Showing 36001 words to 39000 words out of 55823 words

Chapter 13 - Romon Hakuri Compelet By Mrs Sadauki

13 Jun 2026

41

ƙarshen shekara ɗaya daga cikin mutanen yankin zai zama hadiya ta aljanai.

Shiru wurin ya ɗauka suna kallona,suna jiran amsata a matsayina na shugaba.Ni ma shirun na yi ina nazari,wanda ban san ashe cewa tazarar lokacin da na ɗauka kafin na miƙa yardata ya fusata aljanun ruwan sun komawarsu.


“Sun fusata ba za su sake yin magana ba sakamakon shirun da kika yi yayi yawa.A matsayinki na shugaba ya kamata a ce kina bada amsa ne a kai ba tare da nazari ba” ƙawata Debora ce ta yi wannan furucin idonta na kallon tsakiyar ruwa.Dukkan matsafan sun yi amanna da furucinta,ban ce komai ba sai taku da na fara yi ina ɗaga kafaɗata gefen da ke da ƙusumbi na shiga can tsakiyar ruwan.Tafin hannuna na hagu na kalla ina yin wani furuci nan take ya tsage jinina ya soma ɗiga a cikin ruwan.Duk ɗigo ɗaya ina iya jiyo wani nishi daga can ƙasan ruwa,na ɗauki kamar minti biyu a haka kafin na dakatar da zubar jinin sai kuma na soma yin magana cikin sauti ƙasa-ƙasa “joliho kuntahee namaruju kalmari hanaighar kashmuh balbilancaaaa!” babu shiri na lumshe ido jin yadda wata irin guguwar ruwa ta tashi tana tunkuɗo duk wani masarafin tsafi izuwa gare ni.


“Ya ke ƴa ga Bazuka ki sani cewa kowanne tasiri da farashinsa,sannan mu halittun ruwa ba mu taɓa mance duk wata alaƙa da aka ƙulla da mu .Za mu bai wa garinki kariya kamar yadda kika buƙata sai dai ki sani a duk lokacin da kika take dokarmu za mu bayyana miki asalin me ake kira da masifa da annoba ” wata murya da ke kama da ta macijin ruwan ta yi mini jawabi.

“Hakan ba zai taɓa faruwa ba,zan kiyaye dukkan sharuɗanku” wannan karon na bada amsa kai tsaye.

“Mu ne za mu zaɓar hadiya da kanmu,a duk sa'ilin da lokaci ya yi za mu nuna miki mutumin da muke buƙatar jininsa ta mafarkinki ”

“Na amince!”

“Sannan kuma haramun ne shiga ruwa ranar Laraba ”

“Na amince!” ina furta haka kawai sai yanayin garin ya canza ya ɗauki wani irin launin duhu amma ba sosai ba,sararin samaniya ya cika da baƙaƙen giza-gizai yayin da kuma kukan tsuntsaye da kaɗawar bishiyoyi ya tsaya cak.


“Aroroke! Aroroke! Aroroke!” shi ne abin da sauran mutanen da muka zo suka fara faɗa cikin murna saboda dukkan alamomin nan da suka bayyana na nasara ne.

A hankali na fito daga cikin ruwan ina mai fuskantar su sai duk suka yi shiru tare da sauke idonsu ƙasa don nuna girma a gare ni.


“Daga yau na sama wa garinmu suna za a dinga kiransa YANKIN MUTUWA,duk wanda ya shigo sunansa gawa ba wai mutum ba ko dabbar da ba ta wannan garin ba ta shigo na bada izini kafin a zo a faɗa mini a kashe ta” nan ɗin ma jin daɗinsu suka bayyana a fili kafin na wuce gaba su mara mini baya muka koma can tsakiyar gari inda na sa aka ƙara ƙawata gidanmu.


Kan shimfiɗar da gawar Maa ta rushe na hau tare da yin kwanciya.Ina lumshe idona fuskar Naslam ta dawo mini da wani mugun sauri na buɗe su tare da tashi zaune ina jin zuciyata na harbawa da sauri.A fili na ja wani tsuki ina jin tsanarsa da su kansu mabiya addininsa.Yatsun hannuna na murza tare da furta kalmar tsafi nan take ragayar da ke maƙale a tsakiyar iccen rufin ɗakinmu ta yo ƙasa ta zo daidai inda nake wata ƴar ƙaramar takarda na gani mai ɗauke da haruffan tsohon asiri.Ban yi wani dogon bincike ba na fahimci cewa wannan takarda daga mahaifina take,mutumin da daidai da sakan ɗaya ban yi rayuwa da shi ba.Rubutun bai da yawa a ido,amma ma'anoninsa sun isa a rubuta dogon labari.Tsam na miƙe bayan na maƙale takardar a ƙuguna,daidai ƙofar da za ta ba mutum damar shiga uwar ɗaga na zube tare da shafar wurin nan take ya ɗau wani haske yana mai bayyanar mini da jan rubutu wanda aka rubuta da jinin mahaifina.

