Showing 21001 words to 24000 words out of 79064 words

Chapter 8 - MEKE FARUWA BOOK COMPLETE BY HALIMA K. MASHI.doc

wuyanta. Tunda ta fito take kallon bilkisu a zuciyarta kuwa fadi take masha Allah, ta zauna kan kujerar ta dubi farooq da suka zube kan carpet tace idonka kenan ko farooq?Yayi murmushi yace ayimin afuwa umma, ta dubi su mansura tabe to wace ce matar taka cikinsu ko dukansu ne?Yana 'yar dariya ya nuna mansura sannan ya mika mata dady,kiyi hakuri umma ko gombe ma ina dadewa ban zo ba,saboda yanayin aiki wannan karon ma dan hutu ne muka samu,shi ne muka zo gaishe ku, tace to mungode Allah yayi albarka,
.ta nuna Bikisu wadda kanta ke sunkuye tace wannan fa?Bata san me yasa yarinyar ta tsaya mata a zuciya ba,farooq ne yayi magana,kawar mansura ce itama ta biyo mune tayi gaisuwa,umma tace mungode kwarai amma tana da aure ne?Yace tukunna dai tace to Allah yabaki miji na gari,shi da mansu suka ce amin, tace umman taka fa? Tana gaishe ki su sumayya ma ina ga yau za su zo,yaya gurin su anty salma su Aisha?Ta ce duk suna lfy sai gobe zasu zo gaida mai martaba,yace sai dai a gaishe su dan gobe zamu juya Modibbo ma mutane sun mishi yawa bai san ma munzo nan ba,tace yau kam Modibbo ai har dare amsar gaisuwa zai dinga yi.yanzun nan ma nake ma takwaranshi magana yazo yaje ya gaida shi tunda kwana uku zuwa hudu zai yi ya tafi farooq yace Al'amin yazo ne? Tace jiya me martaba yace mishi yazo gida yayi salla farooq yace ya fito ne?Yaushe rabon da mu hadu anfi shekara7,Umma tace kai dashi duk ba masu son zumunci bane bari in kira muku shi ku gaisa,
Dai dai nan wasu 'yanmata su biyu suka soma jere kayan ciye-ciye da shaye-shaye a gaban su mansura da farooq. Bilkisu gabanta ya tsananta faduwa kanta kuma yana kasa wasa take da zoben dake karamin yatsanta, umma ta kira layin Yarima tace babana ga yayanka ummar faruk kazo ku gaisa yace to su dan jira shi zai yi wanka, tace babana kayi sauri na sanka fa,yace to su ka ci gaba da hira tare da 'yan ciye-ciye, bilkisu kam kasa cin komai tayi kuma sai ta samu kanta da matsanancin jin nauyin umma,kula da hakan da umman tayi na kin ki cin komai da bilkisun tayi ne yasa tace ke kin ki cin komai saboda me?Ta dubi umman cikin jin kunya tare da dan murmushi,ta ce na koshi ne.Umma tace ka'idar gidan nan in ka shigo sai kaci abincin gidan,tasa hannu ta dauki yankakken apple ta saka abaki,tana taunawa a hankali idanun umma na kanta yarinyar sha'awa take bata,ta dubi mansura, yaya sunan kawar taki ne?Mansura tace sunanta bilkisu a ranta tace ta ci sunanta,Bilkisu maigadon zinari..

