Showing 168001 words to 171000 words out of 319356 words
Chapter 57 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
baya picking meyasa?
Cikin rashin nutsuwa ya zayyana masu komai, basu yi mamakin jin Ɗan iya da Alhaji Musa suna a cikin Elders ba, saboda dama can mutane suna zargin dukiyar Musa bata halal bace, musamman yadda yake almubazzaranci, ga girman kan tsiya da izza ashe yasan meya taka..
Ɗan iya kuwa duk sun san halin shi na maitar son abun duniya, ya cika haɗama ga ƙarya a bakinsa, bayan kasantuwarsa munafuki ya kuma ƙware gurin haɗa yan siyasa faɗa, ya ƙulla masu makircin da zai raba kansu, in har aka biya shi kuɗi babu abun da bazai iya yi ba, shi dama baki gare shi, ko dan jarida bai kai shi haɗari ba, ya iya tsara kalaman ƙarya, idan yayi wa ɗan siyasa campaign zai yi wuya ka ga dan takarar bai yi nasara ba, shiyasa ya siye zuciyar politicians da ta al'umma, in ya so abu kamar zawo yake baida hakuri, ya iya shisshigewa masu hannu da shuni wadanda suka shahara, kuma baya gajiya da bauta masu don ya samu abin duniya.
A tare suka haɗu da shi da Uncles din nashi, suka fara shawarar ta yadda zasu shawo kan baba Obie don ya taimaka masu su gano inda Musa ya je da yaran nan, sun san zai iya, a wannan ga6ar sun yarda ko sihirin ne ya yi saboda a taimaki rayuwar yaran kafin ya cimma manufarsa akan su, don suna ji a ransu ba hakanan ya za6e su su biyu ba, bayan ga fursinonin da suka killace a asibiti, amma duk ya tsallake su ya ɗauki yara biyu kacal dake a gidan Dg! Meyasa? Dama yana bibiyar rayuwarsu kenan? Wadannan tambayoyin ne suka tsaya masu a kahon zuciya, sun kasa samun amsoshin su, amma fa suna a cikin rudu da fargaban me zai biyo baya don sunsan ba alkhairi bane da akwai sauran rina a kaba...🔥
Da farko har sun yanke shawarar zasu tunkari Baba Obie gaba ɗayansu don su roƙe shi, prime minister ya ce kada su wahalar da kansu, sun manta wanene baban nasu, ba zai ta6a sa6a alƙawari ba, amma akwai wata hanya da ya ke ganin in suka bi za su yi nasara akan shi..
A kagare suka tambaye shi wace hanya ce.
Ya ce nazarin da ya yi cikin tattaunawar da Owais ya yi da Baba Obin, ya fahimci wani abu, tabbas bazai karya masu alkawari ba amma in har suka ci amanar shi zai tona masu asirin su ne, dalili kuwa a maganar shi ya ce in har suka kawo masu farmakin bazata, su yi saurin sanar da shi, shawarar da zai bada su yi amfani da Saratu dake jinya, su faɗa masa an kawo masu farmaki kuma an raunata wasu daga cikinsu ga kuma shaida nan.
Gaba ɗaya sun yi amanna da maganar Prime minister, sun kuma jinjina ma hikimarsa.
A daren ranar Hateeem ya kira Sharafuddeen ya fada masa komai dake faruwa har set up din da zasu yi, ya kuma ce yana son ya tura ma Owais video din Auta.
Cikin abun da bai fi mintuna biyar ba, Sharafuddeen ya tura ma Owais video din hajiya Saratu kwance akan gadon asibiti tana ta sambatu.
Prime minister ne ya tsara mashi komai da zai fada ma baban, bayan sun gama shirya komai..
Chief Owais ya nufi back room dinsa, A gaban tagar ya tsaya tare da fashewa da kuka yana ambaton sunan shi baba baba baba, yadda kasan ƙaramin yaro.
