Showing 9001 words to 12000 words out of 79064 words

Chapter 4 - MEKE FARUWA BOOK COMPLETE BY HALIMA K. MASHI.doc

makarantar sune bari zanyi maganin su yau sun samu mama tana cin abinci suka zauna mansura tace mamanmu zan ci tuwon nima, ta turo mata kular gashi nan ki saka gamiyar can cikin tukunya wata nayi kin san yau ladiyo ce ta yi girkin mansu tace. A'a mamanmu ba an raba girkin ba? Bilkisu tace kin san matan gidan sai dai shirin Allah sun kuma cewa sai dai a hada,Mansura ta ture kular tare da cewa ba zan ci tuwon wannan kazamar ladiyon ba. Bilkisu tace yauwa. Mamanmu, gaskiya kima su sakina magana su daina kula kananan yaran nan, ga masu sonsu 'yan mutunci, ai gara ma su fitar da mazan saboda fadan baba ko yaya ki ka gani tunda suna j.s.s3 ne sun ci gaba can dan fadan baba yana daga min hankali ta soma hawaye duk dana tsani maza da ace na samu mai sona ko yaya yake Allah zan yi aure ne..
Ko dan ke ma ki huta da gorin'yan gidan nan, mansura tace haka ne tunda suna da manema, cikin tausayi mamanmu tace maigado kena ke tunani bana son su riga ki aure,gashi naso suma suyi karatu mai dan zurfi.Bilki tace kada ki damu aure da mutuwa duka na Allah ne,kema zaki samu saukin fadan baba in kin rage biyun,suna cikin tattaunawa ne maryam ta shigo mama tace mamina daga ina?Tace banace miki Ibrahim ya iko kirana ba?Tace yauwa dama ina son in ji shin da gaske ne auran ki zai yi?Maryam ta sunkuyar da kai kasa tace tun tuni fa yake cewa zai turo na ce mishi a'a saboda ga antinmu nan bata yi ba. Bilkisu tace kin ji shirme,to dama in yazo kice mishi ya turo tunda ba boyayye ba ne,kowa yasan gidansu akwai mutunci,mansura ta duki kafadar bilki tace kai su Bily akwai shegen manyace,suka sa dariya bily tace Allah kuwa na sakina ne wannan Abdul din nake ganin sai an dan yi bincke kanshi,saboda don kano ne Mansura tace shin kece za ki bincika?Bilkisu tace,to hakkin baba ne kema kuma kin san ba zai yi ba amma a san yanda za'ayi ko Mamanmu? Ta ce dole kam.

Bayan binciken da Mamanmu ta saka aka mata kan mai son sakina ta hanyar mijin hajara suka gamsu da maneman sannan ta basu dama suka fito aka sa rana. Walimar saukar su Bilkisu tazo inda aka yi a cikin harabar makarantar tasu. Bilkisu ta amshi kyaututtuka, kamar su'ya mai ladabi ta daya, tsafta tare da taimakon malamai, wato in ba malami sai a sata ta koyar da yaran. Mamanmu sai da tayi kukan murna, yayi da labari ya karade unguwar, Umma ta shirya musu walima ta musamman tare da buga musu kalanda da sauran abubuwa, wai! Nan Abu ya ba su Ladiyo haushi in da suke ta yar da habaici.

Washe garin walimar, wai a banza tunda ba walimar aure bace, shi kan shi baban su kanshi kato yake duk Wanda ya mishi murna, sai ya yi ta fadi 'yarshi tayi sauka amma bai taba basu koda biyar din fensir ba.

A gida kuma cika ya shiga yi yana cewa bata da ladan komai dan ta sauka tundaba aure tayi ba, ga Bilkisu duk ba wannan ne a gabanta ba, mafarkin Yarima da ya zame matan masifa shi ne matsalarta, ko gyangyadi ta yi sai ta ganshi, ga rashin mashinshini ta rasa me ke faruwa da ita.

