Showing 51001 words to 54000 words out of 110493 words

Chapter 18 - Ja Ya Fado Ja Ya Dauka Complete Hausa Novels By Zainab Makawa

Saida Man Bashir ya dawo shine ya dawo damu ba yadda zatayi don kamar tana tsoronsa kuma fa dashi Salman dash Abu dayane iyayyensu son kawai dai shi salman ya fito a gidan maluntane alma duk da hakan ba tayi masa kallon daraja a idonta.

Balle ni da tasan iyayyena a Barga suke zama cikin fadawa ai banda ko digon daraja a idanunta kawai su ahalin daddy ne kawai suka fita daban a cikinsu.

Auwal ai gaskiya ta fada ina ni ina Man Bash dama ai kowa yasan yafi karfina kawai dai haduwan mu dashi gamon jinine na dauka amma bawai nakai level din da zan tsaya dashi bane.

Balle har suyi zargin ko ina soyayya dashine ko wani watsewa don kawai ina yar tallakawa Auwal zaisa su dauka banda gata ko tarbiya shin laifine don nazo duba wanda ya damu da damuta sai hakan ya zamo laifi a wajensu na dauka kana kula wanda ya damu da naka ne ai.

Kar kice haka Aeesha donsu a zaton su soyayya kukeyi da Man Bashir zama dake zaki iya hana ya auri yarta kamar yadda suke fatan hadusu bakiji meta fada a cikin zancen ta ba.

Shiko a yadda na san sa yana da wuyama ya auri yar nata kamar yadda suke fatan hadasu auren don banga alaman wani kaunanta ba gareshi.

A school dinku take itama amma ko sau daya kin taba ganin ya tsaya kulata balle yasan da tana nan sudai me sukr haukansu kawai a kan sa don sam bai zancenta da kowa.

Idona na lumshe tare da cigaba da tunane ina duban sakamako wanan wani irin abune shiya akeson musulmi da biyayya ga ubangiji da manzonsa akan duk abinda suka hani bawa dayi don rashin yinsa yafi sauki ga bawa akan ya aikata abin ki din.

Don yanzu gashi ni da banji ban kuma gani akarshe nice da uwayen rikona muke girban wahalan dake cikin hakan duk da Abbu yana kan jadda min ni din ba shegiya bace ina da ubana saidai balarabene kuma ba,an inda yake ba.

Yanzu mai gari ya waya agareni sunan ina da uba wazai taba yarda da hakan cewa ni mai ubace wai tunda ba,aga uban nawa ba a zahirance ?

Hakan dole na nufin bandashi ke nan tunda ko kudi aka zube babu mai kawo uban nawa yanzu kawai makomana da mara uba yanzu dayane.

Bansan lokacin dana fashe da wani irin kuka ba mai tsuma rai da yasa Auwal cin burki da sauri yana tambayana ko lafiya karshe dai ya samu wuri ya packer motar ya shiga lalashina fita yayi zuwa wajen wani shago ya also min goran ruwa ya kawo min wai insha.

Kai na girgiza masa alaman ya barshi yace karbi ki wanke fuskanki dashi to kada ki shiga mutane a gane kinyi kuka.

Zancensa gaskiyane dole na karba din na Dan sauke kafata ta waje na wanken fuskan nawa da ruwan kana na danji sauki ina ajiyan zuciya.

Auwal din yana tsaye cikin damuwa da nuna kulawansa akaina kafin yace dani mu tafine ?

Na gyada masa kai a hankali alaman eeh yana tsaye saidana zaune ya rufe kofan ya zagayo ya shiga ya tayar da motan saida muka kai kamar five second a motan ba wanda yai magana kafin can inji yace addua da sadaka ya kamata kiyi Aeesha.

Addua yana kau da komai ga bawan daya yarda Allah shikeyi a duo lokacin da yaso sai kiga abin yazo maki a cikin sauki ba anbinda ya gagari ubangiji matsawan ka dogara gareshi.

Can kamar ba zan yi magana ba sai yaji nace Auwal tawa kaddaran ta riga data faru a kaina ko gaskiya suka fada Auwal dan asali sai yar asali nima rigimace yasa nayi saurin yarda da malam a yanzu.

Don matsayina baikai ga ko dan tallakansu ba ballesu diyan sarakuna masu kuma fada aji a gari irinsu komai sun hada a wajensu ilimi sarauta kudi mulki duo akwaishi wajensu .