“Finstako Bazaku enfinstako naheee” ina furta haka ƙasar wurin ta tsaye sai ga wata ƴar madaidaiciya wuƙa ta bayyana mai ɗauke da sunan mahaifina,nawa da kuma na Maa.Sai da na tsaga jinina ya ɗiga a kai sannan na samu damar ciro ta.Wani mummunan iska ne ya taso daga sama ya cilla ni gefe kafin guguwa ta fara haɗuwa daidai wurin da na ciro wuƙar.Wata siffa ce ta bayyana a gare ni,tun a kallon farko na ga ne shi ɗin mahaifina ne duba da fuskarsa sak irin tawa ce.Hannu ya miƙa mini,daga wurin da nake zuwa inda yake da ƴar tazara amma hakan bai hana ni ɗora hannuna kan tafinsa ba sai ya janye ni muka ɓata cikin iskan guguwa.Wata tsohuwar maƙabarta ce mai zubin ta kiristoci,kowanne kabari da nasa sunan.


“Wannan ce hanyar da matsafa ke bi don kawar da maƙiyinsu ba tare da sun sha wahala ba.Da zarar kin ginawa mutum kabari to lissafin mutuwarsa zai dawo hannunki ,ke ce za ki zaɓar lokaci da kuma yanayin da zai bar duniyar bil'adama zuwa ta matattu” shi ne bayanin da Abbana ya yi mini ba tare da na tambaye shi ba.


Kallonsa na yi ina mai cewa “ni banda maƙiyi ko ɗaya”

“Shi kuma Prince ɗin da kuka haɗu fa? Kin yi tunanin cewa haka kawai ne kika fita daga duniyarmu ta tsakiyar ruwa zuwa duniyar turɓaya? Ya ke ƴata ki sani daga ranar da muƙamin iko na prophecy ya fara aiki a kanki to abu na farko da uwayen gijinmu suke nuna maka shi ne babban maƙiyinka”

Shiru na yi ina nazarin furicinsa ,so nake na san ta ya aka yi Naslam ya zama maƙiyina,don na fahimci sarai a kansa ne yake magana.


“Dalilin da yasa kika zama maƙiyiyarsa saboda ta silarki ce aka yi galaba a kansa,ba don a ce ya shagala da kallonki ba to da tabbas magauta ba za su harbe shi ba” ya ƙara faɗa kai ka ce shi ke sarrafa tunanina da har yake sanin abin da ban furta ba.



“In dai duk abin da ka furta gaskiya ne,to zan so a ce a duk lokacin da yake tsakiyar fafatawa da maƙiya ya zamana ni kuma na bayyana a wurin ta yadda zan zamo rauninsa,ya gane ya kuma fahimci cewa wutsiyar raƙumi ta yi nisa da ƙasa.Ta hakan ne kawai ba zai taɓa sha'awar farmakar yankina ba”


Bai ce mini komai ba sai wuƙar nan da ya cire daga gidanta ya miƙo mini tare da nuna mini wani buɗaɗen kabari wanda a jikinsa aka rubuta sunan Prince Naslam.
Hannuna na tsaga jini ya zuba a cikin ramen kabarin,babu jimawa wuta ta soma ci balbal.Daga nan kuma kawai sai tsintar kaina na yi a ɗaki,ba tare da na san alƙawarin jini ne na ƙulla Ni da aljanai ba.




★DAULAR ABU NASLAM


Tutar daular ce aka juye alamun babu lafiya a yankin.Dakaru haɗi da hadimai sai faman kai komo suke yi suna jiran tsammani na farfaɗowar jagoransu,madubi kuma gun babbar masarautar musulinci.


