Showing 225001 words to 228000 words out of 319356 words
Chapter 76 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
jikin nata?"
Cikin karyayyar murya doc ɗin ya ce "Unfortunately, the patient's condition has taken a turn for the worse, Her blood cancer, specifically Leukemia has progressed rapidly, and we're seeing signs of severe bone marrow failure...." Salati Ummi ta zabga tare da ɗaura hannayenta saman kanta, Hajiya Sarah da ta zo da niyyar ta ɗauki fansar abun da ta yiwa ƴarta koda jin bayanin likita sai ta ji jikinta ya yi sanyi.
A ruɗe Chief Owais ya dubi ummi yana tambayarta dama tana da blood cancer? Cike da damuwa ta ce batasan komai game da ciwonta ba, in ma ta daɗe a jikinta bata ta6a faɗa mata ba, bata ma tunanin Natasha tasan tana da leukemia.
Doc ya katse maganar Ummi da cewa,
"We're doing everything possible to manage her symptoms and stabilize her condition, but I must be honest with you the prognosis is grim she's at high risk of sepsis, organ failure, and even cardiac arrest."
We're monitoring her closely and adjusting her treatment plan accordingly, but I want to prepare you for the worst, It's possible that we may lose her at any moment...."
Gaba ɗaya damuwa ta ƙara mamaye zuciyar su, Owais kamar yasan ba zata rayu ba ya yi dubarar zuwa da ƴa'ƴanta, kwata kwata ba su san gurin wa aka kawo su ba.
Shi ya ruƙo hannayensu a cikin nashi, ya shigar da su ɗakin, sauran ma duk suka shigo, Ummi ta zauna kan chair din gaban gadon, ta ruƙo hannun Natasha dake a kwance cikin mawuyacin hali, fuskarta asanye da oxygen mask da wasu na'urorin dake taimaka mata, Hajiya Sarah tana a tsaye daga bayan Ummi ta ƙura idanunta akan Fuskar Natasha tana tuna abubuwan da aka faɗa mata ta yiwa ƴarta, amma da ta tuna cewa Mahaifin Unaizah ne ya ja mata, hakan yasa ta ji zata iya yafe mata, musamman da ta ga halin da ta ke a ciki.
Da hannu Owais ya nuna mata Hajiya Sarah ya ce, "Matar Jan Wuya ce, Mahaifiyar Unaiza."
Zare blue eyes dinta ta yi, cikin ruɗu da razanar jin maganar shi take kallon Sarah.
Hawaye ne suka ciko idanunta, jikinta na kerma ta soma ƙoƙarin cire Oxygen mask ɗin fuskanta, da sauri Ummi ta dan ɗage mata shi kaɗan ta yadda zata iya yin magana.
Cikin shesshekar murya da gajarcewar numfashi Natasha taita kokarin furta ta yafe mata, ta yi nadama, ta yi danasanin abun da ta yi ma Unaizah, Musa ne sanadi, kuma hada ƙarin bata san wanene shi ba, da tun farko tasan manufar shi akan ta, da ba abun da zai hana ta kar6e ta, bata ta6a cutar da Unaizah ba, tana son ta, tana jin ta kamar ƴar da ta haifa, duk da tasan bata ba ta tarbiya ba, amma ta yi haƙuri tasan ta biyewa son zuciya, bata raini Unaizah yadda ya kamata ba..."
dakyar ta ke iya magana saboda raɗaɗin da jikinta ke yi mata.
"Who's she"? Gabriel ne ya tambaya.
A hankali Owais ya dube su, suna tsaitsaye bakin gadon hannunsu ruƙe cikin na juna.
"Mahaifiyar ku ce Sajeed, kamar yadda mahaifinku ya raba Sarah da ƴarta batare da saninta ba, itama haka ya rabata da ku bayan da ta haife ku, batasan kuna a raye ba..."
kallon juna suka yi cikin ruɗu da al'ajabi.
Sajeeda da ta gama ruɗewa ta ce, " Idan wannan ce mahaifiyar mu toh wacece ɗayar wadda ta raine mu?" Girgiza kai ta yi. "She'll never be our mom, I don't like her, she has no morals."
yayin da ta ke yin maganar Natasha tana kallonsu idanunta cike tab da ƙwallar baƙin ciki da takaici.