Kamshin data ji ne yasa gabanta ya tsananta faduwa menene take jine kodai mafarkin tane na yau da kullum?Muryar nan ta Yarima ta jiyo mai cike da kasaita da son girma, ya dubi farooq cike da sakin fuska yace,yayana sannu da zuwa,ashe da rabon zamu gaisa ne, farooq ya mike tare da mika mishi hannu,suka yi musabaha yana tambayar farooq iyali ya nuna mansura yace gata nan,ya dubi dady dake wasa kusa da umma, yaronka ne wannan? Yace eh Yarima ya tsugunna kusa da daddy yace Hello handsome, mansura tace ina yini, ya zuba manyan idanunshi kan fuskarta, yace lafiya yaya boy da yayana tace lfy,Bilkisu kam ta kasa dago ido ta kalli Yarima ganinta irin mafarkin da ta saba yi ne,mansu ta tabata tare da yi mata alama da ido wai su gaisa da Yarima, ta dago ta dube shi dai dai sanda ya zubo nashi idon kanta miyan bakinta ya kafe,ta kasa motsa lebanta ma bare ta iya furta wani abu,shi dai ya kauda kanshi amma zuciyarshi cike da mamaki,kyawunta tafi kama da larabawan gabas ta tsakiya,
Fiye da yan nigeria ta kuma kallonshi tana son ta tabbatar da cewa ba mafarki take yi ba,don haka tace Yarima! Ya kalle ta da sauri tayi dan murmushi har yanzun baka huce ba kenan?Cikin mamaki ya dube ta,a ina ki ka sanni ni?Ta dubi mansura sai kuma tayi shiru. Farooq yace cikin mamaki,kin san shi ne Bily?Tace tunda bai gane ni ba bar shi kawai,shiru Yariman yayi yana son tuna inda ya santa,umma cikin dan murmushi tace babana baka santa ba? Ya mike tare da fadin ban taba ganinta bafa, cike da rainin wayo ya fada,har ma su mansura da umma basu ji dadin yanda yayi ba,musamman mansura da tasan cewa Bilkisu ba ta da son magana da maza to ko shi ne Yariman mafarkinta?Shi ko ciki ya koma bilkisu ta bishi da kallo,Yariman mafarkinta ne tabbas, meyasa bai gane taba? Shin ko shi ba ya mafarkinta ne?Abokin wasanta tun suna yara? Suyi fada suyi wasa.
[8:46AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 25??}_

Har suka koma gidan Modibbo mamakin Yarima tayi tana kwance a kan katifa a masaukinsu, Mansura ta dafata Bily a ina ki ka San Yarima? Cike da nadamar yi mishi magana ta ce shi ne Yariman mafarkina, tun muna yara amma dubi yanda yayi min, ba laifinshi ba ne ni ce da na mishi magana, Mansura ta dan yi murmushi kin manta ne cikin mafarki ne? Kin manta cewa mafarki ba gaskiya ba ne? Sam Bilkisu ta manta da wannan batun har ma ta ji haushin kanta game da maganar da ta mishi, tayi data sani sannan ta cika da al'ajabin ganin Yarima yanda ta San shi a mafarki haka yake.

Farooq ne zaune gaban tsohon suna tattaunawa cikin nisan dare, ya sanar mishi da Abu buwa masu yawa game da Bilkisu kuma tsohon ya yi mishi alkawarin ganawa da ita, da safe bayan yayi istihara kan lamarinta, hakan ce ta kasance da safe inda ya gana da Bilkisu ya yi mata yan tambayoyi domin yaga Lamari da yawa cikin al'amuranta, ya dube ta jikata ki kanyi mafarki ne haka ko na ruwa ko na gini ko na wani mutum? Tace eh to na kan yi mafarkin wani tun ina yarinya kuma har yanzu ina yi sai dai in ban kwanta ba, ya dube ta kamar ya ya kike yi? Tace ina mafarkin shi wani dan sarki ne, muna wasa kuma yana yawan ce min in je in nemi tarihinsa, tsohon ya kalle ta na tsawon lokaci tamkar me son ya karanci wani Abu a fuskarta, sannan yace Bilkisu In'sha Allah za ki yi aure, kuma a yanda na fahimci al'amaran mijin naki zai kasance wani ne ma'ana babban mutum ne, kuma lokacin ya kusa sai dai naga rigingimu da yawa kici gaba da addu'a nima zan taya ki, kanta a kasa tace In'sha Allah zan dinga yi zuciyar ta kam tab da tunanin wai ta kusa aure? Kuma mijin dan babban gida ne?

