Showing 144001 words to 147000 words out of 413917 words

Chapter 49 - KURKUKUN KADDARA BOOK 3 4 HAUSA NOVELS BY BOSS BATURE.doc

27 Feb 2026

2660

Ya nufi dressing mirror, zuciyarshi cike fal da tunanin Angel dinsa, yayi maraicin ganin ta idanunsa sun kwaWaita da son ganin ta, tun safe baici komai ba, abincin da haris ya kawo mashi yana nan ajiye kan table ko buWesa baiyi ba.

Har ya yunkura zai zauna kan mirror chair, sautin knocking din kofar Ya dakatar da shi . ....

Cike da zumudi Ya nufi kofar, fatan shi Allah Yasa Angel dinsa ce,
BuWe ?ofar yayi a hankali, tun daga kasa Ya fara kallon ta, ko takalma babu a kafarta kamar an korota,
Gown din jikinta tayi mashi kyau sauke idanunsa yayi akan fuskarta har saida gaban shi Ya faWi, ganin yadda ta kumbura gashi babu fara'a ko kaWan ta haWe rai, ido cikin ido suke kallon juna har na tsawon mintuna biyar kafin sanyayyar muryarshi ta katse mata shirun ta

"Mu shiga ciki" yayi mamakin ganin batayi mashi musu ba, ta nufi ciki da sauri yabi bayanta, a tsakiyar dakin suka dakata


"Meke damunki? Idanunki sun kumbura kamar kinyi kuka, faWamin waya ta6a min ke"

Lumshe idanunta tayi kafin ta buWe su a hankali.

Takawa tayi har zuwa gabanshi ta tsaya suka fuskanci juna

"My man, Ina zoben da prime minister Ya baka"? Cike da fargaba Ta furta maganar ita kanta tsoron amsar da zai bata take ji saboda bata son zargin da take yi ya tabbata.

da sauri Danish Ya Wago da yatsun hannun shi Ya kallesu kwata kwata babu zobe

aruWe ya furta"ban gan shi ba, bansan a ina ya faWi ba, bari na duba toilet watakil na manta shi a ciki"

Juyawa yayi da sauri ya nufi toilet ya shige ciki.

tana atsaye cikin jin kunar rai, take kallon shi har ya 6ace ma ganinta, wani irin kululun bakin ciki ne Ya tokare makoshinta, hankalin ta yayi mugun tashi, zuciyarta ta karaya jikinta yayi sanyi, ta gaza yarda da abunda take zargi!!

dagaske danish ne ya aikata mata rashin imanin nan? babu tausayi babu imani Yana ganin tana fama da azabar radadin ciwo ahaka Yayi abun da yakeso yayi? Tunawa tayi da lokacin daya wurgar da ita kan gado, Ya sa hannu Ya hambareta har kanta Ya daki pillow, abun ya tsaya mata aranta.


Fitowa yayi daga toilet din, ya Wago suka hada ido, wani irin faduwa gaban shi yayi ganin kallon tuhuman da take jefa mashi, tuni yasha jinin jikin shi

"My man, kaga zoben"? La66anta na kerma ta furta maganar
Girgiza mata kai yayi"ban gan shi ba, bansan a ina Ya faWi ba..."

Murmushin takaici ta sakar mashi, kafin tace"Ni na ganshi"! da mamaki Ya kalle ta, hannu ta zura cikin aljihun gown din, ta zaro zoben ta mi?a mashi

"A ina kika gan shi"? ya faWa tare da matsowa kusa da ita, ya mi?a hannu zai karba, daddagewa tayi da iya karfinta na karshe ta ware yatsu biyar ta wanka mashi zazzafan mari kan kun cin shi, tashin hankalin da ba asaka mashi rana! lamarin ya gigita shi da sauri ya dafe kun shi, jikinsa na 6ari ya Wago amatu?ar ruWe ya kalli fuskarta...la66ansa na kerma ya furta"my.. Angel? Kina cikin hayyacin ki kuwa? Ni kika mara"?

