Showing 15001 words to 18000 words out of 79064 words

Chapter 6 - MEKE FARUWA BOOK COMPLETE BY HALIMA K. MASHI.doc

%???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 18??}_

kwanan mai martaba biyu a malaysia kafin ya wuce Saudi yayi kwanakin ne a wani shahararren masaukin baki dake cikin birnin na malaysia. Yarima sam bai yi mamakin shirun da mahaifin nashi yayi mishi ba. Domin yasan zai yi maganin abin, wani Abu da yaba magajin Malam mamaki, gidan Yarima yake kwana kuma ganin da mai martaba ya mishi bai sa Yarima ya daina kwana da mata guda biyu a shimfidarshi ba, don haka magajin Malam yake kwanciya a falo ko dayan dakin Yarima, magajin malam dai shine babban abokin Yarima kuma shi da ne ga waziri, mai martaba yana son shi tamkar Yarima. Shi yana karatun injiniya, yayin da Yarima ke karatun likita mai martaba yazo da shi don yaga abokinshi ya juya gida shi kuma ya wuce Saudi, bayan sun ga tashin mai martaba suka dawo gida, kai tsaye fridge magajin Malam ya nufa a kitchen ya dauko robar ruwa, kusa da Yarima ya zauna da yake kokarin kiran Ummarshi,

Layin ya ki shiga, ya dubi Yarima yana son yin magana amma yasan halin yan kayan shi, don haka sai yayi nufin share zancan amma kasancewar Yarima mai matukar saurin fahimta sai yace um'hum ina jin ka, magajin Malam yace ban yi magana ba.

Yarima ya dube shi cike da kasaita irin ta yayan sarakuna, sannan yace kana so yin maganar ne ai, magajin Malam yace nasan halinka ne zaka iya cewa yanzun ba time din amsa ba ne, Yarima yace tambaya zaka yi kenan?
Magajin Malam yace tun shekaran jiya nake son yin tambayar, Yarima yace bata dame ka ba ne da kayi ta koda ba zaka samu amsa ba.

Magajin Malam yace zan iya tambayar yanzun ko? Yarima ya tabe baki tare da fadin in kaso ba, magajin Malam ya gyara zama, dama ina son jin me yasa kaci ka son mata? Kuma me yasa ka canza daga silent din ka zuwa mara jin magana? Yarima ya ajiye wayar a gefenshi sannan ya ce na kasa samun Umma din ma ya kalli magajin Malam wacce zan amsa maka? Duka in har zan samu, ya ce to mata abin so ne don su ne nishadi na karshe, duk cikakken namiji mai lafiya yana son mata, sai dai kowa da nashi salon son, sannan ban canza ba har yau ina nan a silent dina, magajin Malam yace ka canza domin a da in har mai martaba ya hane ka da yin wani Abu ka bar shi har abada, amma yanzu ba ka damuwa da hakan. Yarima yace me ka gani? Ya ce in daina ban daina ba? watannin baya mun zonan dashi mun sameka da mace. Sai kuma gashi wannan zuwan ma gara wancan cikin sutura kuke wannan karon ba Ku da maraba da tsurara, sannan kuna cikin halin sumbatar Juna, kilama damun jima ba mu shigo ba mu same Ku cikin wani halin. Yarima ya zuba mishi ido babu wani hali da zaku same mu da ya wuce wannan domin ni kamar yanda ka sani komai da lokacin shi, wannan lokacin ne na wasanni kuma duk nacin mace ba zan wuce mata haka ba ka fahimta?