Kwata kwata baya iya hangensa saboda ya kashe light din dakin, duhu ne ko'ina.
Sautin kukansa da baba Obie ya jiyo yayi matuƙar ɗaga hankalinshi, cikin raunanniyar muryarsa ya shiga ambaton sunan shi Owais Owais, jikallena? Meya faru? Kukan ka nake ji ko kunnena ne su ke jiyo min ba daidai ba?"
Cikin shesshekar kuka ya ce, "Baba muna a cikin tashin hankali, jiya da daddare baka ji jiniyar motoci ba?"
"Owais na ji, wani abu ya faru ne?"
"Eh baba, jiya an kawo mana farmaki, muna tsaka da bacci, wasu miyagu suka ritsa da mu, kafin mu ɗauki mataki sun raunatar da wasu daga cikin mu..."
Bai ƙare maganar ba, ya ji baba Obie yana ambaton Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, cikin ruɗu da tashin hankali, "Owais dawa dawa suka farmaka..."
"Gidana, harma sun ɗauki yara biyu daga cikin yaran da nake kula, bayan haka sun farmaki auta, baba muna zargin da sa hannun Elders.
Muryarsa da tashin hankali ya ce, "Owais me suka yi mata? Sun cutar min da ita? Tana raye? Owais ka fadamin! Ina Saratu take?"
"Tana a kwance rai hannun Allah, gaba daya sun faffasa mata fuskarta da glass, kwata kwata bata a hayyacinta sunan ka kaɗai take fada, ba don munyi saurin kaita asibiti ba da tuni rai ya yi halinsa, ga shi ka kalli videon ta da na ɗauko maka." Ya fada tare da tura wayar ta cikin tagar.
Baisan sa'adda ya sanya hannu ya kar6a ba sai dai ya ji babu wayar a hannunsa alamar ya ɗauka, cike da zumudi yake jiran ya gama ya ji me zai ce fatansa Allah yasa ya taimaka masa.
"Owais, ku yi hakuri, komai ya faru ni ne na ja maku, laifina ne! Da nasan zasu ci amanata da ban boye maka su wanene sauran ba, gashi nan har sun fara farmakar ahalina, dama nasan za'a rina tun da ba Allah ne a ransu ba, wallahi tun da har suka ta6a jinina bazan ƙyalesu ba, sun ja ma kansu bala'e da musiba..."
Farin ciki ne ya lullu6e zuciyar Owais.
Aje masa wayar yayi kan tagar ya zura hannu ya ɗauka.
"Baba kada ka damu dan Allah, ni ban nuna maka don na ɗaga maka hankali ba face don ka taimaka mana mu nemi mafita, in ba haka ba zasu iya ƙara farmakar mu..." Bai kare maganar ba, ya katse shi cikin fushi ya ce, "Owais, yaran da suka ɗauke meye sunayen su?"
"Unaisah yarinyar da zan aura, ɗayar kuma sunan ta Batool, mun neme su sama ko ƙasa mun rasa baba! Na manta ma ban faɗa maka ba, na gano mutun biyu cikin Elders, Musa da Ɗan iya, kuma muna zargin Musa ne ya shirya komai.
Da jin wannan maganar yasa baba Obie ya gano me suke shirin ƙullawa wato basu daddara ba bayan gargadin da ya yi masu akan su aje makaman yaƙinsu su gudu su nemi mafaka, amma saboda haɗama ƙarfin ikon shi suke so su ƙwace shiyasa suka ɗauke yaran don su cika sharuddan, kuma yafi zargin musa ne kamar yarda ya faɗa, saboda yasan mugun halin shi zai iya komai don ya cika burin sa.
"Baba ka yi shiru ba ka ce komai ba, meya kamata muyi yanzu? Yaran tun jiya suka sace su bayan isha'e suka tafi da su, bana so su cutar da rayuwar su, gaba daya komai ya kwance mana!"