Sajeed ya ce, "Kunsa na ruɗe, tayaya wannan zata zama mommynmu? Bayan mommynmu tana nan, wadda ta haife mu ta kuma raine mu!"
Cikin rawar murya ta ce, "I know I don't deserve for you to call me Mother, Redneck betrayed me, separated you from me, I never knew I had you, but I want you to know it's not my fault Please forgive me, Forgive me..." Ta faɗa tana kuka.
"..Ku duba halin da nake a ciki, I'm not going to live, I want you to call me Mommy, just once, and hug me, I love you like my soul, I really wanna feel the warmth of your bodies against mine.."
ta ƙarashe maganar tana kuka ta dubi ummi, "Ku sanya baki, ku taimaka min, ina son su kamar raina, ina so na ji ɗumin jikin su.."
Cikin karyayyar murya Ummi ta dube su. "I'm sorry, As she said, it's not her fault, your father cheated on her and lied to her she didn't know you were alive, all she knew was that you died at birth, No one will love you as much as your mom, she carried you for nine months in her womb and labored, The one you're talking about is not your mother, she's his mistress"
Maganar Ummi ta yi tasiri a cikin zukatan su.
Owais ya ce, "Ku duba halin da ta ke a ciki, mu tausaya mata, bana so ku yi danasani daga baya.."
Cikin sanyin jiki suka matsa kusa da ita, Ummi ta miƙe tare da taimaka mata ta miƙe zaune, Sajeeda ta rungumo ta sosai cikin shesshekar kuka ta furta. "Forgive me, Mommy, but I love you, I don't want you to die, ina sonki, bana son ki mutu, Ina so mu rayu da ke, kada ki tafi ki bar mu..."
tsantsar ƙaunar su da son su ne ya mamaye zuciyarta, suma haka su ka ji son ta.
Bayan da Sajeeda ta raba jikinta daga na Natasha, ta matsa ma Sajeed shima ya rungumota tighly kamar zasu koma mutun ɗaya, "Tun da na ganki raina ya bani muna da alaƙa saboda na ji tsantsar ƙaunar ki a zuciyata, ban so muka haɗu a ƙurarren lokaci ba, amma za mu yi maki addu'a, Allah ya baki lafiya mommy, muna son ki fiye da yadda muke son kan mu, zamu baki kulawa mommy, zamu kasance a tare dake har sai kin ji sauƙi.."
Kukan farin ciki ne ya kubce mata, ta ƙara ƙanƙame shi, ta miƙa hannunta dake kerma ta tallabo Sajeeda ta haɗa su ta rungume a ƙirjinta, sautin koke koken su ya cika ɗakin.
Kowa da ke a gurin ya tausaya musu.
Sun daɗe a manne da juna babu mai lallashin wani sai daga bisani Ummi ta lallashe su ta samu ta shawo kan su.
A hankali Natasha ta mayar da dubanta ga hajiya Sarah dake ta share hawayen ta.
In a broken voice ta ce, "I didn't do you justice, I had the opportunity to meet my children, and you never saw your daughter until she died, I wish I could go down on my knees and ask you to forgive me, but I can't, my body is weak..." Tana magana twins ɗinta suna share mata hawayenta.
"Amma a madadin Unaizah da kika rasa, ga twins ɗina, na bar maki su har abada, ban cancanta na zama mahaifiyar su ba, na san ma bazan rayu ba, ki ruƙe su a gurin ki, na bar maki su.."
Cikin shesshekar kuka Sarah ta ce, "Na yafe maki Natasha, ba laifinki bane, laifin Musa ne, kuma shima yanzu haka yana a prison, Bazan kar6i ƴa'yanki ba bayan kina a raye, ki ruƙe abunki, babu wanda zai iya maye gurbin ki a gurin su..."
Girgiza kai Natasha ta yi tana ƙoƙarin buɗe baki da niyyar ta furta kalma, kwatsam suka ga ta fara jijjiga, numfashinta ya dinga kokawar ɗaukewa, ta dinga zubda gumi.
