Showing 1 words to 3000 words out of 44681 words
Chapter 1 - Bakin Ruhi Book Compelet By Mrs Sadauki
[06/03 16:23] MRS SADAUKI: *BAƘIN RUHI*
```LoVe aNd HoRrOr story```
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI✍️}
*SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a
kan dukkan wani da ke son cutar da mu.
*FCWA*☀️
________________________
Happy sallah my dear fans, Allah karɓi ibadunmu Amen !!!
*Wannan labari da da kaso saba'in ya faru da gaske,don haka don Allah kar wacce ta ji
haushina yayin ganin abin da ya saɓawa ra'ayi*
01
“Kowanne ahali da nasa sirrin,haka kowanne ahali da nasu tabo ko ƙaddara ko kuma dai wani
al'amari wanda suke ɓoye wa.Motar tsautsayi ce ta ja ni na bankaɗe mayafin da ya luluɓe
baƙin sirrin gidanmu wanda silar haka yasa na baro ahalina domin tseratar da da gajiyayen
ruhina,wanda aka raunata shi ta sigogi da dama” na yi shuru saboda hawayen da suka cika min
ido.Ita kuwa Lubna banda aukin kallona babu abin da take yi,da dukkan alamu ta ƙagu ta ji
ainahin labarin nawa.
Na ɗan yi murmushi mai ciwo wanda ya bai wa ƙwallar da ta taru a idona sa'ar zubowa kan
kumatuna,na ci gaba da cewa “ Gidanmu irin family house ne wanda za ki kaf yayyu da ƙannai
a ciki,mu biyar ne mahaifiyarmu ta haifa,mu biyu ne mata ukun maza.Anty Aliya ce babba,sai
Aliyu,sannan Fahad,sai ni sannan autanmu Haidar.Sannan akwai ƴaƴan kawunana su ma duk
da matansu da ƴaƴansu,duk yawanmu a tukunya guda ake yi mana girki haka muka taso muka
ga iyayenmu na yi.Sannan in za a ci abinci ma su iyayenmu maza a tare suke ci haka ma
matan,mu kuma ana banbanta wa ƴan sa'inni ɗaya ake zuba mana a cikin faranti guda da
wannan ne na yi sabo da cousin/cousine ɗita Hassana wacce ƴan biyu ne su ɗaya ta rasu a
wani dare bayan mun gama cin abinci.Ni da Hassana akwai wani abu da ke faruwa cikin
ahalinmu da yake mugun ɗaure mana kai yake kuma ci mamu tuwo a ƙwarya.Ba zan manta
wata rana mun je ɗebo ruwa a ƙatuwar rijiyar da ke can bayan ɗakunanmu Hassana ta dube ni
da kyau ta ce “Haule har yanzu mutuwar Husseina ta ƙi fita raina , kowane dare sai na yi
mafarkinta tana kuka tana ce min na cece ta,amma jiya sai take ban shawara wai na gudu na
bar gida ban san dalili ba”
“Kawai don kin san abin a rai ne shi yasa, sannan duba da cewa ku ƴan biyu ne ƙila shi yasa
kika kasa fidda abin a kanki amma kusan shekara fa yanzu da ta rasu” shi ne abin da na faɗa
mata a wancan lokacin amma sai ta girgiza kai ta ce “a'a na fi tunanin dai wani abun ne yasa
take zuwar min a mafarki, sannan kar ki manta ko sau ɗaya ba ta take rana sai ta kawo min
ziyara tana maimaita abu guda na cece ta,amma na jiya ya banbanta kawai ta ce na gudu” ban
kai ga ce mata komai ba goggo Lami wacce ta kasance mahaifiyar Hassana ta iso bakin
rijiyar,sam ba mu yi tunanin ta ji abin da muke cewa ba don ba ta nuna alamu ba kawai dai ta
ɗauki bokitin da muka cika da ruwa ta tafi.To mu ma sai muka watsar da zancen muka ci gaba
da aikinmu,bayan mun gama sai muka koma can cikin gida.