Inani ina gwamatsuwar irin wanan ahalin nida banko san asalina ba balle makomata sai bayin Allah nan dake rike dani suna gatana da komai nawa Auwal

Don Allah kibar fadin hakan akanki Aeesha ki godewa Allah daya baki masu rikeki din wasu na can kamarki ga gata ga komai amma sun taso a gidan marayu basu da kowa a duniya sai Allah da manzonsa kuma haka suke rayuwa suna my,amula da kowa cikin salama.

A hankali na gyada masa kai kafin nace kwarai hakane Auwal tabbas akwaisu yace kin gani ashe ke naki mai saukine tunda yau kina da wa yanda zaki nun a matsayin iyayye a gareki.

Sosai naji maganansa ya kwanta min a rai tabbas dole in kara godewa Allah bisa ni,imar da yai min da bai barmi hakana ba cikin duniya kara zube kamar yadda yabar wasu .

Da sauri na furta astagarullah a fili yace haka ya dace dake a yanzu shawara da zan baki shine ki cire zancen kowa a zuciyar ki yanzu ki maida hankali ga karatun ki koshi kika kama ya isheki a rayuwa.

Haka kuma zaki samu madogara mai kyau da kowa zai manta da asalin naki kiga an koma ana binki son abinki wanan haka duniya ta gada a yanzu ko ba,a soka don komai ba za a soka don abin hannun ka.

Na tabbatar tunda kika shigo rayuwan Man bashir yana da wuya ki tabe a rayuwan ki haka kara zube don yadda kike tsamani din nan donshi mutum me mai kaifi daya ga duk abinda yasa a gabanshi.

Ko bashi ba na tabbatar har daddy a yanzu sun tunzurashi a kanki yau Allah kadai yasan abinda zai biyo bayan hakan zakice na fada maki wannan watarana ki dai dage da addua ki yawaita sada kuma kina tawakali ga ubangiji.

Nagode Auwal na fada a sanyayye ina ajiyan zuciya lokaci guda saida naga yakai hanyan da zai dauka zuwa school nace dashi kaini gida kawai ba zan koma school din ba yau.

Hakan yasa bai min musu ba ya dauki hanya kai tsaye sai gidan mu nayi masa godiya ya kara yi min nasiha nafito zuwa cikin gida a falo na samesu suna kallo .

Sukai min sannu da dawowa na amsa tare da tambayan Ammah samira tace yanzu ta shiga sallah la,asar sai lokacin na kula da lokaci yaja sosai garama dana dawo gida don anshiga lectures ko da dadewa a lokacin ana batun fitowama.

Zaune take a falonta ta tasa abinci a gaba tana tunanen zancen yar uwarta da suka rabu dazun gaskiya dole tasan abinyi don sanin halin yar uwar nata da tayi ba kyau gareta ba.

Komai zata iya yi kan abinda ta furta din amma ta yaya hjy Nasare ta tambayi kanta hakan gashi zancene ba Wanda zakayi da wani kai tsaye ba sai su da abin ya shafa amma dawa zata soma zancen kenan a cikinsu ?

Duk wanda ta lalabo a zuciyarta sai taji ai hjy kura taji ta gama don't wasu na iya tunkaranta kai tsaye don zafin zuciya.

Zuciyanta ya tsaya akan hjy umma don lokaci da dama takan sameta da zance kuma ya tsaya iya su din babu mai jin sunyi a tsakaninsu sai Allah.

Dole taje ta samu umma din su tatauna akan matsalan tunkan wani abu da ba,aso yazo ya faru daga baya kuma a koma dana sani.

Da wanan zance ta samu taci abinci duk da dai bata iya ci sosai ba sai faman sakawa take tana warwarewa yadda zata fitowa umma da zancen don ta fahince ta.

Yayin da nikuma tunda na Shiva daki ba wanda ya kula da ya bi bayana ko ya tambayeni dalilin dawowana a lokacin sai shewa sukeyi akan film din da suke kallo.

Can Asmau ta shigo tana fadin mummy lafiya kuwa run dazun naga baki fito ba naji dadin hakan kwarai amma cikin dakiya na dago kai na dan kalleta nace lafiya lau Asmau.

Tayi dan shiru kafin tace in debo maki abincine maida yajine sai ganyen salad naga kina son shi ban iya cin abinci Asmau ina so amma ban iya ci yanzu.

Kallona tayi yanayi nadata gani ta sake fadin baki da lafiyane mummy naga idanunki sunyi ja ja jaarr mana ?