"Owais, you have my word babu abun da zai faru da su, in har ba sun riga da sun cutar da su ba saboda jinkirin da kuka yi baku sanar da ni ba, amma ku shirya rundunar sojoji ku tafi kurkukun ƙaddara yanzun nan, suna a can tare da yaran, kafin ku isa taimakona zai riga ku isa."
Godiya ya yi masa cike da zumudi ya juya cikin sauri ya tafi.
Kafin ya bar gidan saida ya fara zuwa falo ya sanar da Uncles dinsa yadda suka yi da baban, sun ji dadi bayan sunyi masa fatan alkhairi ya fito daga gidan ya shige motar shi, Ya ce da driver dinsa ya kaishi Headquarter ɗinsu, kafin su isa ya kira layukan senior agents dinsu ya ce su yi gaggawar shirya rundunar sojojinsu daga ya ƙaraso zasu tafi kai farmaki gidan Kurkukun Ƙaddara🔥
(Kunji Yadda aka yi Suka yi Nasarar Kama Elders)
Wani taimako baba Obie ya yi masu?
Bayan tafiyar Owais, cikin duhu ya zauna kan kujerar gaban madubin dakin sa, da tsafi ya yi amfani, Duk Elder din da ya kira sunan shi zai bayyana ta cikin madubin, gaba daya saida ya kira Elders din kurkuku mazauna kasashen waje, ya ce sun kuwa san da makircin da Musa ke shirin ƙulla masu? A rude suka ce basu gane me yake nufi fa?
ya yi murmushi saboda ya gane Musa bai sanar da su ba, shi kadai ya ke shirin shi,
Ya ce dama ya san bazai sanar da su ba, saboda baya son su sani, amma zai fada masu yanzu haka Musa ya dauke ƙaddarar kurkuku, da bugun zuciyar kurkuku, Kuma ya tafi da su gidan Kurkukun don ya aiwatar da sharuddan dodon tsafinsu, in har suka bari Musa ya cimma burinshi, babu tantama zai ƙwace sihirin jikinsu ne sannan ya kashe su, ya ce abun da ya sa ya faɗa masu saboda ya tsiratar da su daga kaidinsa saboda shi ma Musa bai ƙyale shi ba, jiya ya turo da giants sun farmaki ahalinsa, tun da har shi da ya yi mashi halacci ya butulce masa su su wanene da suke tunanin ba zai ci amanar su ba?"
Maganar da Obie ya fada masu tayi matuƙar daga hankulansu, da ya ga sun yarda da shi ya kuma cewa, "Ni ban damu wani daga cikin ku ya samu karfin ikona ba, amma ku yi tunani idan Musa ya hau karagar mulkin Elder me zai biyo baya? Kun dai san halinsa ba sai na fada maku ba, kun kuma san me zai iya da wanda ba zai iya ba, " Abun da ya harzuƙa su ta yadda Musa ya 6oye masu abun da yake shiryawa, shi yasa suka yi amanna da maganar baba Obie..
Daga karshe ya ce masu yanzu ya rage nasu! Ko dai su yi gaggawar zuwa gidan kurkukun kaddara kafin rana ta fadi ko kuma su yi dana sani na har bada, yana ƙare maganar, ya rufe madubin nashi da sihiri.
Ya ɗauko wayarsa ya kira layukan sirri na Jan ido da Jan le6e bayan sun ɗaga suma ya faɗa masu abun da Musa ke shirin aikatawa.
Jan Ido ya ce shi bai damu ba don hankalinsa ba a kwance yake ba, asirin shi ya riga da ya tonu, neman mafaka ya ke yi,
Baba Obie ya ce mafaka ɗaya ta rage masa, ya gaggauta zuwa gidan kurkukun ƙaddara, Musa yana a can zai cika sharuddan dodon tsafi, idan suka samu ƙarfin ikon shi zasu fi ƙarfin kowa, in ma suka so zasu iya shafe memory ɗin mutanan da suka san sirrin su.."
