Showing 291001 words to 294000 words out of 319356 words
Chapter 98 - ZINARE Book 1 Complete Hausa Novels by Nafisa Aliyu Salsal.txt
domin ya halarci family Meeting, hakan na nufin ko su Nazli basu san komai game da Omair ba.
A lokacin ta shiga damuwar tayaya zata tafi tabar danta dake bukatar kulawarta duk da akwai maids dake kula mata da shi.
Badan taso ba, Ta damƙa musu amanar shi, taja kunnansu sosai akan su kula mata da shi! Ranar kamar kar su rabu, ya rurruƙeta har bakin motarta da kyar ta shawo kan shi Yabarta ta tafi..
Daga guest house dinta ta wuce Zabeel palace the ruler's resident, kwana biyu tayi kafin su ka shirya tafowa Nigeria ita da Yazrin da Nazli.
Bayan da suka bar ƙasar, cikin ma'aikatan gidanta, aka samu wani munafuki Yaje har fadar Emir ya kai masa tsegumin Yaron da Mujeedat ta ke boyo agidan ta, ta bayan fage, Emir Khalid Ya turo Royal guards don su Binciko masa wanene yaron da ta ke boye"?
Ranar da guards suka zo palm Jumeira cikin guest house ɗin mujeedat, guards dinta na ganin su suka basu iznin shiga saboda sunsan Emir ne ya turo su.
A lokacin Omair Yana a zaune kan dining Chair, Chefs sun kewaye shi, ga abinci sun jera mashi akan table, sunata lallashin shi don yaci abinci yaƙi ci sun rasa gane meke damun shi, ko magana bai yi masu tun bayan da Shiekha ta tafi! basu san kewa bace ke damun shi..
Sa'ilin da Royal guards din suka shigo dining din
Wata razana su ka yi da ganin Omair, su ka ruɗe saboda ganin kyakkyawan matashi mai kama da jiƙar Emir.
Cikin sauri ɗaya daga cikin guard ɗin ya ɗauke shi hoto da wayarsa Ya tura ma Emir duk Fa Yana kallon su a lokacin baisan su wanene ba bai kuma san meya kawo su ba.
Ba'ajima da tura masa hoton ba sai ga kiransa bayan guard din ya yi picking Emir Ya Umarce su da su tabbatar sun tafo mashi da lu'u lu'un nan, Yana son ganin shi a cikin fadar shi"!
Bayan guard din Ya gama yin wayar da Emir, suka Umarci Omair daya taso su tafi fadar mai martaba Khalid Yana son ganin shi.
Rashin sani Yafi dare duhu, Omair baisan wanene mai martaba ba balle yayi musu biyayya ya bisu, hasalima ko kallo ba su ishe shi ba.
Tun suna bashi Umarni yana share su, har suka fara haɗa baki gurin yi masa tsawa akan Ya taso su tafi, kai a karshe da su ka ga yaƙiya sai suka kama lallashin shi..
da sukaga dagaske bazai bisu ba, sai suka fara ƙoƙarin ɗaukarsa ta tsiya, aikuwa Ya fara naɗe hannuwan rigarsa zai yi dambe da su, wayaga Iliya ɗan mai ƙarfi.
Koda Chefs suka fahimci me Ya ke shirin yi cikin sauri ɗaya daga cikin su tayi masa magana cikin harshen turanci tace mashi royal guards ne daga ruler's resident na dubai, kuma mahaifin Sheikha Mujeedat ne sarkin su sannan shine Ya turo su, kada yayi faɗa da su yayi musu biyayya su tafi ba cutar da shi zasuyi ba.
Kasa fahimtarta yayi har saida ta kira sheikha Mujeedat ta faɗa mata abun da ke faruwa, tayi mamakin jin baban ta ya turo guards har guest house dinta don su tafi da Omair, amma bata damu ba nan take Ta umarce ta da ta bashi wayar suyi magana, bayan hadimar ta bashi wayar ya kar6a ya kara a kunnansa ta fayyace masa alaƙarta da mahaifinta tace karyaji shakku aranshi, Yabisu su tafi zai fi samun kulawa agurin daddyn ta.
Bayan da suka kammala wayar ne, ya bi Royal guards din suka buɗe mashi mota Ya shiga ya zauna, suka tada motocin suka fuce daga guest house din ta..