Gani dai Asmau lafiya ta kalau kawai yanayine na maida kaina saman filo na sake kwantawa yadda ta sameni da farko.

Zama naji tayi a gefena saidai bata kara magana ba dukkan mu mukai shiru na dan lokaci can tace mummy gaki da kayan shayi in dora ruwa mana ko shayi kisha don't Allah ?

Nagode Asmau na fada hakan yasa ta mike taje dora ruwan zafin bata jima ba sai gata ta dawo dashi tana fadin ga ruwan mummy saidai naga kamar ba bread ko in fita in sayo makine ?

Jin hakan yasa na dago nace tea kawai zansha nagode na nuna mata kayan tea ta hada min mai kauri tana miko min samira ta shigo tana fadin yau mun kalli wani film mai kyau mummy bakya nan .

Sai kuma tayi shiru tana duban yanayina kafin takai zaune a sanyayaye tana fadin bata da lafiya ne ?

Kai Asmau ta girgiza mata tana fadin tace lafiyanta kalau kawai yanayine amma shine kikai kuka haka har idonki yai ja ?

Wasu hawayen he suka zubo min jeki kira Ammah ta fada da sauri na girgiza mata kai alaman a,a ta barta kawai na dan kako murmushin dole nace lafiyata kalau fa.

Shiru sukayi suna bina da kallon rashin yarda da abinda na fada a lokacin kiyi hakkuri mummy in wani abu ya bata maki rai Asma,u ta kara fada nagode nace mata ina mikewa zaune.

Kafin in nisa ince dasu duniya kowa keda iyayye ya godewa Allah koyaya suke kuwa Asmau don' babu mai kallonshi yace dashi baida asali.

Ballema ke me asalice ai mummy tunda kina da su baban kano da Ammah damuwa wani irin gata yahi wanan kuma walle da nita yau sai mashi ya gane kurene wajena don zagin barnan mansha zanyi mai ta uwa ta uba in samo kazafin dayahi wanda yai min in lakaka mashi me duniyace ai ba lahira ba .

Kai amma dai mummy shi kinka zaunawa kina wagga ciki dama kakarai ki tai can zuciyarki ta harba ga banza maishi baida damu dama shi akaso again gareki.

Tunda anga kin kilance kin zamo tauraruwa mai wutsiya a yanzu duk wanda ya tareki da maganan banza fada mai asalin uwatai da ubanai cikin sheri gobe wani bai mafalkon hwada maki hakan .

Mutanen duniya yanzu baka da gadon mutum amma kana da gadon magana tai su masu uban mi sunka tsitsina wanda yahhi naki ga iyayyen nasu samirace ke wanan maganan a cikin fada.

Hakan yasa na murmusa tace awo gaskiya mummy ai duk kinka tsaya zubar da hawaye sunka gani gobema hwada making wanda yyahi haka zafi zasuyi.

Ai ba a shege sai mai uba suddiya,I an masu uban abinda sukai yanzu ba gara asan babu ubaba mu nan banda Allah ya taromu munka dawo nan da yanzu halan aikin gama bai gama ankan mu ba ?

Tunda ba a taimakon mutum don Allah sai ya bada jikinai ko wani abin banza can ba gara ma marasa uban ba yanzu sunsan zafin kansu.

Wai halan mummy was heads maki wanga magana Asmau take tambayana nace wata hjy ce akan danta.

Tace wai barkado halan yayan masu kudin nakwaraine wasu da aurensu suka biyan maza suna haihuwan diyan siti,alharni cikin duniya su dawo su zamowa mutane bala,I

Hiran su yasa na sake suna ta ban labari ni abin ma mamaki yake ban yadda macen aure zata dinga bin maza a waje da aurenta samira tace a daiyi sha,ani kawai wai an cuci na kauye waye ba waye ba yanzu.

Hiransu sosai ya min dadi duk da zagine yafi yawa amma saina shagala da hiran nasu har na manta da abin dake zuciyana lokacin.

Wayana dake a jakkata silent tana ta ringing bamu ji ba sai bayan sallah magariba sun fita wajen hada sana,ar su dana dauko waya miscalled ratata a wayan daga MB da kuma wasu sabbin number biyu dana Auwal.

Sako na tura mashi da ban kusa da waya a lokacin kamar jiran sakon yake dama sai gashi ya turo min da wani sako cewa da baiji gareni ba yanzu yake zancen salman ko Auwal sukayi shi gidan mu.