Sarki Haroon mahaifi gun Prince Naslam a tsaye yake a wata kusurwa wacce ta yi daidai da alƙibla.Idonsa a rufe suke,yayin da kuma ya haɗe hannuwansa wuri guda domin nuna ladabi ga Ubangijinsa.A hankali yake motsa bakinsa,duk da ba a jin furucin amma za a iya fahimtar abin da yake cewa shi ne “Ya Hayyu! Ya Ƙayyum! Wato ma'ana Ya Rayayye! Ya dawamamme!” iya shi kaɗai yake furtawa bai dakata ba kuma sai da ya ji murya jakariya Ali yana cewa “shugaba cikin amincin Ubangiji ka'aba Prince Naslam ya dawo hayyacinsa ”


“Shukuran Ya Rabb!” shi ne kawai abin da ya furta kafin yake juyowa yana kallon Ali wanda duk ya fita hayyacinsa tun ranar da suka dawo daga yaƙin tsibirin Mayu.

Murmushi sarki ya sakar masa wanda ya haifar masa da samun wata ajiyar zuciya nan take kafin cike da girmamawa ya ce “yarima na buƙatar ganinka”

“Mu je!” ya furta kafin sarki ya shiga gaba shi kuma Ali na take masa baya har suka shiga ɗakin yarima Naslam inda yake kwance yayin da kuma tsoho Barham ke kula da lafiyarsa.

Suna haɗa ido da mahaifinsa ya yi saurin yunƙurowa da niyyar tashi,sai dai raunin ƙirjinsa ya dakatar da shi da wani mugun sauri ya koma ya kwanta yana mai yin wani irin nishi.


Barham ya ce “na yi nasarar cire dattin garin mahalbiya,nan da kwana uku in sha Allah zai iya tsayuwa kan ƙafafunsa”

Sarki ya ce “Ubangin ka'aba ya albarka ce ka ya ƙara maka ɗimbin ilimin sanin magani”

Barham ya amsa da “ Amin ” kafin kuma ya yi wa Ali alama suka fice suka bar sarki shi da yarima.

“Ya jikin naka?” sarki ya tambaye shi yana mai dafa goshin Naslam ɗin.Maimakon ya basa amsar tambayarsa sai cewa ya yi “Abih aljanar da nake baka labari ita ce silar raunin da aka ji mini,na gan ta a zahiri tana tsaye gaɓar teku sanyen da kayan arna,ƙusumbin tsutsotsi maƙale a bayanta,idon sharrinta na fitar da gubar tsafi ”


“Naslam na sha faɗa maka ita ɗin ba aljana ba ce,wakiliyar duk wasu sheɗanun Mayu da matsafa ce.Ita ce aka damƙawa kundin prophecy domin cika wani baƙin ƙuduri nasu.Amma da ka gan ta wane yunƙuri ka yi?”

“Abih ta ya zan iya yin wani abu? Yanzu dai ina so a shirya dawakan yaƙi su ƙara komawa can domin binciko mini ita”

Shiru sarki yayi kafin kuma ya fita,cike da bayar da umarni ya sa aka shirya dawakai majiya ƙarfi da kuma dakarun yaƙi . Jakariya Ali shi ne ya shugabanci tawagar,sai dai sama da awa biyar suka kwashe ko kusa da ruwan sun kasa zuwa saboda tsantsan tsaron da aka shimfiɗa musu a dole ya jawo su suka dawo gida a lokacin tuni yarima Naslam ya kasa sukuni ya sa an kawo masa farin ƙyalle haɗi da abin zane haka ya zauna ya zana Naomi kai ka ce ta gasken ce .

Ido ya tsura mata cike da tsana yana tambayar kansa a zuci ‘ wace ce ke? Me yasa tun da na shiga zangon balaga kika addabi rayuwata?’

Jin an banko ƙofa yasa shi barin zancen zucin tare da maida idonsa kan ƙofar shigowa.Jakariya Ali ne sanye da kayan yaƙi,zanen ya fara kallo kafin ya cewa yarima “babu wata nasara dangane da tekun can,amma wai don Allah me yasa ka damu? ”

Cikin zafin rai ya ce “aljanar mafarkina ce”


“Amma fa ita ce ta cece mu lokacin da Mayu suka fara sarrafa tsafi ” jakariya Ali ya faɗa .