~___________________________________💋🌹~ Zabeel Palace 🔥
Fadar Zabeel hadaddiyar daular arziƙi ce dake a cikin daular larabawa, kuma Babban mazaunin Sheikh Khalid, mai ɗumbin tarihi da ikon, tana a tsakiyar Dubai, katafariyar Palace din tana a kewaye da kyawawan lambuna, tafkuna, da maɓuɓɓugan ruwa, ga dogayen bishiyin dabino, ta haɗu karshen haɗuwa, Alkamina bazai Iya misalta maku ƙawatuwar Katafariyar daular ba, Aljannar duniya, abun sai wanda ya gani
Tun daga katafariyar main entrance zaka fara cin karo da Royal security Guards karfafa masu kirar Zakuna..
Bayan da Motocin suka karaso, a harabar ajiye motoci suka yi parking, lokacin da Danish ya fito daga Motar, ya ruɗu da ganin haduwar ginin kamar a mafarki Ya ke jin kanshi..
Guards ɗin ne su ka yi escorting din sa zuwa ciki
tun shigowarsu Royal Guards suke ta Zare ido suna kallon shi, duk inda ya gifta idanun su akan shi haka da suka shiga ciki Hadimai da sauran jama'ar Fadar suka dinga binshi da kallo mai cike da tsantsar Al'jabi..
Har cikin Katafariyar Fadar Emir Khalid suka shiga da shiga, Fadawansa na ganin sa Suka zare idanun su cike da al'ajabi suke bin shi da kallo, Abunka ga wanda baisan takan Fadar Emir ba, maimaiko Ya zauna saiya Tsaya a tsaye ƙiƙam kamar gunki ko fara'a babu akan fuskarsa babu ladabi babu biyayya, Emir Khalid Yana zaune kan throne dinsa Cikin shigar sarakunan labarawa Na alfarma, Ya nutsu Yana kallon sa.
Cikin harshen larabci fadawan suka dinga umartar shi daya zuƙunna Ya miƙa gaisuwa gurin Emir.
Ko kallo basu ishe shi ba, har saida Emir Ya miƙa masa hannu alamar Yazo gurinsa tukunna Ya nufesa ba tare da jin fargababa, da ya ke yaga kamanninsa da Gimbiya mujeedat kamar yayi kakin ta.
Ruƙo hannunsa yayi a cikin nashi ya rungumosa Yana shafa bayansa..
Karo na farko daya fara ganin shi, duk da baisan wanene shi ba? Menene alaƙarsa da Yarsa Mujeedat? Amma kamanceceniyarsa da surukinsa Hateem da jikarsa Nazli Ya sa ji aransa zaiyi wuya in ba yaron jikansa ba ne duk da yasan Mujeedat bata da ɗa Namiji.
Bai ta6a jin tsantsar ƙaunar bare farat ɗaya a kallo ɗaya makamancin yadda yaji akan Omair ba, Bashi ba Hatta fadawansa sun kamu da kaunarsa, Kyawunshi Ya ruɗe su su da suke larabawa jinsin kyawawa, duk yadda suka kai ga ɗokinsa da jan shi a jiki sai dai sun kasa yin magana da shi saboda Yaƙi basu hadin kai, da Emir kaɗai Ya yarda shima albarkacin mommynsa ya ci.
Daga Palace Emir Ya shiga da shi Cikin gidan, Zo kuga Yadda Royal Family mutane masu ƙima da daraja su Ke kallon Omair kamar zasu haɗiyesa saboda ruɗewar da su ka yi da kyansa da kuma kamanninsa da Nazli.
Kowa Saida Ya hallara Dangin su, tun daga kan Grandparents, parents, Uncles, aunts, elders, kowa da kowa, kyawawan labarawa wadanda suka gaji Sarauta da arziƙi na fitar shari'a..
Kowa Tambaya ya ke yi wanene kyakkyawan matashin saurayin nan? ɗan wanene? daga Ina Ya ke? Wasu ma daga cikin su tambaya su ke yi mijin sheikha Mujeedat yana da wata matar ne da ta haifa masa Yaron ko kuwa Nephew dinsa ne (dan dan uwansa).
Emir ne ya fayyace masu abun daya sani game da Omair, Ya daura da cewa su yi hakuri zuwa lokacin da sheikha Mujeedat zata dawo daga Nigeria, zata fada musu wanene shi, amma Yanzu Yana so kowan nan su Ya ja shi ajiki, su bashi kulawa kamar yadda suke kula da sauran ya'yan sheikha Mujeedat saboda yana ji aranshi da akwai wani abu game da yaron tun da har take 6oyen shi a guest house din ta.!
kunsan larabawa da girman kai musamman ga bare amma dayake Omair ya kwanta musu arai sun ganshi da abubuwan ban al'ajabi atare da shi shiyasa su ka yi saurin amince ma shi.