Cike da fargaba suke kallon ta cikin tashin hankali, Sajeed ne kaɗai ya yi tunanin biya mata shahada, gaba ɗaya suka shiga maimaita mata don sun fahimci ba rayuwa za ta yi ba.
Cikin kuka twins ɗinta suke faɗin kada ki mutu mommy, muna sonki, muna son mu rayu da ke, kar ki mutu ki bar mu a lokacin da muke cikin buƙatar ki!"
Sajeed da ya cire rai da ita bai daina furta mata shahada ba yana faɗin Mommy ki biya don Allah idan kika musulunta Allah zai yafe maki zunubanki, kuma muma zamu sa mu yi maki addu'ar samun rahama..." Da ƙyar da siɗin goshi suka samu Natasha ta biya shahada da numfashinta na ƙarshe.
Alƙalamina bazai iya misalta muku raɗaɗin da twins ɗin Natasha suka ji ba na rashin mahaifiyar su, bayin Allah sun zama abun ban tausayi a ranar da suka fara ganin mahaifiyar su a ranar ta mutu, Musa ya cuce su, wata shari'ar sai a lahira.
Ummi ta yi kukan rashin Natasha, Chief Owais ya yi danasani da tun farko bai yi saurin haɗa ta da ƴa'yanta ba, hatta hajiya Sarah saida ta zubda mata ƙwalla saboda tausayin ƴa'yanta da ta bari. A ƙarshe Hajiya Sarah ce ta kar6i twins ɗinta da hannu bibbiyu.
😭😭😭
~_________________________________💔~
Haƙiƙa dangin baba Obie sun fuskanci jarabawa mafi tsanani a rayuwar su.
Mutane saida suka hana Ahlin Obie sukuni, har ta kai ga basu iya buɗe wayoyinsu ko su fita waje batare da ƴan jarida da mutane sun farmake su ba, gaba ɗaya fita ta gagare su, suka killace kansu a cikin Estate ɗin su, saboda surutun mutane da masu barazanar lahanta su.
Sun fuskanci barazana da tozarci daga gurin abokan hamayyar su na jam'iyoyin da ke adawa da su.
Duk wanda ya ra6e su sai laifin baba Obie ya shafe shi, hakan yasa abokan su ƴan siyasa suka dinga zame jiki daga gare su, kowa tsoro ya ke kada su shafa mashi baƙin tabo, babu irin 6atancin da ba a yi masu ba, cin mutunci da ƙazafi iri iri ba wanda ba a yi masu.
Surukansu suka fara ƙoƙarin yanke alaƙar su da su, waɗanda suka fi ɗaukar zafi, mahaifin Her Excellency Muhibbat da yake jan wuya ne babban mutum ne, bai son duk wani abu da zai ta6a mutuncinsa, tun a ranar da Muhibbat ta kira sa tana kuka ta bayyana masa komai da ke faruwa ya ce ta dawo gida babu ita ba Abdul Razak, ya yanke alaƙar su, da yake halinta ɗaya da na Ubanta bata musa mashi ba, duk da tana son mijin nata amma ta biyewa mahaifinta, batare da sanin kowa ba ta gudu daga Obie estate ta tafi gidan Ubanta da ke a nan Abuja.
Her excellency Jameela ma a ranar da suka ji komai, ta koma gidan ubanta mai martaba sarkin Adamawa saboda tsoron kada abun ya shafe ta duk da itama bada son ranta ba, su dukansu ma babu wadda ta yi hakan don son ranta, saboda suna son mazajensu da ƴa'yansu, amma ba yadda suka iya, baba Obie ya karya zukatan su, ya ha'ince su ya kuma ci amanar su, ya yaudari yardar da suka yi ma shi, da suna alfahari da kasantuwar su surukan shi yanzu ya 6ata komai, abun da ya fi ƙona masu rai, jariran su da ya dinga sadaukarwar, shi yasa ransu ya 6aci suka zuciya.
A yanzu ƴa'ƴan Obie sun gane waɗanda suke tare da su saboda Allah, da waɗanda suke tare da su saboda arziƙinsu da kuma ɗaukakarsu.
