Showing 396001 words to 399000 words out of 413917 words

Chapter 133 - KURKUKUN KADDARA BOOK 3 4 HAUSA NOVELS BY BOSS BATURE.doc

27 Feb 2026

2646

duk yadda taso ta hana zuciyarta bijirema mahaifinta saida takasa saboda tana son zuwa itama.

Wuraren ?arfe biyar na marece dai dai, suka shigo gidan Alhaji Ubaid, Aunty Laura ta dauki wankan shadda, Ta coge daurin dan kwalin ture kaga tsira, Ita dai Aisha Abayane a jikin ta doguwa har kasa, sai nikab din da ta sanya.

Anan suka iske manyan bakin su Hajiya layla, babu masaka tsinke, Yan uwa da abokan arziki duk sun hallara a katafaren garden din gidan da aka kawata shi da kayan ado da kujerun da baki zasu zauna an tanadi duk wani abu da baki zasu bukata don jin dadin su, Ga mawaka da Maroka sun Cika gidan sai kaWe kaWe sukeyi da yan raye raye.

Tunda suka shigo gidan gaban Aisha keta faduwa rass rass, kwata kwata hankalinta ba akwance yake ba, duk sai taji ba dadi saboda ta sabawa mahaifinta.

Lokacin da ta lula duniyar tunani Yayin da Aunty laura ta shige Cikin mutane tabarta.

Sam bata ji takun mutun ba, sai dai taji an rungumeta, har firgita saida tayi amma da taga Benazir ce sai ta sauke ajiyar zuciya, cike da farin Ciki suke kallon juna, Banezir ta Wauki wankan tsadadden leshi ko arzikin dan kwali babu akanta..


"Amma wallahi naji dadin zuwanki Aminiyar, har na fara fidda rai, ashe zakizo, ya ki ke ya baba imam? Cikin sanyin murya tace"baba bayanan ya tafi sudan, atare da aunty laura mukazo" ruko hannun ta Benazir tayi "mu shiga ciki, ki gaishe da Uncle Musa, tun Shekaran Jiya ya dawo Nigeria, tare da matar daya aura baturiya, amma baizo da ita nan ba, acan gidansa na Abuja yabarta, bai sanar da kowa game da auransa ba sai dai muka ji abakinsa jiya daya zo"

tun da Benazir ta fara surutu Hankalinta ba akwance yake ba, wani irin faduwar gaba taji jin ta ambaci sunan Uncle musa fuskarta babu walwala tace"kina nufin Uncle musa yana acikin gidan nan"?

Jinjina mata kai tay"eh," tace toh tabari da anjima in an gama partyn sai suje su gaida shi, Benazir ta amsa da toh, damuwace karara Akan fuskarta, Benazir bata lura da halin da take a ciki ba.


bayan sun shiga falo ta iska kawayen Benazir Hada Anila kowaccen su ta dauki wanka na mutunci Aneelerh na ganinta cikin sauri taje ta rungumota, Sauran kawayan Benazir sai murna suke yi Aisha bintu imam tazo, har rige rigen daukar hotuna sukeyi da ita, baiwar Allah tadinga kakkauce masu saboda gudun kada baba Imam yaga hotanta agurin partyn daya hana ta zuwa, Aneelerh ce ta lura da yanayinta hakan yasa taja ta gefe daya ta tambayeta meke damunta? Bata boye mata komai ba ta sanar da ita, ta kara da cewa ita kawai hankalinta bai kwanta ba, tana ji aranta kamar wani abu zai faru, cikin sigar lallashi Aneelerh ta soma kwantar mata da hankalinta har saida taga ta saki jiki...

tun da aka fara gabatar da shagalin hankalin Aisha ba kwance Yake ba, ga kawayen Benazir sai cashewa suke yi suna tikar rawa ga abinci kala kala ko kadan batay sha'awar ci ba.