Omair bai ta6a sanin Yana da babban Family na hamshaƙan masu kuɗi ba kuma kyawawan gaske sai da Ya tsinci kanshi a cikin ruler's resident na dubai, ashe shi din ɗan dangine, Ya fito daga tsatson mashahuran larabawa.
Kowa ɗokinsa Ya ke yi, amma Rashin sabo ya hana shi sakin jiki da su.
musamman Emir Ya ware masa katafaren Bedroom dinsa tare da Hadiman da zasu dinga yi ma sa hidima, in a short time Emir Ya siye zuciyar Omair, shine mutun na farko daya fara sakin jiki da shi, saboda kyautatawar da ya ke yi masa, Har takaiga dare kaɗai ke raba su, ya zama kamar ɗan Cikin sa, In zai shiga Palace a tare suke zuwa, su ci abinci atare da shi da iyalansa su fita yawon shaƙatawa, Hadiman Gidan sun sanya mashi ido sosai, kunsan ba'a raba hadimai da tsegumi burinsu kawai su ji wanene shi"?
Daga bisani Lokacin da Asirin kurkukun ƙaddara Ya Tonu duniya Taji, sa'ilin da labarin Ya risƙi Familyn Mujeedat, sun razana sun kuma shiga tashin hankali da jin wanene surukin su Obinna, Ransu ya 6aci matuƙa, Baba Obie Ya Karya musu Zuciya, Ya ci amanar yardar da su ka yi ma shi, sun kuma fusata sosai, sai da su ka yi dana sanin ƙulla alaƙa da shi saboda basu son abun da zai ta6a mutuncin su duk min ƙanƙantar shi, suna girmama mutuncin su fiye da komai.
dama tunfil azal basu so sheikha ta auri bare ba kuma baƙar fata ɗan Nigeria saboda su a ƙa'ida basu fiye auran bare wanda ba jinsin su ba, abaya lokacin da Mujeedat tazo da Hateem amatsayin wanda takeso ba karamin rikici akayi a family din ba, duk da matsayinsa da arziƙinsa Yasha wahala kafin su bashi auranta, saboda ta rantse ta maya bata da miji a duniyar nan daya wuce Hateem, mahaifinta ne mutun na farko daya fara goyon bayan ta auri za6inta saboda tsantsar son da yake mata fiye da sauran ya'yansa ita kaɗai ce mace kuma autar sa, mahaifiyarta ma ta goyi bayanta, daga bayane kuma bayan sunyi aure Dangin nata suka Fara son Hateem saboda yadda Al'umma su ke yabon kyawawan halayansa.
saboda fallasuwar asirin Obie Har Family meeting su ka yi game da Yanke alaƙarsu da surukinsu, Mafi rinjayen su wadanda su ka fi fusata, sun goyi bayan a kira Hateem Ya saki sheikha Mujeedat, Kaɗanne basu goyi bayan yin hakan ba, daga ciki hada Mahaifinta da kawunta da kuma yayanta sun ce sai dai A kira Mujeedat tazo Nigeria suji ra'ayinta in har ta nuna tana son taci gaba da zama da mijinta babu abun da zaisa su raba su.
Haka wasu daga cikin fadawan Emir Khalid sun shawarce shi da ya yanke alaƙarsa da obinna saboda gudun surutun mutane amma Ya tsawatar ma kowa akan shi bazai Raba Mujeedat da mijinta ba, In har ba itace ta nuna tana son rabuwa da shi ba
Komai da ke faruwa a family dinsu gimbiya Mujeedat bata sani ba, Ta kashe wayarta saboda rashin kwanciyar hankali da damuwa.
Daga baya ne Emir Ya tuntubi Prime minister awaya, Ya umarce shi dayazo Yana son ganinsa, Idan masu karatu ba su mantaba akwai wani kira da Emir yayiwa Hateem Har yaji shakkar zuwa saboda zullumin kada Su raba shi da matar shi, to abun daya faru bayan ya amsa kiran, suka yi tafiyar sirri zuwa dubai tare da Iyalinsa.