_Ba zaka ta6a gane me sonka tsakani da Allah ba har sai musiba ta afka maka a sannu zasu dinga guduwa suna barinka_
Senate Lateef bai samu matsala da Hajiya Madina ba, mahaifinta malamin addini ne koda ya ji komai da ya faru daga jiharsa ya zo har Abuja ya ziyarce su don ya yi masu jajen abun da ya faru da su, ya kuma haɗa da yi masu nasiha akan su yi haƙuri kada su sare Allah yana a tare da su a sannu komai zai zama labari..
Hakan ba ƙaramin faranta ransu ya yi ba. Baiwar Allah Turai bata bari ta karya zuciyar mijin nata ba, sai ma lallashin shi da ta dinga yi tana kwantar masa da hankali saboda ganin halin damuwar da ya shiga.
Sharafudeen bai samu matsala da Gimbiyarsa ba saboda ita ɗin jininsa ce, abun da ya shafi family ɗinsa ya shafe ta.
A bangaren Prime minister Hateem tabbas iyalinsa sun girgiza da jin abun da baba Obie ya aikata amma basu bari sun baiyana damuwar su ta yadda zai karya zuciyar Hateem ba, Gimbiya Mujeedat ta yi jarumta gurin danne damuwarta da kwantar masa da hankali, wallahi kowa ya yi tunanin Sheikha Mujeedat ce ta farko da zata fara neman yanke alaƙa da su saboda martabar royal family ɗinta amma sai ta basu mamaki, ta ja mijinta a jiki, ta nuna ta ƙara jin ƙaunarsa da tausayinsa, kuma ta ce in ma yana tunanin zata juya masa baya to ya daina, bata aure shi don su rabu ba face don su rayu na har iya rayuwar su, don haka laifin babansa bai shafe shi ba, kuma ba zata bari mijinta da ahlinsa su tozarta a idon duniya ba, zata bada gudummuwarta don ganin mutuncinsu bai zube ba.
Gimbiya Mujeedat ta ƙarfafa masu ta kuma basu mamaki sosai, sai dai Hateem bai samu nutsuwar zuciya ba, saboda yasan yadda royal family suke, sun ƙi jinin abun kunyar da zai zubar masu da mutuncin su a idon duniya.
Yana ta jin fargaban kada iyayenta su neme shi, Unexpected sai ga kiran mahaifin Mujeedat, Emir Khalid ya shigo wayar Hateem da kan shi ya kira shi ya ce ya ji abun da ke faruwa a family ɗin su, ya zo ya same shi a fadar shi yana son ganin shi.
Tun da suka yi wayar nan kwanciyar hankali ya ƙarewa Prime minister saboda zullumin me zai biyo bayan kiran nasa, don wlh ji yake zai iya barin komai har muƙaminsa amma ba zai iya rabuwa da Mujeedat ba, koda za a kashe shi ne, saboda tsantsar son da yake mata.
Abu biyu ya haɗe mashi, ga gwamnatin ƙasar Canada suna jiran dawowar shi, don har ya zarce kwanakin da ya ɗiba, sun ji shiru ko sun kira baya picking kuma ba ya basu response na saƙonninsu.
A lokacin duniya ta ji komai da ke faruwa da ahalinsa, amma gwamnatin kasar Canada da ƴan ƙasar sun fi so su ji daga bakin shugaban ƙasar nasu.
Da ya ga bashi da wata mafita, ƴan uwansa suka bashi shawarar ya yi magana da Deputy ɗinsa in ma mulkin zai ajiye sun goyi bayan shi don sun san a halin yanzu ba lallai gwamnatin Canada ta bar shi ya ci gaba da yin mulki ba saboda abun kunyar da mahaifinsu ya aikata.