Yanzu zan ba ki wasu addu'a zaki dinga yin su a lokutan sallah da kuma bacci, duk da cewa na lura ke din mai tsayawa ce akan addininta, Allah ya yi miki albarka, tace na gode kwarai, In'sha Allah zan kiyaye, Mansura ko da ta ji labarinn da suka yi da tsohon daga bakin Bily murna ta hau yiwa aminiyarta ta kusa aure, tace da yace mijin da za ki aura dan babban gida ne sai na raya Yarima, Bilkisu ta kalle ta cikin sauri ki ka raya Yarima! Mansura ta ce sosai ma, Bilkisu taja dogon tsaki don Allah ki bar yi min mugun fata,ni fa Yarima nan ba wai ina sonshi ba be, ko cikin mafarkina aboki na dauke shi tunda shekarunmu daya, sannan ma sabonmu cikin mafarki ne tunda dibi wulakancin da yayi min gabanki Mansura ta ce Aa ba zamu shirya ba, ni fa bani da burin Auren yaro karami , Yariman nan fa na girme shi, Allah ya tsare ni da auran karamin yaro ko da Modibbo yace babba ne zan aura ina zaton yana nufin babba mai shekaru, shi ne kuma ya dace dani, Mansura ta ce ba wani ke dai kin cika ra'ayi kuma In'sha Allah shi ne mijin ki, fita Bilkisu tayi har ga Allah cikin ranta ta tsani zancan Yarima. suna cikin shiri sai gombe yau, kuma sai Kaduna, sun gama shiri tana cikin wani Jan yadi mai ratsin baki, tayi kyau sosai Mansura ta ce don Allah kiyi kwalliya ki dan yi shafe shafe zaki yi tamkar balarabiya, tace Aa bana so yar hodannan ta ishe ni tana magana tana fesa turare ta dauki karamin kum tana taje gashin ta zuwa baya farooq suka shigo shi da Yarima da kuma magajin Malam, da saure ta dauke dan kwalinta ta rufe kanta amma duk da haka Yarima ya gani, magajin Malam kam cewa yayi Masha Allah ya dubi Yarima ya mishi rada, kaga hurul inin duniya? Yi yayi tamkar bai ji ba kuma yaki kallon inda take tun da ya kalle ta sau daya, kan kujeru suka zauna Mansura ta gaishe su, suka amsa farooq yace Mansura babu rabon ku kalle hawa yau zamu tafi su kuma yau zasu fara, Mansura ta kalle Bilkisu, Bily ko mu tsaya ne? Ta yatsina fuska, A'a aikina Ku ku tsaya ni kam zani koma bakin aikina Yarima ya saci kallon ta wannan ya kula tana da gadara, shi zata ma gadara? Yaji bata iya ta gaishe shi ba don ma rainin wayo jiya har da nuna tasan shi ? Gashi yanzu ma ko ta gaida su magajin Malam yace ina kwana Malama? Ta dube shi lafiya, ya ya sallah ? Ya ce Alhamdulillah, jin muryarta ta saka magajin Malam rudewa yayin da Yarima yayi tsam da ranshi yana sauraronta, suna hira ne jefi jefi Yarima yace ma farooq mu zamu tafi dama mun zo gaida tsohon nan ne nima gobe ko jibi zan koma in ban zo yau ba maybe ba zan samu zuwa ba farooq yace to kun gaisa ne? Yarima yace kasan shi da mutane, mun zo yana da baki ya dubi magajin Malam duba mana tsohon nan ko bakin sun tafi,