Da jin wannan maganar yasa suka amince zasu je gidan Kurkukun ƙaddara...
(Kun ji yadda a kai Obie ya haɗa Elders gaba daya a gidan kurkukun kaddara saboda ya sawwaƙawa su Chief Owais don su kama su duka, da yake ƙwararrun matsafa ne har wadanda ke a nesa da zarar sun so zasu 6ace su dira a inda suke son su kasance, shiyasa suka haɗu cikin ƙanƙanin lokaci.)
Sannan kuma ya tura Evils din jikinshi zuwa Prison Temple don su hukunta Musa, waɗannan Evils din da suka zane Musa da bulalai ba asalin Temple Evils bane, ba mutane bane, shaiɗanun aljanu ne masu haɗarin gaske, su ɗin amintattun Obie ne babu mai iya sarrafa su sai shi a cikin mutane, umarnin shi kaɗai suke ji, tushen su daga jikin mahifiyarsa ne a ranar da aka haifeshi a ranar suka koma jikin shi, tun yana jariri suke a tare da shi.
Duk fa yana a cikin ɗakinsa ya aiwatar da komai, hatta Mark da ya butulcewa Musa Obie ne ya yi silar komai..
Yasan cewa shine amintaccen likitansa kuma yana tunanin shi zaisa ya cire masa zuciyar yarinyar saboda yasan jikinta bazai jure sihirin su ba.
Aikuwa da ya tashi kawai daga inda yake ya tura Evil ɗaya na jikinshi ya umarce shi da ya shiga jikin Mark, ya faɗa ma evils din jikinshi shine ya turo shi don su sarrafa tunanin Mark, su hana shi cire zuciyar yarinyar su kuma taimaki rayuwar yaran..
Gaba ɗaya komai da ya faru bada sanin Mark ba, gangar jikinsa ce kawai, amma bashi ke sarrafa kanshi ba, aikin Evils ne.
Obie ba ƙaramar tsiya ya yi masu ba, lokacin da hayaƙin nan ke fita daga hancinansu shine ya umarci kowani Evil da ya bar jikin Elders harma da Giants ya kuma ƙwace garkuwar sihirin jikinsu ya lalata komai ya barsu da halin su..
Sun daɗe suna sheƙe ayarsu sai gashi rana ɗaya a lokaci ɗaya Allah ya nuna masu iyakarsu, yanzu kuma saura su gir6i abun da suka shuka🔥
Ta yadda akai Batool ta ku6uta, lokacin da ta farfaɗo daga suman da ta yi, ta tsinci kanta a cikin ɗakin fiɗa saman gado, cikin ruɗu da razana ta soma kiciniyar kwance sarƙoƙin jikinta, tana ta kuka kamar ranta zai fita, adaidai lokacin Musa da Mark suka shigo ɗakin tiyatar, wani irin tsoro ne ya mamaye zuciyarta ko magana bata iya yi sai zazzare idanu ta ke, akan kunnanta suka tattauna game da yadda zasu cire zuciyarta, gabanta ya shiga faɗuwa ta rasa ya zata yi, gashi babu Unaisah a kusa, a cikin zuciyarta ta dinga karanto La'ila ha'illa anta subhanaka Inni kuntu minazzalimin.
Bayan da Musa ya fuce daga ɗakin, Dr. Mark ya nufe ta ta dinga masa magiya tana roƙonsa ya taimaka mata kar ya kashe ta, ya barta da ranta, tana son ganin mommynta, tana son ta ga daddynta, tana son ta ga ƴar uwarta Unaisah..."
Unexpected ta ji ya ce, "Ki yi shiru, ba kashe ki zan yi ba, taimakon ki zan yi amma karki kuskura ki fitar da sautin da zaisa ya gane wani abu.." Zare idanu ta yi a ruɗe take kallon shi cike da mamaki.