Duk abin da aka sama rana ai yazo, sai ga Bilkisu Sakina yazo, 'yan Bauchi sun zo tun sauran kwana uku biki, ranar ce kuma aka kawo a kwatunanan da ket suka kawo, kaya masu tsada da kyau Ibrahim yana aiki ne a zonal office Kaduna, don haka ma can za'a kai ta, yayin da Sakina zata yi kano Abdul dan kasuwa ne in ji ' yan magana suna cewa, Dan kasuwa mai kamar wani sarki.

Su Ladiyo sai zunburar baki da jin haushin maigidan ga zaton su duk abin da ake facaka dashi tun kafin ranar daurin aure shi yayi, basu San ma daga in ake da shi ba, ya kawo kudin sadakin da ya amsa naira dubu ishirin- ishirin ayi amfani da kudin ba, da kyar ya ba da dubu ishirin yace ya dauki dubu goma-goma cikin sadakin kowaccensu, cewarshi zai ci da su ne a banza? Mamar tace sadakin hakkin yara ne amma tunda ka ce haka shi kenan yaje ya dauki ladan tuwon ko kuma kudin hatsin da ya ba su.

Hajiya Kilishi uwar dakinta, hakika ta taimaka sosai, domin ita ce ta yiwa yaran kayan kicin, baban Mansura shi ne ya yi musu gara, yan Bauchi kawunan amare tare da sauran dangi kudi suka kawo, akwai da shin da tayi gidan hajara nan ta hada aka je kasuwa aka hado musu kaya na gani da fada, Umma ita ce ta sai musu zannuwan gado da labulaye, sadkain su kuma a hannunsu mama tace aba su, amma su kace sun bata.

Biki yayi kyau komai cikin tsari dangin uba kam ba wata gudunmawa sai dai su cika gida sunata Jan girki tare da yiwa Bilkisu shaguben tayi abin kunya kannanta sunyi aure sun barta, abokan wasanta kam sun fake da wasa sun cacaccaba mata magana . har da cewa kyau bai ji rana ba. Tun da ba mshinshni kyan Dan maciji batun ya bata ran Bilkisu amma Mansu tace kada ki damu Bily wani jinkirin alkairi ne, amma ba mutane duka ba ne suka San haka ba. Bilkisu ta ce don tani ban damu ba surutun ne bana so kawai, amma nima basa gabana.
[4/21, 01:44] A~PROF: 40. Biki ya tashi lafiya, kowa na sambarka, gudunmawar da ta samu na kudi daga abokan arziki tace da Umman su mansura ta aje mata saboda komai gada,Allah zai fito mata da nata,Bilkisu sun gama zana jarabawarsu cikin sa'a sun riga su mansu da kwana biyu suma suka gama mamanmu ta ce maigado ki shirya kije ki ma ummata kwana biyu mana,tunda baki shiga sana wayyar ba mana? Cikin murna tace kamar kin shiga raina mamanma,Asma'u auta tace zan je Aunty maigado.Bilkisu ta harare ta auta zan fa duke ki in har ki ka kuma ce min maigadon nan, tace na daina to zanje Aunty Bilki?Tace a'a ke kam ki na da islamiyya. Mansura ta dube ta,Bily ba zaki bari sai week end in Abbanmu yazo mu tafi tare ba?Saboda nima zan je gombe ne. Bilki tace,nan da kwana hudu zan fi kowa son muje tare,amma zaman nan da zan yi na kwana hudu zan sha gori da habaicin 'yan gidanmu, kan cewa na rasa mai sona."ta dafa kafadarta, kada ki damu mansu, zan tafi goben in yaso in zaku je gombe sai na baki adireshin kizo nima ba sai naje na gaida yan gombe ba
[8:46AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 13??}_