Harara ta watsa mashi da kakkausar murya ta furta"idan akwai abun da yafi mari zanyi maka shi! Mugu Azzalumi, fasiki Wan iska... " waro idanunshi waje yayi tamkar kwayar zata fado ?asa He was completely confused

"Danish me nayi maka dana cancanci haka daga gareka? Danish kaida kanka? Sai yanzu na gane dalilin dayasa ka tsareni jiya akan in faWa maka idan na fara period, dama abunda kake jira kenan, Ina fata yanzu hankalin ka Ya kwanta, tunda ka samu abunda kakeso ...." rushewa tayi da matsanancin kuka mai cin rai, bawan Allah Yama rasa bakin magana, har yanzu baisan kan me take magana ba, ko kaWan baiji zafin marin da tayi mashi na, babban tashin hankalin shi miya faru da ita a daren jiyaS'

"Kiyi min bayanin meya faru dake"? Tsawa ta daka mashi kamar zata rufe shi da bugu tace"kana nufin kamanta abunda kayi min? Saboda ba damuwarka bace in rayu ko in mutu ko"? Ta fada tana cije la66anta da hawaye suka ji?a su.

"Idan ka manta bari na tuna maka, jiya ka shiga dakinmu da daddare...." zayyana mashi komai tayi tunkafin ta karasa gabansa yayi wani irin mugun bugu na tashin hankali, mi?a mashi zoben tayi"a jikin zanin gadonmu na tsince shi, ina fata yanzu ka tuna komai....."

Runtse idanunshi yayi, wani irin ?unci yaji aran shi, jikin shi ya hau yin kakarwa kamar wanda Sanyi ya kama . shirun da yayi ne ya ?ara tabbatar mata da zarginta akanshi.....amsar shi kawai take jira.. Duk da bata bukatar wannan

"Bani bane! Bazan Iya cutar dake ba Angel! bansan ya akai zobe na Yaje dakin ku ba..."

wasu zafafan hawayene suka wanke fuskarshi, wlh yafi ta jin radadin abunda akai mata, yaji zafi kamar ya fasa ihu! Wai Angel dinsa ce wani yayi ma wannan aika aikar?

"Danish baka ta6a min karya ba sai yau, baka da wata hujja da zaka kare kanka awurina, zoben ka ba ?afa gare shi ba, balle kace shi yakai kan shi dakina...Danish meyasa kayi min haka? Ko amafarki ban ta6a tunanin zakai min haka ba? A zato na kai garkuwane agareni mai bani kariya a duk lokacin da wani yayi yunkurin cutar dani sai gashi kai da kanka ka cutar dani, saboda idonka Ya makance burinka kawai ka samu abunda kake so ko"?

Dafe kanshi yayi da hannu Waya saboda wani irin sara masa da yai, ?afafunsa sungaza daukarsa baisan sa'adda Ya zube kan gwiwowinsa ba.

Ya rurru?e ?afafunta da hannayen shi, hawaye na fita ya furta"Unaish ki yarda dani! Ban ta6a maki karya ba, bani bane! Bansan wanene yayi maki aika aikar nan ba! Garkuwarki bazai ta6a cutar dake ba, ni aikina shine baki kariya kamar yadda kika faWa" ya faWa yana fitar da huci mai zafin gaske

"ki tausayama rayuwata, kada ki yanke min hukunci akan laifin da bani na aikata ba! nayi maki alkawarin zan gano koma wanene yayi miki hakan ..." cikin rauni na murya ya ?are maganar, yana kallon cikin idanunta.

cike da jin tsanar shi ta sa kafa ta buge hannayenshi daya ruke kafarta da su, ta soma ja da baya tana fadin"wallahi bana son ganinka! Ka fita araina Danish! Na tsaneka! Ka 6ata komai, kullum burina in faranta maka rai ashe kai ba haka bane awurinka, abin da baka sani ba ni nema nake na nema mana hanyar da zamu mallaki juna na har iya tsawon rayuwarmu, sai dai kash gajen hakurin ka da son zuciyarka sun ja makaW'

wurga mashi zoben tayi kan kirjin shi, da gudu ta juya ta fuce daga dakin.

Jiki amace ya kwanta kan floor, hawaye suka cigaba da sintiri kan kuncinshi, ga wani azababben ciwon kai da yake ji, tuni zazza6i Ya lullu6e jikin shi, Waukar zoben yayi a hannunshi Ya kura mashi ido yana kallon shi, ya rasa ya akai zoben yaje dakin su?wa ya kai shi? Wanene Ya cutar mashi da Angel dinsa?

sambatu ya fara yi"bani bane! Bazan iya cutar dake ba! Ni garkuwa ne agareki mai baki kariya, kada ki juya min baya, bana jin zan iya rayuwa batare dake ba, Angel kada ki fushi dani bani baneW'W'W'


Gaba Waya kalamansa acikin kunnanta, tana a durkushe bakin kofar dakinsa tana kuka kamar ranta zai fita, ganin lamarin take kamar a mafarki! wai Danish dinta ne yayi mata haka? Wlh ya karya mata zuciya! Ya kunsa mata kiyayyarshi, duk irin burin da taci na son ganin sun rayu a karkashin inuwa Waya ya ruguza komai....