Wani irin kallo na ga Innarmu na bi na da shi,tun ban damu ba har na soma tsarguwa sai kawai
na bar inda take don kaucewa kallon.Da dare bayan duk mun yi sallar isha'i muka fito cin
abinci,tamkar wasu ƴan biki haka duk muka yi kashi-kashi muka kewaya kowa da faratinsu
muna ci muna santin girkin iyayen namu har muka gama sai aka soma yin gatana har sai da
dare ya tsala sannan duk muka rabu.
Ina shiga ɗakinmu har na kwanta na ji muryar Innarmu ta kira sunana cikin wani sauti “Haule?”
sai da gabana ya faɗi amma na daure na ce “na'am Innarmu”
“Zo nan” ta faɗa ,sai na tashi na je kusa da gadon ƙarfenta mai rumfa na yi tsaye tare da sunne
kai saboda har zuwa yanzu irin kallon nan ne na ga tana yi min.
“Kar na sake jin kin yi zancen nan ke da Hassana ,kin ji ko ba ki ji ba?”
“Wane zance Innarmu?” na tambaye ta don ni har ga Allah na manta.
“Na mutuwar Husseina,ki je ki kwanta” shi ne abin da ta ce,na je na kwanta ɗin sai dai fa sam
ba baccin na yi ba kamar yadda na so yi tun farko.
Ido kawai na lumshe,ina jin lokacin da anty Aliya ta zo ta kwanta gefena bayan kuma Innarmu ta
ce ta kashe ƙwan lantarki.Duhu na game ɗakin na buɗe idona,tunanin na shiga yi iri-iri yadda
ake yawan yin mutuwa gidanmu kusan kuma duk date iri ɗaya ne.Na jima sosai cikin wannan
tunanin,don gari yayi tsit kafin kuma na soma jin motsi a can babban falon ahali.Kamar
munafuka haka na miƙe na fita,amma ban fita zuwa ƙaramin falo sai na laɓe,iyayenmu maza na
gani kaf illahirinsu suna magana akan zancen da ban san ina ya dosa ba.
“Ibrahim yanzu ta ɓangarenka ya kamata mu fitar da alƙawari” Kawu Hamza ya faɗa wanda shi
ne babba kaf cikinsu.
Kawu Laminu ya karɓe da cewa “hakan shi ne daidai,kuma dai kyautar namiji don ni ai mace na
bayar wancan lokacin ” wato mahaifin Hassana .
Ibrahim wanda ya kasance mahaifina yanayin fuskarsa ce ta ɗan canza kafin ya ce “zan yi
shawara” sai kuma suka miƙe suka shiga wani ɗaki ƙwaya ɗaya tal wanda tun da na yi wayo
ban taɓa ganin an buɗe shi ba sai yanzu.
Ba tare da na san mene ne meeting ɗin nasu ya ƙumsa ba sai na koma kan shimfiɗata na
kwanta.Ina shirin rufe ido haske ya game ɗakin nan muka haɗa ido da Innarmu,“daga ina kike?”
ta jefo min tambayar da kafin na bata amsa Haidar ya fashe da wani masifafen kuka wanda
yasa Innarmu nufarsa da sauri.
Haidar ƙaramin yaro ne duka ba a yi wata biyu da yaye shi ba,ruwa Innarmu ta basa amma
yadda take ɗura masa su to kamar haka ya maido su ta baki da hanci kafin kuma daga ƙarshe
jini ya zubo masa ta hanci shi kenan bai ƙara motsi ba” ina kawowa nan na miƙe na bar Lubna
zaune sake da baki da hanci.
“Haule ina kuma za ki je?” ta tambaye ni,ba tare da na juyo ba na ce “zan wanke kwanuka kafin
Hajiya ta dawo”.
Wurin da aka tanada don yin wanke-wanke na nufa na soma wanke plate ɗin da customa suka
ci abinci.Ina tsaka da yi Lubna ta zo tana yi min ɗauraya,mun yi kamar minti biyar muna aikin
kafin ta ce “fatan dai ba mutuwa Haidar ɗin yayi ba?”