Tana zaune kan kujera Wayarta ta fara ringing, tayi picking tare da karawa kan kunnanta
Muryar shureim Taji yana fadin ta same shi a upstairs yana son yin magana da ita"

Bata kawo komai aranta ba, ta yi azan zai bayyana mata soyayyar shi ne Hakan yasa ta mike batare da sanin kowaba Ta nufi upstairs, abakin kofar dakin dataga takalmansa tayi knocking ana bude kofar dakin aka janyota ta fado ciki, a firgice ta dago don taga wanene rass taji gabanta Ya fadi ganin Alhaji musa atsaye fuskarsa babu annuri daga shi sai short a jikin shi, wani irin faduwar gaba taji, da tsantsar mamaki ta furta"uncle kaine"? Daga mata gira yayi"nine Aisha.."arude tace"amma yaya shureim ne Ya kira ni, yana ina"

"Ni ne nayi muryarsa, saboda nasan idan kikaji ni ke kiranki ba zuwa zaki yi ba" matsawa yayi dab da ita tayi saurin ja da baya cikin sanyin murya yace"aisha, inaso ki dubeni daga kasa har sama ki fadamin me Allah ya rageni da shi"? Kawar da kanta gefe tayi muryarta na rawa tace"bakomai"

"In har hakane meyasa baki sona?..

"Saboda bakai nake so ba,"runtse idanun shi yayi saboda jin zafin maganar shi

"Aisha idan kikai min hakan baki min adalci ba, kin hana zuciyata sukuni saboda ke na kashe makudan kudi donki samu rayuwa mai kyau, Harta karatun da kukayi a germany nine na dauki nauyin shi ba Alhaji Ubaid ba, kawai nayi amfani da shi ne saboda nasan Halin mahaifinki da tsautsauran ra'ayi ba lallai in yaji nine nayi hakan Ya amince kije ba, kuma nayi hakanne saboda in dinga samun ganinki akai akai, saboda Imam bazai bari ina zuwa zance gurin ki ba, amma da kuna karatu a germany ba karamin morewa nayi ba saboda ina ganinki a duk lokacin dana so"


Hankali atashe tace"Dama duk dawainiyar da kayi mana a germany ba dan Allah kayi ba? saboda son da kake min ne" jinjina mata kai yayi...

"Wallahi da ace nasan kaine ka dauki nauyin karatunmu a kasar germany, da ba abunda zaisa inje"

tana fada ta juya zata fuce yayi saurin ru?o qugunta da tafin hannun shi ya janyota da karfi ta faWo kan kirjin shi, ya soma matsa mazaunanta yana sakin nishi, For the first da ta fara hada jikinta da namijin daba muharramin ta ba, rai a6ace ta banbare jikinta daga nashi ta daddage ta wanka mashi zazzafan mari ji kake fasss!.

dafe kuncinsa yayi da tafinsa, idanunsa suka kada jawur cike da bacin rai yace"ni kika mara"? Tana haki tace kadan ka gani, Nan gaba idan ka kara gigin ta6a jikina wallahi saina yi maka abunda har abada ba zaka manta ba, dama ba don Allah kakeso na ba, sai don wata mummunar manufa taka" tana fada ta buWe kofa ta fuce...

Tun da yake wani dan adam bai ta6a daga hannu ya maresa ba sai akan Aisha, yaji zafin marin nan adaddafe Ya fada kan gadon shi yana juyi, ransa ya baci matu?a jikin shi har gumi yake zubdawa.

abangaren malama Aisha bayan fitarta daga dakin a jikin bango ta Jingina bayanta, fuskarta sharkaf da hawaye taji takaicin rungumar da Uncle musa yayi mata, kamar ta hadiyi zuciya ta mutu ta ke ji, Ya dasa mata kiyayyarsa a cikin zuciyarta.

Tana cikin tafiya wani irin ciwon mara Ya turnuke ta, da sauri ta dafe cikinta da tafin hannunta, sam takasa cigaba da tafiya a nan ta durkushe tana faman fitar da huci...

Adai dai lokacin dr shureim Ya hauro Upstairs din domin amsa kiran da Uncle Musa yayi ma shi, Yana ganinta Jikinshi na rawa ya karaso gurinta Yana tambayarta meke damunta? muryarta na rawa ta furta"cikina yaya shureim ciwo yake min, ka taimaka ka maida ni gida" ganin halin da take a ciki yasa shi ruko hannunta, ya taimaka mata ta mi?e suka sauko down, A lokacin babu kowa a falon gaba daya sun Koma garden can inda akeyin shagalin.
Har suka fito harabar gidan basu ci karo da kowa ba.