Mansura tace to shikenan muje ki rubuta min adires din, kuma zan zo da safen na raka ki tasha Bily tace to Mansu.suna tafiya a hanyar sun rike jakar su biyu kowa ya rike hannu daya,Bilkisu tana zayyane ma mansu abin da ya faru yanzu, waton abin da mahaifinta tare da kishiyoyin mama suka mata,mansura tana tsananin son bilkisu, don haka itama taji haushi tare da takaici amma sai ta ce kiyi hakuri, ba komai ke damunsu ba sai hassada,bilki ta dube ta kin sani ne mansu? Taci gaba. Wallahi duk da tsanar dana ma maza saboda wannan abin da ake min yasa nima yanzun nake jin na kosa in yi aurannan, tsaki mansu tayi tare da cewa, duk ma nawaki ke?Don Allah kada ki saka kanki cikin damuwa. Haka taci gaba da lallasinta tare da bata hakuri har suka kai gurin mashin, tace ki koma sai na ganki tace a'a sai naga tashin motarki, haka kuma har gareji ta raka. Bilkisu sai da motar ta tashi sannan mansu ta koma cike da kewar aminiyarta kamar yarda ta bar Bilkisun cikin tunaninta, suna son juna fiye da zaton mai karatu,
Ba ma kmar mansu, tana tsananin son Bily, sukan su iyayanta sun san haka, don tun suna yara ko dinki ne aka mata in ba ama Bily ba sam bazata saka ba komai sai dai ai musu tare,shi yasa ko mamanmu ma in ta dauki albashinta in har zata sai ma Bilkisu wani abu tare take saye. Umman mama taji dadin zuwan Bilkisu don duk cikin jikokinta tafi son ta domin tana da hankali, sannan tana koya mata karatu tare da addu'o'i. Bata manta wani hutu da tazo ta koya mata zikirorin sallah,gasu nan har yau tana yinsu. Adda wata yar dattijuwa ce da su kawu Aminu suka daukarwa umma suna biyanta tana tayata yan aikace-aikace,don ma umma akwai ta da juriya tare da kazar-kazar.Bilkisu tana son bauchi tana jin dadin zama da umma tun jumma'a ta damu yan gidan da labrin zuwan mansu,umma ma ta damu tana son taga mansura nan dai,ga tsarabar mansu da tasha,sai dai har lahadi ba mansu duk ta damu. Monday gidan kawu Aminu ta kwana,ta tatara ta wuce gidan kawu Abubakar ko'ina taje sonta suke su da ya'yansu.
Ran Jumma'a tana kwance kan gado umma ta tafi masallacin jumma'a adda tana wanke-wanke sai kawai taji sallama muryar mansunta ce da gudu ta fito tana fadin oyoyo mansuna.nan ta yar da jaka suka rungume juna,sai yau ki kazo? mansu na shiga damuwa,tace bari ke dai Bily,Abbanmu ne ya kwafsa min,tare da shi ma muke yana waje,da sauri Bilki ta dauko hijabi ta debi ruwa suka fita,suna cikin gaisuwa sai ga umma ta dawo,nan tace ya shigo ciki,ya shhiga suka gaisa nan kuma yayi mata sha tara ta arziki yace shi zai wuce kaduna ne,shima satin shi daya a gombe suka mishi rakiya ya tafi. Da dare suna kwance kan gado barci yaki zuwa sai hirarsu suke yi, mansura tana ba bilki lbrin tun wancan satin suna gombe,tace har kuka na yiwa Abba akan ya kawo ni nan amma ya ce sai ya tashi tafiya. Bilki tace nima haka nan duk na damu,mansu tace albishirinki?Bilki tace goro kwarya goma sukayi dariya,tace.Abba yace kafin mu dawo zai saya mana form na jamb,murna bilkisu ta somayi domin da har ta debe tsammani da karatu tunda abin na kudine

Suna tafe a kan hanya suka ji anata horn bayan su amma duk suka share
Ganin basu da niyyar tsayawa ya saka shi fitowa ya biyosu, assalamu alaikum yace musu,suka tsaya mansura ta jujo yayin da Bilkisu ta sha mur tare da kin juyowa,don Allah zan iya magana daku ko da na yan mintina ne? Mansu tace muna jin ka, yace nagode gaskiya ni dai na ganki ne nake sonki,mansu tace wa ni?Yace kwarai,tace gaskiya an min miji,sai dai wannan Bily ta dube su cikin daure fuska tace,ni matar aure ce, ita ce budurwa,dan kyakkyawan saurayi yace,ai ke kam nasan kin fi karfina shi yasa ma banzo nan ba jama'a na kaini inda Allah bai kai ni ba,kalmar nan ta kinfi karfina tana ba su Bilkisu mamaki,shin dama mace tana fin karfin namiji?Bilkisu ta daure tace,na gode da ka gane haka,yanzu dai na baka kawata,domin na ganka da alamu na masu hankali,yace nagode sosai,ni sunana Umar Faruk Sulaiman ni mutumin gombe ne,nazo gaida kanwar mamana ne a nan bauchi,sannan ina aiki a kaduna ne, tare da bankin PHB, ku fa?Bilkisu tace mu yan zaria ne,
[8:46AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 14??}_