Na san halin Lubna da mugun son jin labari,in ba ta gamsu ba to ƙila har gida tana iya bina don
ta ji ƙarashe hakan yasa na ɗora daga inda na tsaya.
“Ina tsaye a gaban idona Innarmu ta soma yin hawaye tare da furici guda “don me sai Haidar?”
wannan kalmar ta daɗe tana yi min yawo cikin kwanya don nemo ma'anarta amma tsawon
lokaci ban samu ba.Na durƙushe kan gwiwaina tare da tambayarta “Innarmu me ya samu
Haidar ɗin?”
“Ya mutu Haule! Haidar ya mutu!” ta bani amsa tana ƙanƙame gawar Haidar,ban san lokacin da
na yi kururuwa ba wacce kusan ita ta tashi kowa na gidan ciki kuwa har da anty Aliya.
Kan ki ce wani abu ɗakinmu ya cika da mutane,ana ta kuka goggo Lami ce ta je ta rungume
Innarmu tana bata haƙuri.Yayin da Hassana ta yi tsaye kusa da ni ta ce “duba ki ga irin yadda
Husseina ta yi ne yayin mutuwarta” cak hawayen da suke yi min zuba suka ɗauke,yayin da
idona ya soma tariyo min gawar Husseina wacce har bayan an yi mata wanka jinin da ya fita ta
hancinta yana nan bai goge na sai ma ƙari da aka samu wanda kafin safe har da idonta suke
shatatar da kukan jini.Ban iya cewa Hassana komai ba a wannan lokacin sai dai mun ci gaba da
kukan mutuwar Haidar,wanda har asubah babu uba namiji ko ɗaya da ya leƙo ɗakinmu sai da
gari yayi haske shi ma ɗin karɓar gawar suka zo.
Bayan an yi wa Haidar wanka aka bai wa Innarmu damar yi masa ganin ƙarshe,haka don
ƙwaƙuwa na mara mata baya har sai da ta buɗe likafanin nan na yi arba da idonsa su ma suna
shatatar da jini.Kuka ne ya kubcewa Innarmu,kawai aka rufe gawar tare da fita shi nan gidan
namu ya ƙara kancamewa da koke-koke ganin an fita da shi.
Ana cikin zaman makoki ne Hassana ta zo ta ja ni gefe,na ce “ke lafiya?”
Sai da ta waiwaiga sannan ta ce “jiya bayan mun kwanta na yi mafarkin Husseina ta ce na baki
kayanta waɗannan wanda ta mutu da su ki saka a jikinki”
“Saboda me?” na tambaye ta ,ta ce “ke dai don Allah ki saka” nan na yi da ita zan saka ɗin
kamar yadda ta buƙata” sai kuma na sake yin shuru na kalli Lubna wacce ta tsaya cak da yin
aikin,na sakar mata murmushi na ce “ya dai kin tsorata ne? Ai ba ki ji komai ba nan duk
shimfiɗa ce ke dai ki yi haƙuri da sannu duk za ki ji dukkan labarina”
Lubna ta ce “ai duk jikina yayi sanyi duk da dai ni ma da nawa labarin mai matuƙar firgici ”
Masifar Hajiya ce ta katse hirar tamu,da sauri na fita ina bata haƙuri ita kuwa kamar ƙara zuga
ta nake sai ƙaimi take ƙarawa wurin faɗan.
“In ba ku canza ba wallahi sai duk na kore ku na kawo sabbin ma'aikata,dubi yadda har yanzu
ba ku goge table ba”.
“Yi haƙuri Hajiya amma don Allah kar ki kore ni ba ni da kowa” na faɗa murya na ɗan rawa
,amma da yake Hajiya ƙarshe ce wurin rashin mutumci sai ta tsiro da wani zancen “yau ba za ki
ci abincina ba sai da ki saya da kuɗinki,saboda kin ga ina tausayinki ne kike yi min iya shege”
tana gama faɗar haka ta yi ƙuuu ta fice,ni kuma na yi baya na zauna kan kujera saboda kaina
da ke mugun sara min.....