Jin motsin mutun yasa tayi saurin share hawayen ta, jiki ba kwari ta mi?e daddynta ta hango yana shigowa, da alama Ita Yake nema...
Sai da ta fara daidaita nutsuwarta kafin ta sauko down ta nufe shi, sam baiji takun tafiyarta ba, sai dai Yaji ta faWa kan bayan shi ta rungumeshi, bata san sa'adda ta sake fashewa da wani kukan ba, duk yadda taso ta shanye shi takasa har saida Taj yaji, gaba daya yabi ya rikice, kafin yayi yunkurin ruko ta da gudu tabar jikin shi, ta nufi dakinsu ta shiga, a lokacin Batool ta jima da fita, kan gado ta haye ta kifa kanta jikin pillow ta cigaba da kuka kamar ranta zai fita.

da gudu Taj Ya faWo dakin, Ya hau har saman gadon, jikin shi har kerma yakeyi tsabar rudu da tashin hankali, janyota yayi da karfi ya rungumeta sosai a kirjin shi, muryar shi na rawa ya furta

"Unaisah! my Angel! Meya faru? Waya ta6a mun ke? baki da lafiya ne?

fuskarta tayi sharkaf da hawaye, hatta temperature din jikinta ya dauki zafi rau.


"My Angel meke damunki? Dan Allah kiyi min bayani? Ko baki da lafiyane?" sai da tayi kukan mai isarta kafin ta raba jikinta daga nashi ta sauko daga kan gadon, ta nufi toilet ta shige, jim kaWan ta fito da alamun ruwa akan fuskarta...tsayawa tayi nesa da shi tana faman sauke ajiyar zuciya.


"Zonan Unaisah" Ya kirata fuskarshi babu walwala, kamar babu laka a jikin ta ta karasa tare da zukunnawa ta zauna kasan gadon, saukowa yayi ya zauna suka fuskanci juna
Ya ruko hannayenta a cikin nashi"fada min meke damunki? Meyasa kike kuka?

Shiru tayi jimm har cikin ranta bata jin zata iya tona mashi asiri, koda zuciyarta zata buga saboda bakin cikinsa, ta ?wammace tabar abun aranta.

"daddy dan Allah kada ka tambayeni meke damuna, ka tayani da addu'a, in sha Allah zanji sau?i.."

ta faWa tare kwantar da kanta saman kafadarshi, Waura hannun shi yayi akan bayanta yana dan shafa shi cikin sigar lallashi yace"kiyi hakuri duk da bansan meke damunki ba, tun da kin nuna bakison in tambayeki dole in hakura, amma dan Allah kada ki sanya damuwa aranki! Ki kai kukan ki wurin Allah, Nima zan tayaki da addu'a in sha Allah.." lumshe idanunta tayi har yanzu bata daina jin kukan ba...


"Daddy, Inaso nayi nesa da gidan nan, na wani lokaci..." tun da yaji wannan maganar Ya fahimci akwai wanda Ya 6ata mata rai, a sannu zai gano koma wanene.

dagowa tayi a hankali suka kalli juna, idanunta sun ?an?ance sun kaWa jawur saboda kukan da ta sha..
"Daddy, Ka kaini part dinka, in zauna gurin Aunty danejo, ko kuma ka kaini wurin aunty Aneelerh dan Allah" marairaice mashi fuska tayi kamar zata fashe da kuka, kallonta kawai yakeyi gwanin bantausayi, arayuwarshi yatsani duk wani abu da zai ta6a lafiyar yarsa, bai son damuwarta.

"Daddy kayi shiru bakace komai ba"?
Numfasawa yayi kafin Ya furta"magana nakeso nayi dake, shiyasa na shigo gidan nan, sai kuma na taras da abunda Ya 6ata min raina..."
"Ka yi hakuri daddy, na daina kukan ay, ba zan kara sanya damuwa araina ba..." ta faWa tare da ?a?aro murmushi akan fuskarta.