Amma batun dogon bayani sai mun sake haduwa,yace a ina? Kuma yaya sunan kawar taki?Tace sunanta Mansura,ta nuno mishi gidan su umma daga nesa ga gidan kakarmu can in ka samu lokaci a nan zaka ji sauran batu, taja mansura dake tsaye tamkar wawiya tana jin su,yace nagode ko zan rage muku hanya?A'a mungode,cewar Bily Gidan uncle suka kwana,kani ne gurin umman mansu,adaran farooq yazo nemansu basa nan,sai da yamma suka soma shirin dawowa,anty salma matar uncle itama tana ta yaba kyan Bily,haka sanda suka taho kowa sai ya tsaya yana ta kallonta,ta saba ko zaria haka take fama da kallon nan,kullum mutane suna ganinta amma tana fitowa sun dinga kallon ta kenan. Sun idar da sallar isha'i umma tana basu lbrin zuwan bakonsu,sai ga dan aiken mansu tace,Bily ba ki kyauta min ba,meyasa ne zaki jona ni da mutum?Ko sauraran mansu bata yi ba,tace da yaron kace tana zuwa.Wasa wasa saida mansu taga bacin ran Bily sannan ta fita gurin farook,sunyi hira kuma yaji komai dangane da mansu sun yarda dajuna da suka ji yangari daya ne
Mansu tana son farooq sai dai tana tunanin Bily bata son tayi aure,ta barta don haka tayi mata shawara su aure shi tare mana? Hkan ya kusan kawo musu rigima sai dai umma ta tsawata sannan mansurta hakura.Satin mansu biyu ita kuma Bilkisu hudu Abba yazo yace zai wuce gombe ne,jibi zai zo su tafi saboda monday zasu soma zana jarabawa,don haka su shirya ran jajibarin tafiyarsu.Sun yi sallama da kowa kawunan Bilkisu sun musu dinke-dinke tare da tsarabobi, umma tace gaskiya ya kamata kuje gomben ne don haka kawu Abubakar ya saka su cikin mota yayi gombe da su sun ji dadin ganinsu Abba ma yace shi kenan ya huta tsayawa.Daren ranar ne Bilkisu cikin mafarkintan nan na fama,Yarima ke ce mata,kiyi kokarin sanin wanene Yarima kafin ki bar bauchi da safe kam suka dauko hnyar zuwa gida, zuciyarta cike da tunanin wanene Yarima?Meke faruwa tsakaninsu? Umma da mamanmu sunyi farin ciki da ganin yayansu Bilkisu har wani kyau ta kara tare da yar kiba duk da cewa ba wani jiki ne da su ba.
Sun zana jarabawa cikin sa'a duk su haye,Abba ne tsaye kan komai har suka samu shigewa Bilkisu ta samu fannin da take so na yayinda Mansura ta hakura da gefen lissafin don bashi ta nema ba,baba ya tambayi mamanmu shin wani sabon karatun ta kama?Mama tace to Allah bai kawo miji ba,ai sai aci gaba da karatun ana cikin yi in mijin yazo ai dole ne ayi auren, yace ba wani,na lura Fatima akwai burin daki kaci akan yarinyar nan, amma nasan maganin abin ya fita yana zage-zagenshi,mama ko cewa tayi Allah ya kyauta. Haka rayuwa taci gaba abubuwa na faruwa yau sauki gobe tsanane shekararsu ta farko, lokacin ne farooq ya matsa kan batun auran su da mansu.Tun dama ita ce mai jan lokaci wai ko Bilkisu itama zata samu ko da cikin school din su ne amma duk son mata irin na yan jami'a babu wanda ya taya Bilkisu,sai dai kallo wasu har tuntube suke yi in suna tafe suna kallonta,bisa ga wannan dalilin ne yasa mansura ta jira yi zuwan farooq wannan satin da yake kaduna yake aiki shi yasa duk sati yake zuwa shima yazo..
[8:46AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 15??}_