“Bayan ta yi silar cutar da ni,Ali na tsani aljanar nan tun ba yau ba na fahimci cewa ita ɗin rauni ce a rayuwata”

“Yarima a duk lokacin da na ji kana irin wannan zantukan sai na dinga jin cewa kai ma fa tamkar kana ɗauke da ikon prophecy ”

Kafin yarima Naslam ya kai ga yin magana wani irin iska mai sanyi ya fara ratso ɗakin yana shigowa,babu abin da ya motsa sai zanen hoton Naomi shi ma ɗin cike da abin al'ajabi yadda bakinta ke ɗan buɗewa tana murmushi.....
[12/06 12:37] MRS SADAUKI{Laouali Rabo}: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐
"""""""""""""""""""""""
LoVe aNd HoRrOr StOry☠️

```MRS SADAUKI```💫✍️

FCWA☀️
____________________________________________

03


Zanen fuskar Naomi bai gushe yana murmushi ba suka jiyo sautin wata waƙa wacce yarima Naslam ne da kansa ya haramta ta saboda kalaman da ta ƙunsa na tsafi da kuma kirari zuwa ga tawagar dabar Mayu da matsafa.

Jakariya Ali ne yayi saurin tsayuwa kusa da window ta inda ya fi jin sautin na fitowa.Wata makauniyar tsohuwa ya gani a durƙushe riƙe da sanda tana rera waƙar tana wani jinjina kai haɗi da murmushi.


“Ina ga mun yi baƙuwa ne ,ba don haka ba ai ka haramta raira waƙar nan” jakariya Ali ya faɗa .

Yarima da ya cika yayi fam kamar zai fashe ya ce “a kama ta”

Da wani irin gudu kuwa jakariya Ali ya fita ,babu jimawa yasa wasu dakaru biyu suka damƙe matar tare da kai ta can ɗakin ajiyar masu laifi ya kuma bada umarnin a ƙara tsaro sosai.


Shi kuwa yarima Naslam zanen ya naɗe tare da adana shi ƙarƙashin pilow .Sai a lokacin kawai ya tuna akwai sallolin da suka hau kansa waɗanda bai yi ba,tsuki ya ja a fili yana cewa “duk sharrin aljanar nan ne”
Cikin ikon Allah sai ga jakariya Ali ya dawo ,shi ne ya taimaka masa zuwa banɗaki ya yi ɗahara haɗi da alwala sannan ya fito ya soma gabatar da sallolinsa.
Bayan ya gama ne,mai magani Barham ya ƙara shigowa ya duba shi tare da basa maganin sha da kuma na shafawa wanda cikin hukuncin Ubangiji sai ya ƙara jin ƙarfin jikinsa.


“Zuwa bayan sallar asar zan haɗa maka ruwan magani a bahon wanka sai ka shiga ka yi,amma ina so don Allah ka cire duk wani tunani akan yarinyar da ka zana ” Barham ya faɗa .

Yarima Naslam ya ɗago manyan idonsa masu firgita maza ya ɗora kan Barham kafin ya ce “me ka sani game da ita?”


Barham ya gyara tsayuwarsa kafin ya ce “ita ɗin ba kamar sauran mutane take ba,an haife ta bayan ɗaukar ran mahaifinta,an raine ta cikin gata da soyayya sannan kuma an damƙa mata muƙamin prophecy a ranar da mahaifiyarta ta yi gushewa wannan dalilin kaɗai ya isa ya tabbatar maka iya tunaninta ma kaɗai ba alkhairi ne ba ga Sarkin goben masarautar nan”


“ Ban fahimce ka ba,kana nufin ita ɗin annoba ce ga duniya baki ɗaya?”


“A'a! Ita ɗin fa shugaba ce,kamar yadda kake kare Yankinka to ita ma haka jininta ke tafarfasa in aka ce an taɓa ahalin mugaye.Tana da ƙarfin ikon maitar ido,ga kuma baƙar maita ta baki wadda da za a ce ta tofa yawunta a tekun wani yanki da ba nata ba to tabbas da ruwan sun haramta saboda tasirin ƙwayoyin cutar da ke ciki.Na yi magana da jakariya Ali ya shaida mini duk yadda komai ya faru,kuma na gaskata sarauniya Naomi ce saboda abin da na tsinta a yayin yi maka magani”

“Me fa?” yarima Naslam ya tambaya.

Shiru Barham ya yi kafin ya tako ya iso gun yarima,cikin muryar raɗa kamar mai jin tsoro ya ce “ta jefa maka cutar ayni wato maitar ido, wannan ne ya hana ka motsi ya juye maka tunani ka manta cewa filin daga kake har sai da magauta suka yi nasarar harbin ka”


