, kamar babu damuwa a tare da su.
"Baba, ayi hakuri dai a yafe mata tun da ta gane kuskurenta, mu ma muna so in munyi laifi Allah ya yafe mana." Alhaji ubaid ya ce, "Toh mun yafe mata, ba don halin ta ba." Tana murmushi ta dubi Benazir, "Yanzu hankali ya kwanta ko? No more pretending, and no more tashin hankali akan mijina, ƴata, duk kika bi kika hana mutane bacci.
murmushi suka saki gaba dayan su.
"Daddy, mommy, pls, tun da mun haɗu gaba ɗaya kuma ga Taj shima, ku saka baki ya maidani..."
buɗe baki suka yi da mamaki, kunya ta kama Taj ya sunnar da kai ƙasa.
Alhaji ubaid ya ce, "Koda yake, ay da yake jinin ki ce, fiye ma da haka zata iya." Hajiya Layla ta yi saurin cewa, "Dan Allah ka daina mana, a gaban surukin namu." Ta faɗa tana nuna Taj, dariya suka yi..
Harara ta galla ma Benazar. "Ke ko irin alkunyar nan baki da ita, ay kya bari jikokin namu su dawo lafiya ko." Walwalar fuskarta ce ta ɗauke, ji ta yi kamar ta fama mata raunin zuciyarta.
Lura da yadda jikinsu ya yi sanyi yasa Alhaji Ubaid da hajiya Laylan suka haɗu gurin kwantar masu da hankali.
Daga bisani suka ce su tafi inda zasu je, miƙewa suka yi a tare suka nufi garden, a kan kujerun shaƙatawa suka zauna..
"Pls ki daina zubar da hawayenki, In sha Allah ba abun da zai faru da su, zasu dawo lafiya"..
Jinjina kai tayi, "Zan daina amma kasan ba yadda za'ay hankalina ya kwanta bayan ƴa'ƴanmu suna a hannun fasiki, wlh baka ji yadda zuciyata ke bugawa ba, tun ɗazu nake jin fargaba, gabana yana ta faduwa..."
"Ummu Unaisah, duk abunda kike ji nima ina jin shi, amma ya zamu yi? Tun da munyi