Sannan kai ma zan tambaye ka wancan zuwan da Ku ka yi ka ji mai martaba yace kar na kara? Hasalima bai ce min kala ba. Haka nan wannan zuwan kaji ya yi min magana ? Magajin Malam yace amma kasan hausawa sun ce shiru ma magana CE, ta ishi mai hankali ko? Sannan kana ganin shirun da ya yi maka yana nufin ya ji dadin abin da ka aikata ne? Yarima gairgiza kai ko kusa nasan ba haka ba ne, INA cike da sanin zai dauki mataki kaina, sai dai ina tsoron irin hukuncin da zai yanke min, magajin Malam yayi dariya tare da fadin, ai na san ka shirya daukar kowane hukunci ne tunda ka kasa daina hulda da matan duk da yana garin ka ci gaba da kwana da mata har biyu kasan ko matanka ne na sunna addininka bai amince maka ka kwana da su, su biyu ba ko?

Magajin Malam yace wane hukunci ka ke ganin mai martaba zai yanke maka? Yarima yace sai Allah shi ne ya sani sai kuma shi. da na zace zai CE zai mai da ni Nigeria in yi karatu a ga ban shi yanzun kam na bari wannan tunanin tunda a gabanka ya kara min kudi, magajin Malam yace ni ko sai INA tunanin kila ya yi maka aure........ Da sauri Yarima ya tashi zaune au! What? Yayi yar dariya kada ka manta am 22 fa yaushe aka haife ni, da har zan yi aure? Please bar wannan zancan ban isa aure ba, magajin Malam yace kai ko ka isa har ko ka zarta tunda da mata biyu kake kwana. Yarima yace tab da ko ya yanke min hukunci mafi muni, ni fa aure nayi da wuri in yi shi nan fa shekara goma masu zuwa, kana da garantin kaiwa wannan lokacin! Cewar magajin Malam Yarima ya mike tare da fadin, in na biye maka sai in shiga time din wanka na, ya nufi dakin shi magajin Malam ya bi shi da kallo yana kuma mamakin Yarima, yaro mai shiru shiru da kamun kai, yana da natsuwa ta karshe shi yasa yake samun girmamawa gurin al'lummar Bauchi, shi kanshi ban da ya gane ma idon shi abin da Yarima yake yi zai musa, yana da girmama lokacin shi yasa yake da cika alkawari in har ya dauka.
kwankwasa kofa aka yi tare da neman izinin shigowa, magajin Malam da ke zaune yaba su izinin suka shigo, turawa ne mace da namiji, sun gaisa sannan suka tambayi prince ya gaya musu cewa yana wanka, suka dubi a gogon da ke manne a bangon falon sannan suka jira shi yayi musu izinin zama, jefi-jefi suke hira suna kallon fim din da suka samu magajin Malam yana kallo, Yarima ya fito cikin bakin jeans tare da shirt mai dogon hannu tare da layi-layin baki da fari takalminshi mai shegen kyau tare da tsada shima baki ne, sumar kanshi irin ta asalin fillo tasha gyar tana ta sheki, kamshin turaren matador yana tashi a jikinshi, Dora ta kalli M, tace He's handsome guy, ta mike ta isa gurin shi cikin kasaita ya kalle ta tare da fadin ya take?

Gefen kunnashi ta sumbata sannan ta rike mishi hannu ya dubi magajin Malam wanda haushi ya hana shi magana, yace abokina bari mu shiga school da kai magajin Malam ya amsa suka fita yaja tsaki Allah yasa mai martaba ya yiwa Yarima hukuncin barin wannan kasa da lalcewa tayi mata yawa.

Mai martaba Alhaji Isma'il Abdullah ya kammala umrarshi lfy, kuma ya matsu ya dawo gida saboda matsalar dan shi Yarima, Al'amin yayi addu'o' masu yawa kan Allah ya shirya mishi nutsattsen yaron nashi sai dai wasu lokutan yafi ganin laifin shi da ya dauko shi ya kawo shi wata kasa masu wata irin tarbiya babu mai saka ido babu mai tsawatar wa ya kama mishi gida mai tsadar gaske sannan ya cika mishi account da kudi lallai yace mishi je kayi yanda kake so, duk da cewa ya halasta mutum yaje ko ina ne dan neman ilmi shi yasa duk abin da Muslim ya tsara mana in munce zamu bar shi sai mun gaba dai dai ba, wannan shi ne dalilin da yasa aka ce in danka ya balaga kai mishi aure, mai martaba ma yace wannan ne ya dace da Yarima wato aure, kuma yasaha alwashin da ya sauka gida zai yi shawara da mutum daya, ya san tsohon zai taimaka mishi.