Bayan sun isa Airport Royal Guards suka zo Daukarsu a motoci, kaitsaye suka garzaya da su zuwa Ruler's resident, a lokacin Hateem Bashi da nutsuwa, zullumi da fargaba sun cika zuciyarshi Ya damu da fargaban meyasa Surukinsa ke nemansa? yasan Sun riga da sun ji komai a news, kuma yana da tabbatacin kiran da ya yi masa yana da alaƙa da Abun da ke faruwa a family din su..
~______________________________~
Kwata kwata Hateem baisan Danish Yana a tare da dangin mujeedat ba, saboda a lokacin baida kwanciyar hankalin da zai iya tunawa da shi, bai kuma san komai game da kasantuwar sa ɗan shi ba.
Bayan da suka Ƙarasa hateem bai samu tarbar daya saba samu agurin wasu daga cikin danginta ba.
hakan ya ƙara haifar masa da matsananciyar damuwa, ta inda ya ji sanyi aransa Emir da Kawun mujeedat da Yayanta da ma wasu daga cikin su sunyi mashi kyakkyawar tarba, a bangaren Sheikha Mujeedat da ke a cikin gidan suka fara huce gajiyarsu, bayan hadimai sunyi masu hidimar kawo abinci daga bisani bayan sun huta sosai, sai ga kiran Emir ya shigo wayar Mujeedat bayan ta ɗaga yace su shigo ciki yana son ganin su.
Gaba ɗaya suka ɗunguma izuwa Private Living room, A nan suka Iske Kowa na familyn sun hallara suna jiran su.
A lokacin ba Hateem kadai Ya shiga damuwa ba, hada Mujeedat da Su Nazli, saboda sun san mawuyacin abune su ƙyale Hateem batare da sun raba alaƙar su ba.
Cikin zullumi da fargaba suka zazzauna suna fuskantar Emir khalid da sauran family members din.
Falon yayi shiru babu mai magana, Hateem Ya sadda Kan shi ƙasa cike da jin kunyar hada idanu da su, gimbiya Mujeedat ce ke ɗan tausarshi Tana matsa yatsun hannunsa dake a cikin nata duk dan ta kwantar masa da hankali.
Gyaran murya Emir yayi, Hankalin kowa Ya dawo kan shi, cikin nutsuwa ya ce sunji komai da mahaifinsa Ya aikata, basu ji dadi ba, Ya karya musu zuciya, ya kuma ja masu abun kunya a idon duniya, amma ba zasu alaƙanta shi da laifin da mahaifinsa Ya aikata ba, hakika sun tausaya masu sun kuma jajanta musu, sai dai ya sani bazasu lamunci abin da zai taba martabar family din su ba..."
Lokacin da Hateem ke sauraronsa Hankalinsa Idan yayi dubu toh Ya tashi.
Emir Yana ƙare maganarsa, Khal din Mujeedat Ya daura da cewa"don haka, yayi hakuri da hukuncin da zasu Yanke! Sakamakon Mafi rinjayen family dinsu sun fusata sun nuna rashin goyan bayan alakar sa da mujeedat..."
khal bai ƙare maganar tasa ba, Mujeedat ta fashe da kuka Hankalinsu Ya tashi saboda sun daɗe basu ga zubar hawayenta ba, Cikin karyayyar murya tace kada su rabata da Hateem! Bazata iya rayuwa batare da shi ba, tayayama zata iya barin shi a mawuyacin halin da ya ke a ciki? Dame zaiji? Su dubi girman Allah kodan darajar ya'yan dake a tsakaninta da Hateem kar su rabata da shi, zata iya rasa ranta su tausaya mashi!"
duk yadda Nazli takaiga izza saida ta sanya baki ita da Yazrin suka taya mommynsu rokon danginta akan kada su raba su da mahaifinsu, ba laifinsa bane, ko Allah baya kama mutun da laifin da bashi ya aikata ba, su tausaya masu! In kuma har suka raba mommynsu da daddynsu suma zasu yanke alaka da su, saboda bazasu taba rabuwa da daddyn su ba.
maganar Su Nazli ta ɗaga hankulan su, saboda suna son su kamar ran su amma still basu canza ra'ayin su ba..
Khalar Mujeedat tace ba zasu taba canza ra'ayin su ba, dole Sheikha ta za6a, ko dai Ta rabu da Hateem ta rayu da danginta, ko kuma taja ma kanta itama su Yanke alaka da ita.