Zuciyar Naslam ce ta fara tafasa kamar za ta faɗo,yana jin ina ma zai ga Naomi a yanzu da babu shakka tabbas da hannunsa zai kashe ta.Haka ya danni zuciyarsa,ya yi ƙoƙari sosai wurin manta wa da ita sai dai kamar abin isimi lokacin yin wankansa na yi na magani idanunsa suka fara yi masa gizon yadda ta kafe shi da idonta masu matuƙar girma da kyawu don tamkar gwal haka suke sheƙi.
Jakariya Ali ne ke taimaka masa har ya samu ya shiga ya kwanta cikin bahon wankan,kamar jira ake yi kuwa wani al'amari ya riske shi.Ji yayi kamar an rufe shi bai numfashi kafin ya soma jin wani yanayi wanda sam ba zai iya misalta irin abin da yake ji ba.Jikinsa ne ya ɗauki wata irin kyarma sakamakon wasu halittu da yake gani dishi-dishi waɗanda ya yi imani cewa ba Mala'iku ba ne.Can kuma ya soma wani abu kamar mafarki yana tare da Naomi yana tarayya da ita kamar sauran mafarkansa na baya.
Jakariya Ali da ke gefensa tuni ya fahimci abin da ke faruwa,muryarsa na ɗan rawa ya kira sunan yarima Naslam kafin ya ce “innalillahi wa'inna ileyhi raji'un!” nan take komai ya tsaya cak.Yarima Naslam yayi wata irin zabura haɗi da nishi bakinsa na fitar da baƙin jini.Jakariya Ali ne ya yi hanzarin goge masa jinin kafin ya taimaka masa ya yi wankan,da ya fito ma shi ne ya taimaka masa wurin saka kaya marar nauyi kafin kuma a gabatar masa da tafasasshen shayi wanda suke yi ko wane dare.Har ya yi sallolinsa bai dubi kofin shayin ba saboda abin da ke damun ransa,bayan sallar isha'i ne sarki ya shigo da kansa ya duba shi.


“Gobe ka tura dakaru zuwa bakin Teku su ƙara binciko mini aljanar nan” yarima ya faɗa yana wani kawar da kai gefe.

Sarki ya ce “zan so ka manta da batun yarinyar nan ka fuskanci sabon al'amarin da ke shirin tunkaro masarautarmu Naslam.Sanin kanka ne duk abin da ya cika naci to babu alkhairi a tattare da shi,ba tun yau ba kake faɗa mini kana yin mafarki da aljana to ka sani shigowa da ita masarautar nan daidai yake da ruguza duk wani ginshiƙi da ka gina tsawon shekaru” sai kuma ya yi shiru tare da zuwa ya ƙara ɗaukar wani kofi ya zuba masa shayi sannan ya saka cokali yana juya shi tare da miƙa masa ,ba don ya so ba ya karɓa ya soma sha.Sai kuma a wannan lokacin ne sarki ya ci gaba da cewa “gimbiya A'ishah na waje tana jiran fitowar ka ,zan so a ce ku daidaita kanku tun a yau don a samu a wuce wurin,na san daga lokacin da aka ɗaura maka aure shi kenan matsalarka za ta kau”.

Ambaton sunan gimbiya A'ishah shi ya wanzar masa da nutsuwar zuciya,don yana mugun ƙaunarta har cikin ransa saboda ba ƙaramar gudunmawa ta bayar ba wurin haɓaka musulunci a masarautar nan ba.


A hankali ya sauko daga gadon da yake,sai dai sam ya kasa jurar tsayuwar a dole ya koma ya zauna.Cikin ɗan ɗaga murya sarki ya ce “Ali?” shi kuwa kamar mai jira haka ya buɗe ƙofar ya shigo tare da ƙamewa.


“Ka fito da yarima zuwa waje” ya faɗa tare da ficewa.Jakariya Ali ya ɗauko kujera ya taimaka wa yarima ya hau ya zauna sannan ya soma tura shi zuwa can falo wanda ya cika da ahali da kuma aminnan arziki.Tun daga nesa suka haɗa ido da ita,da wani mugun sauri ta yi ƙasa da kanta cikin kunya tana yin wani sihirtacen murmushi.Har aka ƙaraso da yarima ba ta ɗago kanta ba,haka aka shiga jera masa sannu yana amsa wa amma idonsa na kanta.



“A'ishah zo ki gaishe da yarima mana kin wani tsaya wuri guda kina sunne kai kamar ba ke ce a yanzu ki ƙi cin abinci ba saboda shi” mahaifinta ya faɗa yana wani murmushi haka ma duk sauran mutanen wurin fuskarsu cike take annuri in aka cire mahaifiyar A'ishah ɗin da take jin kamar ta je ta kama wuyar yarima ta shaƙe shi har sai ya mutu.



Gimbiya A'ishah ba ta ko motsa daga inda take ba,sai da mutanen suka dinga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login