Cikin bacci taji ana girgizata, Aunty in ji Mamanmu, ta yi mika tare da hamma sannan ta sakko jikinta a mace zuciyarta cike da tunanin mafarkinta Yarima ne a mafarkin yake matsa mata da son ta nemo labarin shi, har ma suka yi rigima don tace me sanin labarin shi zai kareta da shi? Yayi fushi ya tafi yace mata ba ya kara zuwa sai randa ta samo labarin shi, ta mike tana tunanin dama ta huta don itama ta gaji da mafarkin shi....
[8:46AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 19??}_

Bilkisu ta dubi Mansu, kizo muje tare, ta saba dady a kafada maimakon nonon da take bashi, tayi gaba zo muje, gurin shirya abincin. Shagala abokan farooq suka yi da kallon wannan baiwar Allah, tsarki ya tabbata ga Ubangijin da ya kagi wannan yar tahalika, basu kara tsinkewa ba sai da ta soma gaida su da wannan zazzakar muryar tata, cikin in ina suka amsa mata har ma taji nauyin hakan ta koma falo in da su Sakina suka shagala da kallon wani Nigerian film, a tashar African magic, Mansur ne ya soma magana, abokina ina ka samo wannan zukekiyar yarinyar kaman tasha hatimin Aninabi Yusufa don kyau?

Sani ya amshe iya gane ganena ban taba ganin mace mai kyaun ta ba, farooq yace wanene zai shiga a cikin Ku? Sani yace tab ni wannan tasha gabana, sai dai ko su mansur ko Aminu, Aminu ya ce ni ba Ku ji ban tan ka ba? Dan nasan wannan daga gidan sarauta, sai ko gidan wani shugaba ko na jiha ko na kasa, duk tadin da suke yi Mansu tana jin su wannan Abu yana daure mata kai, farooq yace yaya za Ku ce mata, yarinya ce mai hankali, ko ilimi, da saukin kai, mansur ya ce barni dai wannan ka kalle ta da kyau kuwa? Firgita ni take yi da kwarjininta mai ban al'ajabi, in har na aure wannan tuni zan zama zauna nan, duk suka sa dariya, Mansu ta damu tana son sanin MEKE faruwa ne kowanne namiji ke fadin tafi karfinshi...?

Sai yamma suka baro gidan Mansu, ta cika yaran su Sakina da Maryam da kudi tare da kayan shafa. Bily ko kaya ne kala hudu na salla da farooq yayi mata, kanta amsa sai da suka hau sama da Mansura, don tace sun yi yawa ba zata karba, kuma sun yi wahala da ita da yawa, yaushe ne itama zata samu ta kwatana musu? Mansu tace wannan kuma na Allah ne shi ne mai yanda yaso ke dai ki dauka, Allah ya bar mana zumunci.

************************
magajin Malam ya dubi Yarima, prince don Allah ka sake hali ni zan tafi kaga har mutane sun soma shiga jirgi, please Yarima be a Muslim, Yarima ya kalle shi yanzo ni ba Muslim ba ne? To ka zama cikakke. I will do my best, magajin Malam yace ni fa har mamaki na ke ji, gaba daya ka canza Yarima ya dafa shi na sani kana tsoro ne kada nazo Niger in yi abin da zai zubar da mutuncin gidanmu ne I'll never do it kada ka damu zan kula, Yarima yana kallon magajin Malam har ya shige jirgin don zuwa gida.