[07/03 15:42] MRS SADAUKI: *BAƘIN RUHI*
```LoVe aNd HoRrOr story```
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI✍️}
*SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a
kan dukkan wani da ke son cutar da mu.
*FCWA*☀️
________________________
02
In akwai abin da ya fi ɗaga min hankali shine zancen kora ta da Hajiya ta ce tana iya yi,wanda
kuma ya ɓata min rai shi ne yadda a kullum take wulaƙanta ni kawai don ina ƙarƙashinta.
Lubna ta fito wacce ita tun tuni ta gama aikinta,dama ita iya girki ne take yi.Ni kuma tarben baƙi
da kawo musu abin da suka buƙata,sai kuma wanke kwanuka da share restaurant ɗin.
“Ki je ki yi wanke-wanken ni sai na goge wurin” ta faɗa cikin sanyin murya,ban ce mata komai
ba na miƙe dakyar na je na ida aikin nawa.Sannan na dawo nan muka ƙarasa gugar,bayan mun
gama na rufe ko ina kafin mu kama hanyar gidan Hajiya .Da ɗan nisa wannan yasa sai da muka
yi sauri kafin mu isa,a falo muka tarar da ita ta ƙure ƙarshen ac amma duk da haka sai gumi
take fitarwa.
Kallo ɗaya na yi mata na ɗauke kai,saɓanin Lubna da ta je tana cewa “hajiya ko jikin ne ya
motsa?”
Cikin murya wacce kana ji ka san babu lafiya ta ce “olser ce ta yi min wuf sai ɗan kanoma,ki
bani maganin nan na sha wanda kike bani”
Lubna ta ɗan dube ni kafin ta ce “ai Haule ce ke da shi dama ba ni ba”
“To ki karɓo min”
Ina jin haka na yi saurin wucewa can ɗakinmu da aka ware na ƴan aiki.Ina tsaka da rage kayan
jikina Lubna ta shigo hannunta riƙe da kofi ta ce “ki zuba na kai mata”
Cikin ƙunar rai na ce “na ƙi na zuba ina ce dai yawuna ne”
Lubna ta tuntsire da dariya tare ɗan matsowa kusa da ni ta ce “ke ba abin alfaharinki ba ne a ce
kamar Hajiya tana shan yawun ƴar aiki ? Kin san da ace ta san mene ne ainahin maganin da ba
za ta sha ba Alkur'an yadda ta tsani talaka”
Wani ɗan murmushi na yi kafin na tofa yawuna cikin kofin ruwan,nan take suka soma tafasa
suna motsi tare da canza kala.
Lubna ta ɗaga gira ta ce “ai ke ce Hajiyar,sannan don Allah ki yi haƙuri ki bar saka mana
hajiyarmu cikin wancan halin kar ta je ta mutu mu shiga tara”
“Tafi dai ki kai mata kika tsaya surutu” na faɗa tare da shiga toilet na yi wanka,ko da na fito sai
na tarar da Lubna ta kawo mana abinci.Nan ɗin ma wani murmushi na yi kafin na ce “cewa ta yi
fa ba za ta ban abincinta ba”
“Tun da dai ta zuba miki sai ki yi haƙuri ki zo mu ci” cewar Lubna.
Sai da na canza kaya sannan na zauna muka ci shinkafa da miya muka hauda ruwa masu
sanyi.Sai kuma muka hau yin hira kafin kuma ta miƙe ta ce “bari na je na gyara kayan miya na
gobe,ki shirya don da na dawo za ki ɗora min labarinki” na yi murmushi kawai ba tare da na ce
komai ba.
Ina shirin kwanciya Lubna ta shigo kamar an jefo ta,na ce “ke lafiya?”
Ta ce “uban ƴan tsamin rai ne ga shi can a falo tare da Hajiya yana juya kofin da na bata ruwa
wai yana son ganin wane irin magani ne wannan da ta sha ta samu lafiya lokaci guda”
Na ce “to mene ne na ga duk kin tayar da hankali?”