Nan take ya 6alle sarkokin jikinta da sihirinsa, ya sungumeta akan kafaɗar shi ya nufi kofar shiga pharmacy da ita, anan ya sauketa ya ce kar ta kuskura ta fito, duk abun da zata ji ta yi shiru ta jira shi zai nemo mata yar uwarta, farin ciki ne ya lullu6eta duk da akwai fargaba a tare da ita, cikin sauri ta samu guri ta zauna tana jiran shi, akan idanunta ya 6ace ma ganin ta.
Wannan zuciyar da Mark ya ba Musa a cikin kwalba, ta giant ce da ya kashe batare da sanin shi ba.
~(Kun ji yadda akai Batool ta ku6uta)~
Luxury-incense By Sapnah Borno.
Ta kawo muku turarukan wutan su Na maiduguri dana chad, turarukanta masu masifar dadi da kama waje harma da daukar hankali, indai kikayi kabbasa da turaren ta har wajen da kika zauna indai kika tashi sai kin bar kamshin ki, sannan Tana saida mayukan gashi irin nasu na shuwa Arab masu tasirin gaske, wajen gyaran Amare kuwa babu magana dan tazo muku da Chadian and Sudanese dilka Wanda zaki gyara jikinki da kanki, oga ya kasa ganeki, haka zalika akwai wata humrar ta mai suna hana bacci da kuma sirrin shuwa Abun ba magana, yar uwata ki jarraba turaren yar mutan borno nasan zata zame miki best turaren wuta plug. Tanada turarukan da zaki turara gida, toilet, bedsheets, curtains, kabbasa and hair incense ku jarraba kada ku bari ayi babu ku.
Wardrobe balls
Kabbasa spray
Chadian khumra
Hawee
Halud
Gabgab
Sandal sukkariya
Kajinguru
Dilka soap
Ready to use dilka
Karkar oil
Turaren tsuguno
Habil
Dorut
Dorot after period
Brown khumra
Dufr khumra
Body milk
Sudanese kuleccam
Chadian dufr kuleccam
Musk khumrah.
Maganin matan mu sunada inganci Wanda muke kawo su daga sudan, sannan munada maganin karin girman nono, Wanda basuda effects, ga masu bukatar maganin Matsi ko maganin mata Masu aiki garanti munada su, sannan muna zuwa gyaran jikin amarya a duk garin da take
Our Chadian aphrodisiacs are.
Beejay fire
Sata jagab honey
Wetness and sweetness combo
Daka
Great A sabaya
Breast engagement powder
Ciccibi
Gumbar madara
Gumbar dabino
Bita Zaizai
08093772168
*Welcome, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan number din 08103884440*~_____💞______💗_____💘_____🌹______💋_____💫_____🫀___~
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin kaninfari 1k Tsimin dabino 1k Gumba 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4k
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 maganin Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki.
)~_____🌹______🌹______🌹______🌹_______🌹~
Gaba ɗaya kowani ahali daga cikin su haka suka wuni da fargaban a wani hali yaran nan suke a ciki, tun jiya da dare ba ci ba sha, ruwan tea din da suka sha lokacin da suka yi nafilfili ne kaɗai ya rage a cikin su..
Abu kamar wasa har dare ya yi, babu labari dangane da su.
Hajiya layla da Alhaji Ubaid da mare ce suka bar gidan Owais sakamakon kiran da Hajiya Sarah take tayi masu game da rashin dawowarsu gida, kuma sun bar su cikin fargaba.
Kusan gaba ɗayansu suna a falo cikin damuwa, kowa ka kalli fuskarshi babu annuri bacci su ke ji amma damuwa ta hana baccin ya ɗauke su, sun kasa sun tsare suna jiran dawowar ƴa'yan su, Sheikh imam ne ke tausarsu da nasiha mai ratsa zuciya, Taj ne kadai baya a falo bai jima da fita ba, ya je ya kwantar da baby Junaid da ya yi bacci,