Mai martaba ya sauka lfy jerin gwanon motoci ne suka zo filin jirgin don daukar yallabai, ya kashingida bisa kafet ya dafa tuf-tuf dan hutawa, gefenshi kuma uwargida ce sarautar mata ta jera mishi kayan shaye- shaye da ciye- ciye. Hajiya salma kenan mace mai mutunci da sanin ya kamata, gata da son addini tare da tausayin na kasa, gefenshi ta zauna tana tare da cewa yako lbrin autana?

Cike da sakin fuska ya ce autanki, lfy lau, ya kara girma tare da zama namiji sosai, Hakika kasar ta amshe shi tamkar balaraben kasar misra suka yi dariya, tace shekara biyu kawai da ban ganshi ba shi ne ya zama duk wannan? Yace zaki ganshi zan shirya miki zuwa tace shifa ba zai zo Hutu ba ne? Ya dube ta zai ci gaba da zuwa hutunshi a Saudi ne, duk da cewa ina tunanin nan gaba kadan wani sanadi zai kawo shi nan gida, hira suke yi yana cin abincinshi, taso ya sanar da ita ko menene zai yi sanadin zuwan Yarima, amma sai yace ta bari in lokaci ya yi zata sani.
kamar ko yaushe in har zai je gurin dattijon sirikin nashi yafi son ya fita shi daya kuma yaja motar da kanshi kamar yanzu kenan, karfe tara na dare ne yaja motar dan zuwa gun surukin nashi ne shiga dakin Modibbon ya sanar mishi da cewa ga mai martaba.

Bayan ya zauna suka gaisa da tsohon mai tarin shekaru masani ne na Qur'an and hadisai, Allah ya yi mishi baiwar sanin abubuwa da dama, shi ba mishiriki ba ne, baya duba ko bugun kasa, tsoho ne mai bautar Allah tare da takawa, shekarunshi dari babu uku amma in ka ganshi zaka zata bai fi saba'in ba, wasu suna gani tamkar waliyi ne Allah dai ya bar ma kansa sani cike da girmamawa mai martaba ya gaida Modibbo tsohon mai daraja ya amsa cikin sakin fuska da kulawa ya tambaye hanyar da kuma abokinshi wato takwaranshi Yarima Modibbo mai martaba yace yana lfy yace a gaishe ka,

Ya gyara zama, yanzu ma matsalarshi ce ta kawo ni, tsohon ya tattaro hankalinshi gurin mai martaba sannan yace gaba, zuwa na biyu ina samunshi da mace hankalina ya yi matuka gurin tashi, yanzu da na yanke shawarar in yi mishi aure, sai a tura mishi matar can, ko yaya ka gani? Tsohon yayi shiru tamkar mai nazari, sannan yace haka ne yafi dacewa domin saboda gudun wannan matsalar shi yasa musulunci ya yi horo da ya'yanku sun balaga to Ku musu aure,

Mai martaba ya ce haka ne, kwarai na yi mamakin canzawar yaron lokaci guda, tsohon yace babu wanda zai gagara daga shaidan, don shi ba rago ba ne, yanzu kaje gida akwai istihara da zan yi game da al'amarin shi idan Ubangiji yaso sai musan ta in da za'a bullo, mai martaba ya shiga godiya tare da yin sallama da tsohon wanda ya yunkura ya tashi ya yo ma sirikin nashi rakiya zuwa gurin mota.
Yarima zaune kan wani dan dakali karkashin wata bishiya mai sanyi cikin makaranta, yana nazarin littafan biology, dago kan shin da zai ya sai ko ya sauke idanunshi kan wata yarinya 'yar mutanan China tana sanye da gajeran siket wanda iyakarshi tsakiyar cinyarta, rigar jikinta kuwa singileti ce mai dan siririn hannu,

Ta cikin gilashin idonshi yake kare mata kallo nan zuciyar shi ta kwadaitu da lafiyayyar fatar ta, da takusa in da yake sai ya yi tamkar bai ganta ba, a nata gefen yau ne gani na uku da ta mishi gayen ya tsaya mata a rai, tayi niyya yau zata kula shi ta tsaya gefenshi cikin harshen turanci take CE mishi sannu da hutawa kasaitar tashi ta motsa, yi yayi tamkar bai ji ta ba, sai da ta sake maimaitawa sannan ya amsa ba tare da ya dube ta ba, tace zata iya zama kusa dashi?