Live video ya yi a presidencial page ɗinsa tare da press, ya bayyana masu halin da ya ke a ciki ya ce su yi haƙuri da abun da zai faɗa, yasan ba lallai hukuncin da zai yanke ya yi masu daɗi ba, amma a yanzu ya yi raunin da ba zai iya ci gaba da shuwagabancinsa ba, kuma ba zai iya dawowa Canada ba, saboda ba zai iya tafiya ya bar ƴan uwansa a cikin mawuyacin hali ba, don haka su yi masa afuwa, su nemi wani adalin shugaban da zai maye gurbin sa... "
Wannan Live video ɗin da prime minister ya yi da manema labarai cikin ƙanƙanin lokaci ƙasar Canada ta dauka, labarin murabus ɗin sa ya tayar da tarzoma a duk faɗin kasar Canada, kuma mutane da dama sun yi baƙin ciki da matakin da ya ɗauka kuma sun nuna ƙin amincewar su, haka zalika mutanen da ke kula da shi a tsawon wa’adin mulkinsa sun ƙuduri aniyar shawo kan shi don ya koma Canada ya ci gaba da aikinsa saboda su basu gaji da shi ba, bayan haka bai yi laifin da doka zata amince da yin murabus ɗinsa ba, laifin mahaifinsa bai shafe shi ba, har yanzu suna son shugaban ƙasar su.
Bayan da yayi wannan Live video ɗinne, ƴan uwansa suka ƙarfafa masa gwiwa akan ya amsa kiran surukinsa, bai yi ƙasa a gwiwa ba, ya bar ƙasar tare da iyalinsa, tafiyar sirri suka yi saboda jama'a dake neman su farmake su ruwa a jallo.
Abun da ya ƙara sagar masu da gwiwa rashin tuntu6ar su da Familyn mahaifiyarsu ba su yi ba, a zaton su sune mutane na farko da ya cancanta su ja su a jiki su lallashe su akan mummunar ƙaddarar da suke fuskanta amma sai suka ji shiru daga 6angaren su, hakan ba ƙaramin karya masu zuciya ya yi ba, duk sai su ka ji ba daɗi, suna ganin kamar suna gudun su ne saboda kada martabar family ɗinsu ya rushe, gashi kuma su ne kaɗai dangin da suke da shi a duniya.
Saida damuwa ta kusa illata su, gaba ɗaya suka yi murabus daga kan muƙaman su saboda depression da suke fama.
A lokacin da gwiwarsu ta sage, suka raunata, basu da madogara da ya wuce Allah da Sheikh Imam dake zaryar zuwa yana ƙarfafa masu gwiwa, sai da suka fidda rai da komai, a wannan Lokacin ne kuma Allah ya juye al'amarin yadda basu ta6a zata ba.
Dangin da suke ta jira su ji daga gare su suka yi masu zuwan bazata, gaba ɗayansu, tun daga kan kakanninsu na 6angaren Uwa, tsohon sarkin ƴarbawa, har izuwa kawunnan su, da yayan mahaifiyarsu mai martaba sarkin ƴarbawan jihar Lagos mai ci a yanzu gaba ɗayan su, suka zo Abuja a cikin family private jet ɗin su tare da royal guards ɗin da ke basu kariya.
Tun a airport ƴan jarida suka dinga dandazo gurin neman ƙarin bayani daga gare su, sai dai ko kusa da su basu isa su ƙarasa ba, saboda royal guards ɗin da ke a kewaye da su.
Kuma duk a rana ɗaya Edward's family na bangaren mahaifiyarsu Hateem suma suka zo Nigeria, kowa yasan irin power ɗin da ke gare su, sune ake ma laƙabi da jinin siyasa, they are famous politicians tun kaka da kakanni.
Sun ji komai da ya faru daga bakin Momma da ta kira yayanta ta sanar da shi, family ɗinta sun girgiza da jin tana a raye, sun kuma fusata da jin zaluncin da mijinta ya yi mata, basu ta6a zaton haka daga gare shi ba, hakan yasa suka yi takakkiya tun daga Canada suka zo Nigeria a family jet ɗin su.
Silar zuwan su abubuwa da dama sun faru, haƙiƙa Ahlin Obie sun yi farin ciki da zuwan dangin iyayensu mata, sun zo a lokacin da suke a mawuyacin hali, a kuma lokacin da suka yanke ƙauna da komai na duniya, waɗannan powerful families ɗin guda biyu suka haɗa kansu, suka tsaya masu tsayin daka, suka zama ƙashin