Sai nishi takeyi tana jan numfashi, dr shureim sai sannu yakeyi mata har suka karaso Cikin Gidan Imam, Ya tambayeta tana da maganin ciwon cikinne ko yaje ya siyo mata ne? Dakyar ta bude baki tace mashi bata da shi ya kare" Cikin sauri Dr shureim Ya fita Ya nufi chemist din dake a kusa da su don ya siyo mata maganin, tausayinta duk ya kama shi..

Lokacin daya dawo gidan hannun shi ruke da leda ta maganin daya siyo mata, a bakin kofar falo yai ta ?wala sallama shiru bata amsa mashi ba, Kuma Yan aikin gidan duk basa a kusa, wayar sa ya zaro ya danna mata call tana fara ringing, tayi picking yanayin yadda yaji Muryarta ba karamin Waga masa hankali tayi ba.

Cikin shesshekar kuka take fadin"ya shureim mutuwa zanyi, ka taimaka min, " adabarbarce ya furta"Aisha kina ina ne? Ga maganin na kawo maki" shiru yaji bata amsa mashi ba, a rude Ya mike Ya soma neman bedroom dinta saboda bai taba shiga dakinta ba, duk zuwan da zaiyi gidan A falo ya ke tsayawa.

Dakyar ya gano bedroom dinta, saboda tsabar rudu ya afka Ciki, a kwance ya taras da ita tsakiyar gadonta, sai juyi takeyi tana murkususu, tafukan hannayenta adaddafe da mararta, sam babu abaya ajikinta zafin daya taso matane yasa ta cireta cikin fitar hayyaci batare da saninta ba, sai Camisole data rage a jikinta shara shara gaba daya surar jikinta ta bayyana muraran.

Bai kula ba saboda hankalinsa ba akwance yake ba burinsa kawai ya taimake ta, Aje maganin yai akan bedside drawer Ya fito da sauri jim kadan ya dawo hannun shi ruke da bottle water Ya zauna daga gefen gadon..

Sai da Ya ballo kwayar maganin Ya juyo don ya taimaka mata tasha, kwatsam Idanun shi suka sauka akan Santala santalan Cinyoyinta lokaci Waya tunanin shi ya gushe, ya fara jin wata irin matsananciyar sha'awa na taso mashi kamar ransa zai fita, Zuciyarshi ta dinga azalzalarshi kanshi ya fara juya mashi kamar hankalinshi na barin jikinshi, Bawan Allah a lokacin yaita kokari kaucewa sharrin shaidan amma abun Yaci tura saboda yadda surar ummi ke fusgarsa har baisan sa'adda Ya afka mata ba, ga zafin ciwo tana fama da shi a haka dr shureim ya keta mata haddi, taji radadin da bazai misaltu ba, cikin fitar hayyaci ta dinga Sakin kukan azaba, tana yi masa magiya akan ya kyale ta, kada ya kashe ta, kada ya rabata da mutuncinta, amma duk abanza saboda a lokacin shureim yayi nisan da baya jin kira. Ya Ilahi!




*Daga Al?alamin Boss Bature=?%?
'?*





*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
[10/1, 18:58] +234 903 893 6460: =?%?=???=??? &?=???=???>???

~<><><><><><><><><><><><><><>
'?~

~___________________________________~


Bata tashi farkawa ba, sai Bayan sallar Magrib, bakinta dauke da sunan Allah, tana kokarin motsawa don ta mi?e taji wani azababben zafi agabanta, ga wata kasala data baibaye sassan jikinta, tunani to soma yi meya faru da ita? A ina take"? jin iska na ratsa jikinta yasa tay saurin shafa jikin nata, lokaci daya gabanta Ya soma faduwa jin babu sutura a jikinta cikin sauri ta yunkura ta mi?e zaune, tana kallon kanta kafin ta yi saurin kallon gefenta, shureim ta gani a kwance kan gadon batare da sutura a jikin shi ba, sai dan bargon daya lullu6e ass dinsa, sam ta kasa tuna komai amma tabbas taji a jikinta raping Winta yayi Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un fashewa tayi da matsanancin kuka tamkar ana zare ranta, Koken da ta ke yi ne ya farkar da shi, a firgice ya bude idanun shi da suka kada jawur ya dube ta da su, baiyi aune ba yaji saukar zazzafan mari kan kuncinsa ta sha?e wuyanshi tana kuka ta furta"nashiga uku! yaya shureim ka kashe min rayuwata, ka gama dani! Ka wulakanta martabar jikina ka goga min ?azantar Zina, Allah Ya isa tsakanina da kai, bazan ta6a yafe maka ba..."