Hateem baisan sa,adda hawayen bakin Ciki suka wanke fuskarsa ba, sam Ya kasa magana sai dai jinjina kansa da ya ke yi.
Daƙyar ya iya buɗe baki, cikin girmama yace baiga laifinsu ba, bai kuma ji zafin hukuncin da su ke so su Yanke mashi ba, mahaifin shi ne yaja ma shi! amma bai ta6a zaton jin hakan daga gare su ba, a matsayinsu na musulmai masu ilmin musulunci, sun san komai ya faru da shi mukaddarine daga Allah, bai kamata su juya mashi baya don mummunar kaddara ta same shi abun da ya faru da shi zai iya faruwa da kowa haka Allah ke jarabtar bawansa ta inda bai zata ba! amma kafin su fara yanke hukuncin raba shi da matar shi, yana neman alfarmar su akan su ba mujeedat za6i tun da tana da Ƴan ci, ta faɗi ra'ayinta akan alaƙarsu, saboda bazai ta6a sakin ta ba, kuma bazai rabu da ita ba, In har ba ita da kanta ta nemi ya sake ta ba, idan kuma su ka ce zasu tilasta masu, zai sanya lauyoyinsa a ciki.
lokacin da ya yi maganar zuciyarsa a wuya ta ke, yana jin zai iya komai akan Mujeedat..
Gaba ɗaya sun kunna masu wuta babu wani sassauci so su ke kawai su raba su.
A Lokacin da Hateem Ya sare da rokonsu akan su janye maganar raba su, Cikin fushi da 6acin rai ya miƙe cike da rashin kuzari Ya juya da niyar yabar falon harya fara tafiya, Unexpected Ya tsinkayi Muryar mutum a kunnanshi Yana kiran shi da sunan daddy minister...
A sukwane ya dakata da yin tafiyar, Ya kasa motsawa, cikin ruɗu ƙwaƙwalwarsa ke kokarin tariyo masa muryar wanene Yaji a cikin kunnansa? Wanene me irin muryarsa? Wa kuma ya ke kira..."?
Bai ƙarashe zancen zucin nashi ba Ya kuma tsinkayar muryarsa a karo na biyu yace"daddy minister, it's me Danish.. "
Gabansa ne Ya faɗi a ruɗe Ya juya ya fuskanci inda Yake jin muryarsa kaitsaye idanunsa suka sauka akan Danish dake a tsaye sanye cikin shigar larabawa, kasa yarda yayi da abun da idanunsa ke nuna masa, ganinsa ya ke kamar a mafarki, Ya soma murza idanunsa da yatsunsa don ya tabbatarwa kansa daidai yake gani.
Nazli da Yazin Tun fitowarsa suka hango shi, A rude suka miƙe tsaye kan kafafunsu suna bin shi da kallo mai cike da al'ajabi, ganin matashin saurayin da suka ta6a gani a farewall dinner din daddynsu, ba zasu taba mantawa da fuskarsa ba, musamman Nazli, cos a farko data fara ganinsa Taji kishi sosai saboda arayuwarta batason mutum me kama da ita, batason ace wani nada wani abu irin nata, saboda tsabar izzar ta, a lokacin abun daya ɗaure masu kai tayaya akai Yaron da yake a Nigeria ya zo dubai? kuma har cikin gidan family din su? Tayaya hakan zai yiwu? Wama ya kawo sa? Menene alakarshi da su?
Sheikha mujeedat ce kaɗai bata motsa daga inda take ba, saboda tasan komai game da zamansa a gidan su.
_Gaba ɗaya babu wanda yasan da zaman shi a falon, amma tun farkon da suka fara tattaunawa ya fito daga dakinsa da niyar ya tafi fadar Emir yana shigowa falon idanunsa suka hango mashi Mommynsa da Prime minister wani iko na Allah kallo ɗaya da yayi masa nan take ya tuna da komai daya manta, hakan nufin memory dinsa daya rasa ya dawo, yayi farin cikin sake ganin Prime minister musamman dayasan cewa daddynsa ne, to anan yaji komai da suke tattaunawa hankalinsa Ya tashi da jin zasu raba mommynsa da daddynsa_
Cikin rawar Murya Prime minister Ya furta"Danish! Kaine dagaske nake gani? Ko dai idanuna ne suka nuna min badai dai ba"?
bai ƙare maganar ba, Danish Ya nufe shi da sauri yana isa gabanshi ya rungume shi sosai cikin farin ciki da murnar ganinsa.
Babbar magana! Kallo