Na mayar masa da amsa ya rufa min asiri don Allah kada yasa daddy ma ya fara zargina kan dansa.

Ko kina mussun hakan ne ban iya zuwa din da sauri na mayar masa da amsa nasan zaka iya ai amma don Allah kayi hakkuri.

Don me bakya son ganinane ya rubuto min aina ganka dazun na rubuta ni ban ganki ba tunda kinki tsayawa mu gaisa.

Lah ba haka bane amma dai nina san mun gaisa dakai, kin dai gaisa da mutanen da kika sama a wajen .

Murmushi na tura mai yace ni zakiwa wayau nace gobe zanzo mu gaisa amma huta yanzu kin tabbata nace kwarai kuwa .

Sai yai murmushi dago kan da zaiyi sai a fuskan mami idonsa ya sauka ta karaso tana aje flask dake hannunta tare da fadin .

Zancen hjy kura dai ya zamo gaskiya da wanan kwara din kake hira ke nan har kana murmushi kai kada zaune.

Ai bata fadi karya ba mami yau da kece kikai min hakan sai inji haushi don ban iya ramawa amma ita aikanta tasan bashi taci a wajena don ba kyaleta zanyi ba kan abinda tayi min.

Don ba yarinyar ta muzanta ba ai ni tayi humility tana dauka kowa kamar yayantane da basu da kamun kai ko tarbiya ba gara yarinyar nan sau dubu ba akan yarta dake yawo kusan tsirara kowa na kallonta wai wayewa a haka take son a hada da ita kome ?

Au yanzu nagane uwar ta fada tana zama kusa dashi bayan ta dauko cup tace magaji wai har kasan kishi kan mace ni ina fada baka isa aure ba ?

Ko da yake ai ka isa tunda har yan mata sun fara kara kaina akanka zuwa gida ga Hindu ga yar kwara don ma hjy kura ta Kore su salman yaya hanifa ne ai daka zamo dan madubin mata ke nan .

Mami ba kwara bace fa don Allah kubar batawa yar mutane suna to ba kwara bace mecece ita don dai tafi kama gaskiya da laraba don ba za ace da ita baturiya ba.

Wacece ke nan daddy daya shigo yake tambaya wai yarinyar dazun da hjy kura tayiwa tas kai ya girgiza yana zama yace kura,kura halinta baiyi ba wallahi.

Yanzun hjy ta kirani kan zancen nace ta bari sai nazo don ban son zancen ba tare dana San komai akan yarinyar ba ko kana da masaniya kai akanta.

Kai ya girgiza kafin yace bansan komai akanta ba daddy iya dai wanan dattijon mai rikonta ban jin kuma shi din mahaifintane gaskiya.

Amma zan tambayeta wataran naji to amma meye na tambayama daddy very soon zan bar kasan nan tambayan ma baida amfani yanzu ai.

Kaji shirme ai gara ka tambaya dai kaji din zaifi don nima na yaba da hankalin yarinyar gaskiya yau da wata fitsarariyace da a gaban mu zata yi kokarin kare kanta garesu amma Sam batayi hakan ba.

Kaga ko hakan alaman tana da tatbiya da hakkuri ta nuna a gaban kowa dazun din ni wani zagin saida Addah ke fada min ma don ban tsaya saurarensu ba.

Ko hjy ta hana mu,amulan Man Bashir da yarinyar nan don rashi asali ba zan taba yarda ya auri yar gidan kura ba muddin ina raye sai dai duk abinda zai faru ya faru amma ba zan yarda da hadin da zai dawo ana da an sani akansa ba.

Daddy waini nerve koda ina da ra,ayin aure ba a nan zanyi aure ba Dad don bana son wace zata tsaya terrorting din wani akidan gidan su hjy.

Au mu ke nan bamu san komai ba kome tunda muna bin akidar gida gaskiya mami akwai gyara sosai inba haka ba bakuwarku fa akaciwa mutunci a gaban ki kuma baki dauki wani mataki ba ?

Good my son inna fada tace yaya zatayi yau gashi ka fada kaima a gaban mu gaban kowa kuma ita ya kamata tafara magana kafin nayi.

Gaskiya ina son mace wace zata tsaya a right dinta ba ta yarda da irin wanan cin fuskan da akaiwa yarinyar nan ba yau.

Akan yarta ta nuna muba kowa bane akan yarta ta nuna duk gidan nan bamu san mema mukeyi ba itace ta sani why mami

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login