A ran Bilkisu fadi take wannan dan rainin wayo ne,ban da haka mene nashi na Aiken wannan, shi kuma har da zuwa tashi tayi ta fita ta shiga gurin hajiya Fati, ta same ta tana shafa ma yarta mai,yar kyakkyawar yarta mai gashi, ta zauna tare da fadin baby zo nan in shafa miki man, dama gata da son yara. Hajiya tace kuna ta shiri ko? Tace wlh dan ma wannan Yarima ne ko wanene? Ya zo yana jiran Modibbo su gama da baki da yanzun mun dauki hanya, tace Aa Yarima yazo kenan? Tace ina jin shi din ne taci gaba da shafa ma Aisha mai tana sama yarinyar kaya sai ga Yarima ya shigo tare da sallama hajiya tace Aa mutanen wacan kasa yaushe a gari? Yace shekaran jiya nazo, gobe nake tunanin tafiya suka gaisa da yar hira Bilkisu tana jin su ta taje ma Aisha gashin ta sai nan ta dago kai ta dubi hajiya tace, hajiya ina ribbon din ta? Ta jeho mata sai ta dan kalle Yarima cikin sa'a suka hada ido ita ce ta soma kauda kai shi kuma ya mike bari naga dan takwarkwasasshen tsohon nan da ya ki mutuwa, hajiya Fati ta ce lallai haka ma zaka ce? Albarkarshi fa kake ci ya tafi.
Hajiya fati tace Yarima kenan,tsohon nan naka yana matukar ji da kai,kai ko tsiya ka ke mishi,Bilkisu kan ta duk adaure tun jiya tana son sanin wani abu da Yarima,tace shima yana da dangantaka da Dattijon nan ne?Ta dubi Bilkisu baki bude sannan tayi murimushi jikan shi ne kuma shine jika mafi soyuwa agurin shi, kenan suna da dangantaka da farooq? Cewar Bilkisu kanta bata amsa sai ga mansura ta shigo ki zo ga wayarki ta amsa ta fita tana amsa call din sa'adatu sani abokiyar aikinta ce, farooq ya cekuzo mu tafi fa,bilkisu tace to bayan ta gama amsa waya. Yarima zaune gaban kakanshi bayan sun gaisa ya dan mishi tsokana irin ta kaka da jika,sannan yace Aminu ana can ana ta shirmen ko?Ya shafa keyarshi tare da fadin a haba dai muna karatu ne ba shirme ba,yace to yaya batun aure kuma ina fata ka soma shirin yi?Ya dubi tsohon haba wane aure?Ai ba yanzu ba,sai yaushe?Sai na gama karatuna na fara aikina nahuta,yace nan da yaushe kenan? Yarima cikin jin dadi ya gyara zama domin yasan cewa in tsohon ya daure mishi
[8:47AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_ MEKE FARUWA 26??}_
In tsohon ya daure mishi gindi ba zai yi ba,to dole ne mai martaba ya hakura, ya soma lissafi, shekara 7 zan yi zuwa 8 yanzu nayi 4 ina cikin na5 , saura 3 da yan watanni, in fara aiki duk dai da komai mu barshi nan da shekara 7 ,lokacin shekaruna sun kai 31 kenan.

In soma neman Auren zuwa yin Auren kila ya kai shekara ko biyu haka in an hada tare kenan, tsohon yayi dan murmushi yace haka ne, to Allah ya taimaka, ya dauko wani Kofi ya juye ruwan zam-zam a ciki, sannan yayi wata addu'a ko nace ya tofa addu'a sannan ya mika mishi,

Yarima ya saka hannu biyu ya karba ya kafa kai ya shanye tare da addu'a nasan zaka zo kafin ka tafi ko? Yace eh to zan zo kila gobe ne fa tafiyar, yace to kayi kokari ka zo din dan zan baka wasu addu'o'i su farooq suka yi sallama suka shiga falon dan yiwa tsohon sallama, kusa da Yarima farooq ya zauna, su Mansura suna gefe Bilkisu a ranta du'a'i take yi Allah yasa kada tsohon yayi maganar matsalar ta a gaban wannan sarkin girman kan, farooq yace mu zamu tafi, tsohon ya ce to Ummarul Faruku, Allah yashi albarka, kawun ka ya yi min bayanin tsaraba, Allah ya kara budi mun gode da zumunci, to Ku tashi na sallame Ku har kai Aminu, ya nuna Bilkisu ke kuma jikata bari in dan ganki.

Ya dubi Dady dan zo nan, dady yaje gunsa ya shafa kansa Allah ya yi maka albarka, Mansura ta ce mun tafi sai wata rana, ya ce to ki kula da zumunci kada ki biye wa mijinki, suka yi dariya tare da mikewa, Yarima kam dama ranman gim kuma ya riga su fita, bayan duk sun fita ya dubi Bilkisu zaki samu dawo wa nan kusa? Tayi shiru sannan ta ce matsala ta yana yin aikina, amma da na samu dan Hutu zan zo, yace shi kenan amma ki rike addu'o'in nan da kyau, tace na gode, Ya ce zan ci gaba da addu'a nima a nan, tashi kije Allah ya yi miki albarka, ta tashi tana godiya suna sallama da Yarima Bilkisu ta fito, ya bita da kallo a ranshi yana tunanin shin KO dai yar uwarsu CE?