Kwantar da ita ya kuma yi????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
ajikin shi don ta samu relief din abunda ke damun ta..
Calmly ya fara zayyana mata maganar da suka tattauna da su chief
"Ita mara lafiyan yar uwarsa ce, kuma kawar auntynki Aneelerh, tana a kwance gadon asibiti kwata kwata bata acikin hayyacinta tun lokacin data rasa yarta da mijin ta, likita yace idan har ba asamo yarinyar da zata iya acting kamar yartaba, to zata rasa ranta ne..." Wagowa Unaisah tayi a hankali ta kalle shi da alama taji tausayin matar.

"Muna so kije a matsayinta Unaisah, nasan zaki Iya!"

"Daddy na amince muje asibitin, dama najima ina neman hanyar da zan kyautatama chief, na ji dadi data kasance yar uwar shi, Allah yasa in zama silar samun warakarta .." murmushi taj yayi

"Ameen, amma akwai abunda nakeso in ja maki kunne akai! Idan har muka kaiki asibitin kada ki kuskura ki faWa ma wani ina raye! Ko ki bayyana wacece ke! Saboda har yanzu rayuwarmu tana acikin hatsari akwai masu bibiyarmu unaisah! WaWanda suka kashe uzair zasu iya kashe ni idan sukaji ina raye!" cikin matsananciyar damuwa yayi mata maganar donta dauki abun serious...girgiza kai tayi"daddy bazan bari kowa ya sani ba, saboda bana so na rasa ka"
"Koda wani ya nuna ya sanki ki ce bake bace, kinji"? ?aga mashi kai tayi...
"Ko kinsan mutun kika ganshi kada ki tanka mashi ko ki nuna kin sanshi, tun da haryanzu bamu san wanene ya sadaukar dake ba!"

Gefen fuskarta yashafa da hannun shi, ki fara shiri zuwa anjima da daddare zamu tafi" ta amsa mashi da toh, jan ta da fira ya farayi duk don ya faranta mata rai ko ta manta damuwar da take a ciki.......

______________________________
'?

wuraren ?arfe biyar, A jere motocin su Alhaji musa suka kunno kai cikin asibitin, A parking space suka dakata, da sauri body guard din dake driving din sa ya fito ya bude mashi mota, gently ya fito, ya Wauki wankan shadda mai Waukar ido, fuskarsa na sanye da mask, Iya idanunsa ne kadai zaka Iya gani, fitowa Alhaji ubaid Yayi daga motar, a tare suka nufi ciki, wani irin farin jini ne da shi duk inda ya gifta satar kallon shi ake, daga nurses har drs din kai harma da visitors.

Duk da ya 6oye fuskarsa hakan bai hana wasu gane shi ba, cikin girmamawa likitoci ke gaishe da shi wasu kamar zasu durkusa ?asa, cikin isa Yake Waga masu hannu batare daya furta magana ba....

Kafin su karasa ga medical room din, suka hango dr shureim tare da Aneelerh da zahra atsaye suna tattaunawa....

"Shureim"! Alhaji ubaid ne Ya kira sunan shi, kusan atare zahra da Aneelerh suka dago tare da kallon su...Rass Aneeleeh taji gabanta ya faWi ba ita ba hatta zahra saida taji wannan yanayin datayi tozali da Alhaji musa, Yayi matukar jan hankulansu...

?ura mashi ido Anila tayi, a lokacin dr shureim Ya karasa wurin su, kamar taso ta gane wanene, sai ta ga kamar uncle din benazir, bazata ta6a mantawa da Wan tahalikin nan ba, saboda kyautatawar da yayi masu tun da kuruciyarsu, kafin daga baya lokacin daya taka matsayi mai girma gaba Waya suka daina jin duriyarshi.

"Aunty Aneelerh wanene wannan"?
"Kamar uncle din benazir, banga fuskar dakyau ba amma inaji araina shi ne. ." bata ?are maganar ba, su Alhaji ubaid suka karaso wurinsu, atare suka haWa baki wurin gaishe da su
Alhaji ubaid ne kadai Ya amsa masu, da fara'a Yace"Aneelerh sannunku da kokari, Ya mai jikin"? Ita yake yi ma magana amma hankalin ta na akan Alhaji musa ya wani kau da ido kamar bai gan su ba.

"Alhamdulillah daddy, Jikin nata da sauki ba kamar jiya ba"

"Aneelerh ga Uncle musa ku gaisa ko baki gane shi ba..." dr shureim ne ya faWa
Murmushin yake ta saki"ina wuni..." ?asa ?asa da murya ya furta"lafiya..." zahra na gaishe shi ko kallo bata ishe shi ba, Ya wuce Ya nufi dakin Alhaji ubaid yabi bayan shi.

jinjina kai zahra tayi aranta ta ayyana wannan wani irin mutunne? daga gani Yana da girman kai da izza.