Yace in taso haka zata iya, ta zauna tana satar kallon shi, ta dan yi gyaran murya, sannan tace shin zata iya tambayarshi? Hannu ya daga mata kafin yace yanzu ba time din tambaya ba ne, shiru tayi na dan lokaci sannan ta ce to zai iya taimakon ta? Ko yanzun ba lokacin taimako ba ne? Ya bata amsa dace wa in taimakon ya shafi kar2 ne zai iya in ko wani Abu ne daban to ba a yin shi cikin makaranta ya tambaye ta shin ta fahimta? Tace eh ta gane, nan ta soma mishi tambayoyi akan abubuwan da suka yi mata duhu shi ko ya shiga bata amsa yanda zata fahimta har zuwa lokacin sallar la'asar ya mike ta ce ina zai je ne? Yace ya fita lokacin kar2 ya shiga na sallah don haka yanzu sallah zai je.
[8:46AM, 12/28/2016] %???+234 814 912 1821%???: ??}_MEKE FARUWA 20??}_
Mamanmu ta dubi Bilkisu ta ce maigado ki daure kiyi amfani da maganin nan ga na turaren nan wannan kuma wanka zaki yi da shi, Bilkisu ta dube ta Mamanmu kada ki shiga cikin mata masu shiga gurin malamai saboda gudun shirka, aure lokaci ne. Mama tace maigado ba zan kauce hanya ba, wannan da ki ka gani Ummana ta ai ko dashi wannan na iskokai ne, abin nan yana bani tsoro, na rasa gane me ke faruwa? Bilkisu cikin sanyin murya tace kada ki damu Mamanmu, In'sha Allah, Allah zai kawo min mafi alkairi, wata rana sai labari,

yanzun su Bilkisu sun shiga shekara ta uku a jami'a { A.B.U} mass comm. Take karanta wa, tana sha'awar zama yar jarida duk da kasancewarta ba mai yawan surutu ba amman tana so ta zama cikin yan media, karatunta ta saka a gaba in da Mamanmu ta hana kanta ci da sha ta dage dan ganin burin maigado ya cika, duk da Abban Mansura yana taimaka mata sosai to karatun jami'a ya wuce wasa wasa, dan gane da mahaifinta sai abin da ya karu na tsana, da kuma tsangwama.

***************************
Jumma'ar yau kam Modibbo tsohon nan daga masallacin jumma'a ya nufi fada dan ganawa da mai martaba, cikin wani daki na musamman suka kebe duk suna zaune ne kan dar duma bayan gaisawa da suka yi Dattijon ya soma magana. Abu na farko da na fara gani cikin al'amarin Yarima na ganshi mai yawan fitsari ne in na ce mai yawan fitsari ina nufin yana da matsananciyar sha'awa, game da batun aure kuma ba da gaggawa kamar yadda ka ke nufi ba, amma zai yi aure ba da jimawa sosai ba, saboda matar tashi ba yar yankin nan jihar ba ce, sannan tana da matsala, haduwarsu da Yarima zai kawo abubuwa da dama, a cikin binciken nawa na ga al'amura da yawa, amma Allah shi ne mafi sani haka nan yafi mu sanin komai game da abin da zai faru, anan gaba. Sai dai za a iya nema mishi Auren daga wasu jihohi yazo yaga wadda zasu sasanta ko Allah zai sa tana ciki, haka ne in ji mai martaba, za a nemo mishi hotuna nan su sai in sa a kai mishi ya zaba in yaso sai ayi bikin a tura mishi can, dattijon yace to madalla haka din ma ya yi zamu bisu da addu'a, bayan tattaunawa suka yi sallama.

Yarima yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login