Menene hadin ta da. Kakanshi? Ya dan kalle ta yana jin mamakin kyan da cikar halittarta yake yi sai dai kuma kauyanci irin na matan arewa ya hanata ta nuna kyaunta, ya shiga motar bayan shima ya yi sallama da farooq.

Mansura duk murna ta cika ta son surukarta ya kara shigarta, haka nan Bilkisu ji take tamkar mahaifiyarta CE,ta zayyane mata yanda suka yi da tsohon, itama taji dadin jin hakan ta kuma yi fatan alkairi taso su biya gurin Umman Mamanmu amma suna sauri ne jiya da suka je Bauchi, zariya suka tsaya Mamanmu tasha murana jin batun da tazo dashi washe gari da sassafe suka nufi Kaduna ta koma bakin aikinta.

Yarima yana kwance a dakin shi can malesia, ya rasa dalilin da yasa zuciyar shi ta cika da son ya tuno inda ya san yarinyar wadda zuciyar tashi ta mata lakabi da beauty, amma ya kasa, ya sani bashi da saurin mantuwa da sun taba haduwa kyanta ba mai saurin gushewa a rai ba ne da zai tuna, wata zuciyar tace meyasa ka damu kanka da tunanin inda kasan wannan yar kauyen? Tsaki yaja sannan ya mike yana ayyanawa a zuciyar shi, cewa cikin lokutan da ya tsara bai cire na tunanin kowa ba,saboda bai ga macen da ta isa ya tsaya tunaninta ba, can haka ya tashi ya nufi kicin don kora wani abin mai dan sanyi.

Dattijon ya maida hankali ne kan rokon Ubangiji ya karkato hankalin jikanshi ga aure, duk addu'o'in da ya yi mishi cikin ruwa da wadanda zai dinga karanta wa duk saboda hakan ne.

kwana uku tsakani zuciyar Yarima ta tsumu da sha'awar yarinyar da zuciyar shi tasa mata suna beauty, in suna kwance da chelen sai ya dinga rayo beauty, in su Vicky ma yanzu ana dai harka ne kawai, a tsarin shi baya son ya nemi yar arewa don baya son raini, su din basu waye ba, bayan haka ma baya son ya samu zubar da darajar gidansu, to meyasa ya samu kanshi da jin sha'awar yarinyar, ya tuno cikar kirjinta da yanda mazaunanta suke juyawa, lokacin da zata fita daga cikin masaukinsu na gidan kakanshi, tunanin yanda yarinyar take yaji irinta ta yaya, zai kai ga samun haka? Duk da ya kula sai saka yake yana warwarewa, kafin daga karshe ya yanke shawarar neman farooq, bayan sun gaisa ne farooq yace, lallai yau za'ayi ruwa da kankara Yarima yayi murmushi yace dan dai da ba ka da number ta ne shi yasa bana gaisuwa.

yace, haka ne kam dama ina son in tambaye wannan yarinyar ne wani Abu shin kana da number din ta? Farooq yace wace kenan? Yarima yace, wadda Ku ka zo tare din nan,. Ya ce OK kana nufin Bilkisu ba? Yarima yace, kila ita din ce, kawar dai matarka. Farooq yace kana sonta ne?

Ko kusa, zan dai tambaye ta ne wani Abu.farooq dai ya tura mishi number. Yarima ya soma tunanin yanda za ta dauki abin da zai gaya mata, amma sai yace bari ma dai ya fara sanin ina ta san shi? Kuma yaya suke? Ma'ana shi da ita
[8:47AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 27??}_

Ta dan watsa ruwa don taji iska kamar yanda ta saba yi kullum in zata kwanta, ta shafa humra mai hade da wani turare mai dan karan kanshi, ta saka rigar baccinta haye gado. Mansu ta shigo tana cewa.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login