zafafan hawayene suka wanke fuskarshi kwata kwata baiji zafin marin da tayi mashi ba saboda ruWun da kwakwalwarsa ta shiga gaba daya yabi ya rikice yana kokarin tariyo abunda ya aikata mata, saboda baya a cikin hayyacinsa komai ya faru, wlh ko a mafarki bai ta6a sha'awar ya kusanci macen da ba muharramarsa ta aure ba, balle Aisha da yake yi mata kallon kanwarsa, tana kuka Yana kuka Yace"Aisha bayin kaina bane, ba halina bane aisha, ke shaidace akaina, wlh ni ba mazinaci bane..."

bai ?are maganarba ta Fasa tsawa tana huci tace "babu abunda zaka fada min ya shureim, wlh sai Allah yayi min sakayya, da kasan irin burin da nake dashi akanka da ba kai yi min haka ba, da tunfarko ka fadamin kana son Jikina, Ni mai iya aurenka ce don in dinga biya maka bukatarka saboda son da nake maka, amma ka rasa ta hanyar da zaka neme ni sai ta hanyar Zina"?

Tana magana Jikinta na kerma, Idanunta sun kada jawur kamar an watsa mata barkono.

Cikin disasshiyar murya tace "ka karyamin zuciyata yaya shureim, ka cuceni, ka zalunce ni, Inayi maka kallon mutun mai tsoron Allah, ashe kaima fasiki ne, kana daya daga cikin mazan da basa son mace don Allah sai don surar jikin ta, kaja mun aikata zunubi, Yanzu da wani ido kakeso In kalli Babana, da mutanan da sukeyi min kallon mutuniyar kirki! Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un..." duk yadda yaso ya shawo kanta ya kasa, taki ta saurareshi balle ta fahimce shi, saukowa tayi daga kan gadon jikinta duk ba kwari dakyar ta mayar da rigarta da gudu ta shuge toilet tana kuka ta kulle kofar, tabar shureim a zaune kan gadonta yana ta kuka kamar karamin yaro, sau uku yana marin kanshi saboda bakin ciki da takaicin abunda ya aikata ma Aisha, Matar da yayi burin ya aura.

"Ya Allah ba halina bane, Kafi kowa sanin bawan nan naka, Ni maijin tsoronka ne mai gudun saba maka ne, kullum ina rokonka akan ka kareni daga sharrin zuciya da sharrin shedan amma meyasa Hakan ta faru dani? Meyasa na aikata ma Aisha haka"?...

Cikin shesshekar kuka yajiyo muryarta daga cikin toilet tana fadin"Yaya shureim ka tashi ka tafi tunkafin Aunty laura ta dawo"..

Jiki asanyaye Ya sauko daga kan gadon Cike da danasani Ya mayar da suturarsa, Wlh Yaji kunya mara misaltuwa, Yaji radadin da har yau In ya tuna sai yaji Waci aran shi.

______________________________________
'?

Lokacin da su Benazir suka lura babu malama Aysha a gurin partyn nanfa hankalinsu ya tashi suka dinga nemanta sako da lungu na gidan, har layin wayarta suka kira akashe.

Hankalin su atashe suka tuntu6i Aunty Laura da maganar, tace kada su damu, ta koma gida dama bada son ranta tazo ba, bayan Kammala partyn suka biyo Aunty Laura gidan don suga idan ta dawo, bayan sun shigo gidan suka Nufi dakinta, adatse suka iske kofar, Knocking su ka yi tare da ambaton sunanta, Tana jinsu tayi shiru bata amsa masu ba, har saida suka fara gajiya da bubbuga kofar su ka fara tunanin ko bata nan ne.

A lokacin da basuyi tsammani ba, sai ga kiran ta ya shigo layin Benazir, cikin sauri Benazir tayi picking up tana tambayar ina ta shiga ne? Suna ta neman ta.

Cikin raunanniyar murya Aysha tace kada su damu, tana acikin dakin, ta kwanta ne saboda bata jin dadin jikinta amma da sauki.

Cike da tausayinta Benazir tayi mata sannu da jiki kafin ta mika ma Anila itama tayi mata sannu.