Da tashi damuwar tason ya turo magabatanshi zaman gaurantaka ya ishe shi, yana bukatar mace a kusa dashi. Don kada yaki yarda da batun yasa tasha kunu kafin ta bude motar ta shiga ganin yanayin tane ya fadar mishi da gaba saboda nan duniya ya tsani yaga mansura cikin damuwa,yace meya tasani yaga mansura cikin damuwa,yace meyafaru.Sweetyna?ta sake daure fuska gaskiya ni ina ganin zai yi wuya muyi aure. Cikin tsoro yace,saboda mene?Tace saboda Bily,gaskiya farooq ba zan iya aure in bar Bily ba,sai dai ka zaba cikin biyu,ko dai ka aure mu tare,ko kuma mu hakura da juna zan jira ta in ta samu sai muyi tare,baki ya saki tare da bin ta da ido,dariya ma ta bashi yana dariya yace kuruciya kenan,kowa da irin tasa,haushi ya kama ta,tace dariya kake min? Kuma nice kuruciya shekara ashirin shine kuruciya ko?Ta juya zata fita,ya riko ta haba mansura,me yasa kike irin wannan magana? Yaya ma zaki ce in auri Bily?Gaskiya bazai yiwu ba.Bily tafi karfina, bani da halin da kera gidan da zan sakata. Cike da mamaki ta kalle shi kana nufin sai me hali ne zai aure ta, ka kalli gidan su mana. yace ke baza ki gane bane,kuma nima ban san yanda zan miki bayanin yanda nake ganhnta bane,so mu bar maganar.tace to shikenan,Allah ya hada kowa da rabon shi,zata fita yace ban fa gane nufinki ba?Tace ai zabi na baka,kuma kace mu bar zancan cewa zaka aureta,wanda haka yana nufin ni da kai sai bankwana.Ta fice ta bar shi zaune.Mamakinta yake yi yasan takan komai in ta kafe sai dai ya hakura ko kuma ya hada tada Bily,don haka sai ya tashi motarshi sai gidan su Bily,dai dai wannan lokacin tana kwance cikin daki bisa gado jikinta rinkif da zazzabi.Asma'u auta taje ta siyo mata magani,mama tana kofar dakinta yayin da su ladiyo suke zaune a gindin murhu, suna cin tuwo hira suke yi kasa-kasa ba a jin me suke fadi sai dai ajiyo dariyarsu,yaro ya shigo yace wai an ce ana kiran Bilkisu,nan take suka katse dariyarsu,kuma suka shiga kallon-kallo, mama ma taji daban don ba a taba hakan ba,tace in ji wa?
Yar yace in ji wai farooq,mama tace kace tana zuwa,ta shiga daki tace ke maigado ki zo saurayin mansura yana kira, ta sauko tana tunanin anya lfy?Don ko yaushe yazo tare da mansu suke zuwa, sai ta shigo su fita tare tana fita ladiyo ta kwala ma yarta Basira kira,tace zo nan Basira,suka yi mata rada ta fita da gudu,jim kadan ta dawo da gudu tana tsugumawa a gabansu tace wani ne a mota na ganta,a gidan gaba ta zauna,karime tace kin ji ko?Gaskiya gobe zamu koma kusfan na kada mlm yayi mana haka?Salame tace na ma kasa mgana,saboda ko kwanan nan nawa muka bashi? Ladiyo tace niga bashi ma da ake bina ban biya ba,na kuma ciyo wani muka hada muka bashi haka nan suka ci gaba da tattaunawa tare da shirya yanda zasu yi.A cikin mota farooq ya rattafo ma Bilkisu yanda suka yi da mansura, amma sai yace mata shi ne nazo in ji naki ra'ayin. Ran Bilki ya baci tace muje gidan,a fusace ta shiga dakin mansura, bakin gado ta same ta ta zuba tagumi cike da takaici ta dube ta,nagode mansu tallat ma ki ke yi,.
ki sani koda Farooq ya amince ni ba zan yarda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login