"Shureim ko dai Ya manta dani ne? Naga kamar bai gane ni ba, duk sai naji ba dadi..."
Shiru shureim yayi har cikin ranshi baiji dadin halin ko'in kulan da alhaji musa Ya nuna ma Aneelerh ba bayan ya santa farin sani...

Murmushi ya Wanyi kafin Yace"bana tunanin ya ganeki"

Ajiyar zuciya taWan sauke kafin suka cigaba da magana game da yarinyar da suke jiran zuwanta anjima...

Lokacin da su Alhaji musa suka shiga dakin, Hajiya layla tana azaune kan prayer mat, hannunta ru?e da cazbaha, kamshin turaren Alhaji musa ne Ya fara dakar hancinta kafin sallamarsu ta ja hankalin ta ga duban su, kamar taga wani mugun abu haka ta zabura ta mike tana kallon shi cike da mamakin ganin shi, saboda bata tsammanci zaizo ba tun da bai damu da benazir ba....

Tunda ya shigo idonshi na akan Benazir wadda ke kwance ta lumshe idanunta sai sambatu takeyi ?asa ?asa, kai tsaye ya nufi gaban gadon Ya zauna kan chair din dake fuskantarta
"Sannu daughter, Ya jikin naki"? Ya faWa tare dakai hannu Ya shafa goshin ta, a firgice ta bude ido tana kallon shi, la66anta na kerma ta furta"Uncle! Daddy! ina babyna? Ina Angel dina, dan Allah ku nemo min taj ya kawo min babyna"

Lumshe ido Alhaji musa yai kafin a hankali Ya furta"calm down your mind, zansa a nemo maki ita, but ki fara kwantar da hankalin ki"

rurruke hannunshi tayi acikin nata"dan Allah ku kawo min ?ata da mijina, uncle ku taimaka min kada na mutu ban gansu ba...."

tun shigowar shi bai dago Ya kalli hajiya layla ba, kamar babu ita adakin, wato yafi karfin yayi mata magana.

Ita ko tayi tsaye tana kallon ikon Allah, sam batayi farin cikin zuwan shi ba, gani take kamar ba alkhairi ne Ya kawo shi ba...

Gyaran murya Alhaji ubaid yayi mata

"Layla ya jikin nata"?

"Da sauki, mun samu taci abinci har wanka na taimaka mata tayi"

"Ya ake ciki game da yarinyar da Aneelerh zata kawo"?

"Sai zuwa dare zata zo asibitin"

"Allah Ya kawota lafiya, amma iyayenta ba su nemi komai ba"?

"Sai dai sunzo zamuji"

ajiyar zuciya yadan sauke

"Ba kiga musa ba ne? Naga baku gaisa ba" ya fada tare da nuna shi da hannu...
Harara ta watsa mashi kafin tace"ay shi yakamata ya fara yi min magana bani ba, sai kace dai Nina tursasa mashi yazo asibitin"?

gaba daya maganganun da suke tattaunawa akan kunnansa ko ajikinsa.

Sun Wan jima kafin ya mi?e Alhaji ubaid Yabi bayansa suka fito daga dakin
Sai da suka fara zuwa office din likitan dake kula da ita don jin karin bayani dangane da lafiyarta, kafin suka fuce daga asibitin.

_________________________________
'?

Wunin ranar Danish bai le?o ko kofar dakin sa ba, babu wanda Yasan halin da yake a ciki, kamar yadda ita ma ta killace kanta adaki, wuni tayi kudundune cikin bargo lokacin sallah kaWai ke tada ta, tuni zazza6i ya lullu6eta jikin ta har kerma yakeyi kamar zatai hauka saboda azabar raWaWin da zuciyarta keyi mata, tayi kukan har ta gaji ta gode ma Allah, danish ya dasa mata tsanar shi a zuciyarta, ko sunan shi bata son ambato, hauka tadinga tana bubbuga mattress da hannayenta kamar yar dambe duk ta hargitse dakin a karshe ta fashe da kuka tana fadin"ka karya min zuciya my man, na tsane ka! Bana son ka! Bana son ganin ka! Ban ta6a tsammanin zaka iya cutar da rayuwata ba! Meyasa kayi min haka? ..." tajima tana haukanta ita kadai kamar zata zauce.

Wuraren ?arfe takwas na dare, taj ya kirata awaya yace ta shirya ta same su a parking spot,

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login