Ta waro ido ta ce “hajiya ce ta basa amsa wai ke ce kike da maganin,kuma walla...”sauran
maganar ce ta maƙale mata ganin an banko ƙofa da mugun ƙarfi har ni ma sai da na zabura
yayin da haɗuwar idonmu ya saukar min da matsanancin faɗuwar gaba amma na aro mayafin
jarumta na gaishe shi cike da ladabi kamar yadda uwarsa ta ce mu dinga yi.
“Ina wuni Alhaji ?” na furta cikin sanyin murya ina mai sauke idona ƙasa.
“Bani maganin da kika jiƙawa Mama ” shi ne abin da ya ce.
Na ce “ya ida ai dama guda ne ya rage”
“Bani kwalinsa ”
“Bai da kwali ”
“Ina aka taɓa sayar da magani babu kwali?”
“Wannan ɗin ba sayar da shi ake yi ba ai,na gargajiya ne”
“Ina son ganin ledar da aka ƙulla shi to” ya faɗa cikin son sai ya ƙure ni,na ɗago kai na kalle shi
kafin na juyar da idona gefe na ce “na share ledar”
Bai ƙara cewa komai ba ya fice ƙuuu tare da banko ƙofa.
“Ina ga gida zan je zuwa an jima sai na dawo, wannan masifar ba ta ida ba wallahi sai ya sake
dawowa kin san shi da zafin kai.Kuma ni ban son ganinsa cikin wannan halin duk sai na ji babu
daɗi kuma gwiwaina su yi sanyi” Lubna ta faɗa tana yin wani kalar tausayi.
Na taɓe baki na ce “ni ban ga abin da kika gani a jikinsa ba da har kike wani sonsa haka,mutum
a bushe kamar mai cutar HIV sai shegun manyan ido kamar ƙuliƙuli dama-dama dai lips ɗin
nasa su ne kawai masu kyau”
Lubna ta yi min dundun wasa ta ce “ke ban fa son rainin hankali,alhajin ne kike shammata
haka? Haba dai! Kuma ni ba sonsa nake yi ba kawai dai yana burge ni” ta ƙarashe zancen tana
wani murmushi mai tona asirin zuciyarta.
Canza zancen na yi na kamo wani,“ sai yaushe za ki dawowa nan da kwana? Allah na gaji da
zama ni ɗaya cikin ɗaki kamar mayya”
Lubna ta ce “ke na manta ban faɗa miki ba,ɗazu bayan kin tafi restaurant an kawo wata ƴar aiki
da alamu nan za ta zauna ita ma tun da ba ta da kowa kamar ke take”
“Ni babu ruwana da wata,ke nake magana yaushe za ki dawo nan? Na ga dai san ba za a hana
ki ba duba da Umma ƙawar Hajiya ce ”
“In na je yau zan tambaye ta in ji in za ta bar ni,amma da wuya kam zan dai gwada.Na tafi sai
zuwa yamma zan zo kamar kullum” cewar Lubna .Sai na saka hijabi domin yi mata rakiya duk
da ba wani nisa ne ke da kwai da gidan Hajiya zuwa nasu .
Muna ratso falon muryarsa ta tarbe mu sai masifa yake duk a kan maganin da na bai wa
uwarsa ta sha ta warke.
Muna haɗa ido da shi ya ce “nan gaba duk ƴar iskar da ta sake bai wa Mamana maganin ƴan
bori sai na kulle ta ,kar a sake shigo mana da kayan tsibo cikin gidan.Ke ma Mama ki rasa
maganin da za ki sha sai na gargajiya? To mene ne amfanin karatun likitacin nawa?”
Ban kula shi ba don na fahimci tun ranar da na zo nan gidan ya tsane ni,wannan dalilin yasa ni
ma yake ban haushi.Muna fitowa daga gidan Lubna ta ja wata ajiyar zuciya a bayyane kafin ta
ce,“matar Maheee nada jan aiki,a yi mutum sai masifa kuma sam bai ma gajiya ”
Na ce “shi yasa