Daga bisani su ka yi wa Aunty Laura sallama suka tafi, zuciyoyinsu cike fal da tunanin yanayin da sukaji Muryar Aisha.

Tun daga Ranar Aisha ta Wauke Kafa da zuwa gidan aminnanta, Babu wanda yasan abunda ya faru tsakaninta da dr shureim, ita kadai tayi ta nukunuku ta ki yarda Aunty laura ta gane halin da take a ciki, saboda bata son kowa ya sani ta fiso ta rufawa kanta asiri.


Tsawon kwana uku bata bude wayarta ba, baci ba sha, ba bacci, ta killace kanta adaki, wani irin depression ne Ya kamata ga ciwon rabin kai da take fama da shi, In ta fara kuka har sai hawayenta sun kafe tukunna take dakatawa, kusan kwana ta ke yi tana yin istigfari tare da kai kukanta gurin Allah.

Saboda tayi imanin shi kadai ne zai kawo mata mafita, Hankalin Aunty laura ba karamin tashi yayi ba, ganin Aisha na neman ta halaka kanta, Ta rasa gane meke damunta gaba daya ta hana kanta sukuni, ta rame tayi duhu, idanunta kullum a kumbure suke saboda kukan da take sha, ba irin magiyar da batayi mata ba akan ta faWa mata meke damunta amma taki sanar da ita, sai dai tace ta tayata da addu'a Allah ya yaye mata abunda ke damunta, tace toh In sha Allah zatayi mata addu'a.

Idan muka koma bangaren Dr shureim tun washe garin ranar da abun Ya faru, Yabar Kasar, Ya tafi Egypt saboda bazai Iya cigaba da jurar zama yana ganin Aisha da abun kunyar daya aikata mata ba.

Bayan makonni da afkuwar Lamarin, Sheikh Imam Ya dawo Nigeria, Bayan ya huce Gajiya a dakinsa, Aunty laura ta jera mashi abincin shi akan rug din dakinsa, Kasa cin abincin yayi saboda faduwar da gaban shi keyi, kuma yaji shiru Aisha bata leko ta yi mashi sannu da zuwa ba, kamar yadda ta saba yi mashi.

"Ina mamana? Ko taje islamiya ne, Aunty laura tace aa tana adaki Yace ta kira ma shi ita.

Fitowa tayi daga dakin ta shiga dakin Aisha, tayi mamakin ganinta a kudundune cikin bargo jikinta sai kerma yakeyi kamar wadda sanyi ya kama.

Hankali atashe Aunty Laura ta haye kan gadon tare da yaye bargon, gabanta ne ya fadi rass, ganin yadda idanun Aisha suka juye, tsabar zafin da jikinta ya dauka tamkar naman da aka gasa da wuta, arude Aunty laura ta zabga salati Ta watso aguje ta nufi dakin sheikh Imam Ta sanar da shi halin da Aisha take aciki, abincin da bai ci ba kenan, jikinshi na 6ari yabiyo bayan Aunty laura suka nufi dakin Aisha, Suna shiga suka taras da Amai na fita daga bakinta.

"Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un" arude Sheikh Imam Ya furta, baiyi wata wata ba, Ya sungumi Aisha Ya fuce da ita da gudu Laura tabi bayanshi, Suka shiga mota.

Kaitsaye Suka Nufi Asibiti da ita, aranar saida aka kwantar da ita saboda jikinta yayi tsauri.

A asibitin suka kwana, Sheikh Imam bai runtsa ba, Yadda Ya ga rana haka yaga dare, har fada saida yayi ma Aunty Laura akan sakacinta na rashin kula da Aisha, gaya nan har ciwo yakamata batare da ita ta sani ba, Aunty laura dai sai hakuri take bashi tace ba laifin ta bane, nan ta fayyace masa halin da Aisha ta shiga bayan tafiyarsa, ta kara da cewa ba irin magiyar da banyi mata ba akan ta fadamin meke damunta amma takiya sai dai tace Intaya da addu'a, Sheikh Imam ya damu sosai, Babban abunda ya kara daga masa hankali ramewar da tayi, kamar ba Aisharsa ba.


Basu sanar da kowa game da ciwonta ba, a duk lokacin da su Benazir suka kira Aunty Laura su kai mata korafin sun kira layin Aisha basa samu sai tace masu su yi hakuri ayyuka ne su ka yi mata yawa, kwanansu Waya a

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login